wani dariya kamar Boss yace sannu yar karya da ba a San Asalin balbela ba da sai ace daga masar take,ance me kudi ne ya akayi kike sana'a?kina ci da kanki,wa ya taba ganinsa yazo wajenki?makaryaciya rufa miki asiri zanyi kisa ya sakeki na lallaba Na aureki Ku ba gata ba,ba yayan uban kowa ba sai shegen iyayi wai ku kyan da kuke dashi ne yake rudarku ko?
Nima fa bani da hakuri watarana nace ina ganin mutuncinka Hammad karka bari na yaga ma mutunci a unguwar nan,ka gyara kalamanka,ni yanzu me daraja ce da tsada domin ina da aure kuma da ace kasan wa nake aure da sai ka raina kanka tare da yin nadamar kalamanka,ni nafi karfinka wlh ko ace bani da aure hankalinka da nutsuwarka sun min kadan a matsayin mijina,ina fadar haka na juya cike da Raunin zuciya ina son fara Kuka... dum gabana yayi mugun faduwa ganin motocin Aayan sun kai su Bakwai a jere kofar gidanmu,juyowa nayi na kalli Hammad kana nace ga dan Halak can, zo ga mijin nawa sai ka mutu na juya ina tafiya,na barshi nan tsaye,kusa da inda suka yi parking akwai me salat ba ruwana na tsaya na siya mana salat da tumatir sannan na rike ledar zan shiga gida,muryar su Meenat naji da fara'a suna sis mun dawo ina kika je?da sauri suka karaso tare da rungumeni ina musu Kiss a goshi domin mun saba da hakan ma,Ma'eesha ce ta karbi ledar salat dake hannuna ni kuma na karbi jakankunan makarantarsu muka nufi shiga gidanmu,ko kallon motocinsa banyi ba,yana ciki duk abinda mukeyi yana kallonmu,yasha mamakin ganin ko kallon motocin banyi ba kuma yasan na gane shine saima gida yaga mun shige,ni kuma cike da bakin ciki na banko kofarmu da karfi da niyyar na rufe dan Ubansa tunda baida mutunci nima zan nuna masa abin haushi da kunya kawai sai kofar ta balle baras ta fadi kasa rigijif ai ko har securities dinsa sai da suka barke da dariya yanda na shiga gidan cikin fushi da hasala tare da mako kofar kuma sai ta balle.
Aayan ma sai da ya dara duk kuwa da kuncinsa,muna shiga na taimaka musu suka cire kayansu,nace suje suyi wanka muyi sallah sai muci abinci, shi kuwa Aayan ganin masallaci za a fara sallar Juma'a sai yace suje suyi sallah sai su dawo,a nan masallacin unguwarmu sukayi Sallar, kafin su fito na gyara salat na yanka mana,Bayan munyi sallah na zuba mana a tire kato kun San dai akwai ci ni kam,a tsakar gida saman tabarma na wani baje cinyoyina,sanye nake da Vest red,sai skert din atamfata yayi mugun Dameni gani da hips tare da da tudun Mazaune kamar babbar mace,haka nayi wani cas dani ga skin dina jajir da ita fara,ko dankwali ban daura ba sabo da ni dama a gida bai Dameni ba,jelar gashina har yaso wuce tsakiyar baya na,sajena da gashin gaban goshina sun kwanta luf,ina ta bawa su Meenat abinci a baki kamar wasu yara nima ina ci suma suna bani muna hira.
Wani yaro ne ya shigo da Sallama wai Mufeeda tazo sauri yake zai tafi,nasan bazai wuce Aayan ba cike da masifa nace kace bata da lokacinsa,yaro ya je ya fada sai ga yaron ya dawo yace wai idan ya iskeki sai kin gwammace kida da karatu,Mufeeda tace kace nace yazo din koma mene yayi idan zai iya,yaro yace ni dai tsoro nake ji bazan iya fada masa ba,Mufeeda tace to dan uwarka nice sa'arka zaka zo ka fada min fice min a gida,yaro ya fice da sauri yana kuka Mufeeda ta zageshi,can sai ga Oga Aayan da kansa ya shigo gidan cike da bacin rai yana huci,kamar ance wani ya mutu yanda yake kunci,yanda ya hadu yau ba a cewa komai,yayi masifar kyan da ban taba gani ba,cikin kana nan kaya yake hadaddu duk gidanmu ya gauraye da kamshinsa.
Wani Kwarjini ya min tsoronsa ya kamani na fara da na Sanin maganar dana fada masa,Ma'eesha sarkin Surutu tace sis gashi nan ya shugo ko shine mijin naki? Meenat ta kalleshi ta kalleni haka take yi sannan sukace ina yini? Da kyar ya iya bude baki yace am fine tare da kare min kallo ta kasan ido,
ni dai naci gaba da basu abinci a baki ina cewa kuci abinci akwai Islamiyya kun sani, ganin su Meenat a ransa yace har kanne gareta Ashe,muryarsa naji yace ina Mum naki,cike da zafin rai nace taje inda ka aiketa, ba wannan ne ya kawo ni ba ina da aikin yi,kizo muyi magana dake,Meenat tace Sis kije mana,sai da na ebi abinci a hannuna sannan na Mike da abina ina ci kamar mayya,ya kalleni yana mamakin jarabar ci na ko micijin ciki ne da ita oho,hannuna da shinkafa a ciki na dunkuleshi nace shigo wannan dakin,ya wani yatsina fuska yana tabe baki haka dai ya shiga yana wani makale jikinsa irin zai kwashi dirty,
Ji nayi yace ba a gidanmu zaki zauna ba yanzu,wani gidan za a kaiki daban,kiyi fixing Date da kike so su Abbi sunce ba yanzu zaki shiga family house ba sai nan gaba,so gidan dana kaiki rannan kike gyarawa nan zaki shiga,ki sanarwa Mum naki,wani farin ciki ya kamani kamar na taka rawa wannan hadadden gida ga kayan dadi zanci na koshi, ban san sanda na fashe da murmushi ba tare da cewa wannan gidan me kayan dadi? sai kuma wani bakin ciki ya tsaya min wato bai ma San Ammah ta rasu ba,kuma ko irin yace min ya me jiki ko ta warke Sam,nace aiko ya me jiki kace min ko? Au bata warke ba?kamar na mareshi haka naji,nace ta rasu,Allah yaji kanta ya furta irin ko a jikinsa,nace daga ni sai kannena mu uku,yace then? kuma ni yanzu na fasa auren ka sakeni kawai yafi min bashi da amfani sam,murmushi yayi yana daga tsaye yace kin makaro kinci Sadaki,kuma na biya kudin Magani na cika alkawari dole ki cika min nawa,don haka sai ki biyani ko ki karbi aure zabi daya,Hawaye ya zubo min da muryar kuka nace mugu ka kashe mana Ammah zaka ce na biyaka kudi,ai kaine ya dace ka biyani kudin diyyar Ammah kai ka jawo ta rasu,da tuni muna nan da uwarmu,Kuma haka ake Business din idan banda sadaki me ka bani,bayan kai kace zamu ji dadin duniya da kudin,zaka yiwa kannena komai na rayuwa zanyi abinda nake so da kudi yanzu me kayi daga ciki,haka ake Deal din,ai sai na fara gani a kasa tukun,Oya na mika masa hannu nace miko kudin fara harkoki da jin dadi first mu fara murmurewa muma muji dadin duniya sai na yarda nima a kaini gidanka,kuma dole ka sai min injin Markade na dinga yiwa mutane ina samun kudi domin makociyar mu da kudin Markade taje Makkah, tare da keken saka kayan sanyi, bai sanda yayi dariya ba matar dake neman jin dadin duniya kuma wai itace da Markade a inji, ita nufinta duk cikin Jin dadi ne bata saba da dadin ba to,nace kuma sai ka sai min irin abin rannan me dadi,ka bani kudin kashewa,yace nawa zan baki?Na gama tunanina na shirya masa mugunta zanci kudinsa da yawa nan take na sosa kaina nace Dubu bakwai duk wata daya,kacal?yace, Na hangame baki nufinsa basu da yawa nace Dubu goma Sha daya to,ya juya tare da cewa get ready Next wk Driver zaizo ya daukeku.
nace to haka za a kai maka Amaryar taka kai ba dangi?ba kwalliya?ba gyaran jiki?ko haka kaga anayi ko kuma son kudi da tsumulmula ce tayi ma yawa,mene Tsumulmula? Nace gashi nan haka wai ake kasuwancin zaka tafi ko sisi baza ka bani ba cikin kudina na business,abinci ya kare hakkinka ne,bani da Vaseline,ina so zan yi kitso ai sai ka kawo kudin ko? Ni tunanina ai nayi ne dan na tatseshi kudi na hada masa mugunta zan cinye masa kudi su kare,ya kalleni tare da daure fuska yana dariya a ransa yace nawa ne kudin?Na shirya karya na ninka kudin nace Dubu biyu,wata dariya ta kamashi amma ya maze ya zaro Dubu biyu sababbi kar yace gashi,na karba nace tsaya na irga domin kudi suna da doka tare da ka'ida,na dankwali yawu kamar me irga wasu milliyoyi na irga nace sun cika,yayi hanyar fita daga gidan, wai duk cikin Jin haushinsa dan na kona masa rai nace amma wlh girma ya fadi,an fadi kasa ba nauyi,ka bani kunya kuma ka bada guys ashe ma duk bogi ne da ake kurin ana da kudi sai dai a kwashi motoci ana yawo a gari,a tambayi Dubu biyu ba kari ba komai ina laifin ka bani Dubu uku ko ka kankaro girma da mutuncinka,amma yanda na fada haka ka bani a haka kamar gaske,ana tafiya kamar dan sarki aji tsoron Allah wlh azara'ilu ko yaushe zai iya zuwa, ficewa yayi da sauri sabo da dariya taci karfinsa bai so kuma taga hakorinsa yana dariya, haka ya shiga mota yana dariya,su Kansu escort din nasa mamaki sukeyi Aayan kamarsa duk jarabarsa wata na sashi dariya.
MAMAN MEENAT ina godiya da Sharhi,taku ta manya ce kunfi karfin kowa sai dai mu kwashi gaisuwa. page na yara neπHAFCYCY this page is for u Sweety.
QUEENMERMU tamu dubun gaisuwaπππβ€β€β€β€
MAMAN WALEEDA kin boye Allah yasa lfy.
Masu Sharhi yan albarka
ASMABAFFA FANS CLUB
TASKAR SURAYYARMS
TASKAR FIDDAUSI SODANGI
HAUSE OF HAUSA NOVEL tare da sauran Gps ina matukar jinjina muku da godewa.masu min magana ta Pc tare da masu kira ina rangado muku gaisuwa me yawa Allah ya kara kauna.
Koda ya fita basu zarce ko ina ba sai gidan Yarima Bobo abokinsa wanda suke shirya komai tare,ni kuwa mamaki nakeyi kamarsa duk kudinsa wai yanda na tambayi kudin ba kara ba komai iya 2k din ya bani,nan nace bari ya dawo sai na gwadashi nace ya bani Naira Dari kacal na gani iya 100 zai bani,Meenat ce tace Sis mijinki me kyau dan gayu wlh kinyi sa'a wannan irin kyau amma dai dan kasar waje ne ko? Kyan banza ne dashi Meenat sai fadan masifa,Hmm to Allah yasa ya canja ya koma Sonki Sis ai idan munje gidansa kwalliya zaki dinga yi ta jan hankali ki sace masa zuciya da wuri,idan mun ganshi a gidan ko?ai ba gida daya zamu zauna dashi ba main gidansu daban inda za a kaini daban kuma ni ai ba sonsa nake ba ina ruwana da har zanyi kwalliya sabo dashi,sis ke har yau da sauranki Allah ana gabas kina yamma irin wannan ai abin a so ne,baki na tabe tare da cewa ke karki Dameni me zanyi dashi auren Kasuwanci nayi ba abinda ya Dameni ya dauki nauyin mu komai da komai muji dadi shike nan buri na,kallo na Meenat tayi tare da cewa Sis ke bakya sha'awar maza ne kamar wacce wanzami ya cirewa Budurci?ko dai ba a sani ba Ammah tasa wanzami ya yanke miki Belin ki? Dariya nayi domin Mufeeda ta fini Sanin duniya tana zuwa schl,nace baki da kunya Meenat ai ni bana son wani Namiji me zanci dashi tir Allah kiyaye,Meenat ta dinga dariya tare da cewa Sis yanzu ko yar Runguma kuyi bacci ba kya so ga dan Kiss ma? Baki na rike ina kallonta nace ke wanne kiss wanda nake gani a film? Wlh bai isa ba idan yace ma zai min za a kwashi Bala'i da yan kallo ke nifa duk irin harkar nan bata damuna gwara kudi kawai,Meenat tace ni kuwa da nice na Samu me kyau haka ga kamshi,kudi komai ya hada ai da anga kwasar duniya,ke Meenat yarinya dake kike irin wannan zance,da nawa kika girmeni wai ma ki zauna kamar ba yar cikin birni ba gaki a cikin Birni amma kamar kina kauye, ae naji tunda Ku zaku Zama yan birnin ba komai zan muku ko mene abinda nake so kawai na koma makaranta idan ya Amince amma ni me ya Dameni da wani love.
Muna rayuwarmu bayan kwana uku su Meenat suna zaune suna ta faman game a wayata Nokia a tsakar gida,ni kuma sanye nake cikin wando tight 3qrt blue sai rigata iya rabin cinya me gajeren hannu pink kaina ba dankwali jelar na lilo ina kusa da Rijiya na ebo wanki ina ta wanke mana kayan sawa kusan ko yaushe sai nayi wanki haka nake bana son kazanta.
Sallamar mutum muka ji kawai a cikin gidanmu kamshinsa ya gauraye ko ina nan take muka gane Aayan ne yazo yaji lokacin da na Zaba a kaini gidansa matsayin matar Aure,mamakina shine rannan a waje ya ganni ina yawo amma Bai ko tambaya me yasa na fita bada saninsa ba,kaina na bawa amsa ai ba Sonki yake ba ina ruwansa ko ma ina zaki je.
Ganin su Meenat suna wajen yasa na amsa Sallamarsa tare da mikewa ina goge hannu na,gabansa na karasa tare da cewa sannu da zuwa wani Kwarjini da tsoronsa yasa na dan duka nace Ina yini,ko amsawa baiyi ba,na Mike na kawo masa wata kujerar roba fara tare da kara goge masa kujerar da wata duster,sai lokacin ya zauna kamar wani sarki yasha kana nan kaya yau ma wandon kansa abin a kalla ne ya hadu pencil dashi,Meenat ga Uncle yazo nace sabo da shishigina shi kanshi sai da ya tabe baki wai Uncle,da sauri suka zo suma tare da durkusawa a gabansa suna gaisheshi to su dai sun fini samun matsayi sabo da ya amsa musu sau daya da lfy bai kara ko ce musu komai ba suka koma inda suke suna ta game dinsu,Yau wacce rana ya ganni bana cin komai, bai gama tunaninsa ba yana zaune yaga na shige dan kitchen dinmu na fito da pure water a plate guda biyu na ajiye masa,ko kallon plate din baiyi ba sai faman chat yake a waya yana wani murmushi,kara komawa kitchen nayi na dauko Ayaba guda wajen biyar na mikawa Meenat da Ma'eesha guda biyu,tuna ninsa shi zan bawa ragowar sai yaga na koma inda nake wankina na bare guda daya gutsira biyu na cinye gudan Ayaba,na dan ci gaba da wankina na kara bare guda itama gutsira biyu na cinye duk yana kallona ba tare da na gane hakan ba,guda daya na rage na koma wajensa tare da dora masa saman ruwan dana kawo nace gashi nan Kaci sabo da Ido guba ne shi yasa,komawa kitchen nayi tare da zubowa su Meenat tuwon shinkafa miyar ganye tun daga Ido zaka San akwai dadi,Nace kuzo Ku kara abincin yamma kar yunwa ta kama min Ku,dama indai ba schl to dole muna kara cin abinci da yamma,ni kuwa a rana sau hudu sau biyar nake cin abinci,shi yasa kannena ma haka nake dura musu ko basa so sai nace sai sunci kadan.
Documents from AIHAUSANOVELS
Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels
Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels
Ma'eesha tace nidai sis na koshi har sau nawa za muci tuwon nan gashi da dare ma kice sai munci,Na bata rai tare da cewa kin san tunda na zuba sai an cinyeshi ko Amai zakuyi sai kunci,Meenat cike da shagwaba tace pls Sis mun koshi Allah,nace to Ku kuzo muci tare nima zanci na zauna wajensu na fara ci ina dura musu ta dole suna yatsina fuska sun koshi,sai da muka cinye dole sannan na wanke plate din na maida kitchen,nace Ku ajiye wayar nan kuzo Ku karasa wankin nan da sauri suka taho tare da karba sunayi,ni kuma na koma kusa da Angona Aayan na zauna saman tabarma na kalleshi tare da cewa Angon Business,ba tare da ya kalleni ba yace wacce rana kike so? Nace to wai dangina baza suzo a dauki Amarya ba? Ni bana son mutane a harkar nan Business ne mene amfanin sanin mutane,ba auren so ba mene sai an sani wani auren kirki ne wannan da har zan nemi mutane,Allah baka hakuri zabi date da kanka idan ma yau kake so muje,amma kuma da mun tafi tare da Uwaliya da take gidan nan ko? Wani kallo me cike da masifa ya wurgo min tare da cewa wannan gidanku ne ko na haya? Namu ne na kanmu cewa ta,yace to bana son kwashe kwashe ku din ma dole ce zata sa Ku shigar min gida bare wata Uwaliya ko me,ku Uku nan zan iya rikewa wannan gidan kusa yan haya ko Ku bar matar a ciki ko Ku siyar da gidan ni ba matsala ta bace.
Burina kawai muje hadadden gidan nan ace yau gamu a ciki zamu zauna wayyooo dadi gashi nasan ma zai dinga siyo mana kayan dadi ai nan take nace azo gobe a dauke mu,mikewa yayi zai fita,wata dabara ta fado min na Mike da sauri tare da dauko Hijab na saka nabi bayansa da sauri sabo da so nake wasu yan unguwa masu sa ido su ganni tare dashi su tabbatar da gaske ne aure na a daina zagina a gari,sai da nayi sauri na jera dashi har waje,ya kalleni tare da cewa ina zaki je,nace uhmmm makwafta zanje tunanina zaice kar naje ai ina da aure sai naga ko a jikinsa,muka fita har waje tare ina ta faman Mannewa kusa dashi sabo da yan unguwa suga fa ae ga zahiri ga sheda,na rasa me zance nace wai ka tsaya mana banfa gama magana ba,ina jinki ai,sabo da na jashi da zance har mutane su ganmu da yawa nace haka ake Business din kuma ni me zansa idan anzo daukan Amarya? Banza ya min,nace sannan ina son Naira Dari zan sa kati a wayata na kira Family,da mamakina sai naga ya tsaya a jikin motarsa ya zaro Dubu guda sabuwa ya kira Almajiri ya mika masa tare da cewa dan Allah samo min canji ka ce a hada ma da yan 100.