manya a waje na gaba,bakinsa yake dargajewa shi tunaninsa ai dole ma ya auri Meenat tunda yayyenta sunce sun bashi ita.
ta window din sama Na hangosu yana tsaida Meenat yana Meenatu Meenatu yan mata dan Allah ki tsaya,haba Meenatu so kike sonki ya kashe ni? Meenat ta ja tsaki tare da hararsa Malam Kaja mituncinka mun san darajar Dan Adam shi yasa nake daga ma kafa Amma tunda kaki ji zaka ga abinda zanma.
Kwaja yace ko me zaki min ni Bazan ji haushiba tunda ina sonki,da wlh ba da gaske nake ba Amma na yaba da hankalinki da nutsuwarki,gaki kyakyawa ni yanzu ba zancen yayyanki nake bi ba wannan da gaske ne daga makwallaton zuciyata a daina maganar wasa, to bana sonka kaja Life dinka ka kara gaba Malam cewar Meenat,Murmushi yayi yace yan mata bani da Lifan ni bana karya dan a soni,karki kiyi tunanin Ina da Lifan kice Naja Lifan dina na tafi wlh Allah ko Keke bani dashi idan zaki soni ki soni dan Allah nasan ku manya ne kun wuce ayi muku karya,Takaici ya kama Meenat tace ina ruwana da karyarka ka ja rayuwarka kayi Out a gidan nan,Haushi KWAJA yaji yace na fuskanci Ku kunfi son dan karya azo ana muku birga da mota kullum idan nazo zance na baki Dubu daya ko Dubu daya da Dari biyar koma fiye da haka,to ni ba haka nake ba gaskiya da gaskiya nakeyi wlh da zaki aureni kullum sai na dinga siyo miki kifin gona kina soya mana,watarana ma Miyar zabo zaki dinga yi mana,Taliyarmu guda da macaroni da wake gongoni guda ya ishemu na na kwana hudu zuwa biyar, tsaki Meenat taja tayi gaba ta barshi nan,ina jikin Window ta sama ina ta dariya gaskiya Su Haneefa yan Iska ne,Meenat ta shigo na dinga mata dariya,nace Allah sarki kanwata duk iya kwalliyar nan kuma taki sai ki kare a KWAJA tumburarre,Dariya tayi itama tare da cewa ai Allah ya tsinewa su Haneefa yanzu idan nayi wani Saurayin yazo ya ganni da wannan ai wlh rainani kawai zaiyi ya daina zuwa,ina ta dariya harda kwalla Meenat tace dan Allah ki daina,har dare muka kwanta ko farkawa nayi sai nace ta KWAJA tashi na baku lbr,banza tayi min tace wlh sai na fadawa mijinki idan ya dawo tunda haka kike min.
Yau nayi shiri tsab ba schl zanje wurin Daddyn Aayan ya bani labarin gidan nan da yace zai bani,koda naje Sallah ya idar daga kwancen,yana murmushi muka gaisa,nace Daddy yau na shirya a bani Tarihin naku. Yace to yata bude kunnuwanki kiji.
Next page is very Important readers ku tsaya ku karanta da kyau shine zamu san waye Aayan.
Raffa
Page naku ne MADINA ALEEYU
MAMAN SAMHA
NAJA'ATU ALIYU
Jinjina gareku na wajena
MOMMY ARFAT
AYFA
MARYERM MUHD
HAJARANCY
HAULATU KAMBA
QUEEN KK
Zaune nake na nutsu Daddy ya fara bani labari,
Mu yan Asalin Kasar Algeria ne sabo Dama kasar suna da yawan farare duk kusan larabawa jar fata,har yau muna da ragowar dangi acan kawai zumunci ne da yayi karanci yanzu bama yi dasu suma haka,Babana Mahaifi kakan Aayan shine Jabeer Muhd Jabeer tunda suke dama su masu kudi ne sun gaji dukiya me tarin yawa,a tarihinsa kaf ba aji talaka a jininsu ba tun zamani me tsawo,komai sun hada ilmin boko da kasuwanci,Jabeer Muhd Jabeer Allah ya Yoshi me son yawon zaga duniya har Allah ya kawoshi Nigeria can cikin wani dajin Fulani dake Taraba sunje yawon bude ido a rugar fulanin Allah ya hada shi da Mahaifiyarmu Hajja kenan wacce kike gani a gidan nan tana zuba mulki sunanta Karimatu,Karimatu Hajja basu gaji arziki ba don a rugar ma su talakawa na karshe,Allah yayo su da son kai tare da son abin duniya ga tsafi da bin Malamai,Sau daya suka hadu da Jabeer taga yana da dukiya dama bata da burin da ya wuce ta auri me kudi wanda zai kaita kasar waje su zauna,tun daga tambayarta ina ne gidan me gari shike nan ta koma gida ta sanarwa Babarta cewa taga wani tana so Bature ne,sunansa Jabeer,nan Babarta Larai ta shirya sai gidan bokanta,Lokacin Jabeer ya bar kasar nan ma Nigeria yana Ghana,yaji son Karimatu ya shigeshi babu bata lokaci ya dawo a gigice sabo da tsafin da suka masa,yana zuwa da maganar Aure Larai da mijinta Usmanu Baban Hajja suka amince sabo da son abin duniya.
Ko dangin Jabeer babu sai wakili aka yi masa a kauyen aka daura Auren Karimatu Hajja da Jabeer,sabo da aikin bokanci ya tafi da ita Algeria sunyi shekara daya ya dauketa suka koma London inda a nan aka samu Cikina ta Haifeni naci sunan kakana Muhd,ana kirana Muhd Jabeer Jabeer, a London na taso cikin Jin dadi gata tare da kwanciyar hankali,ga ilmi sosai na zamani dana Islama,sabo da Babana akwai son Musulunci,y anda ta mallake Babana yasa take masa abinda taga dama,wulakanci iri iri da cin mutunci,tana ta sace masa dukiya da kadarori amma duk da haka arzikinsa karuwa yake,ita kuma tana ta sace wasu tana adanawa.
Bayan na kwashe shekaru biyar a duniya asirin da Babata Karimatu Hajja tayiwa Jabeer Babana ya karye,nan fa Jabeer yace Bai San zance ba baya son Hajja,ya dinga wulakantata,gashi sabo da kudi bata so su rabu tana kasar waje tana cin daula,haka take jure wulakancinsa sabo da kudi har ya kara Aure ya auri Masoyiyarsa Hafsat Balarabiyar kasar Jordan,mata ta gari suna zamansu lfy tana sonsa tsakani da Allah ba irin mahaifiyata ba da son kudine kawai,a haka take zaune har ma abin yaci tura ya saketa saki har uku,sabo da ta Saci kudi da yawa yasa ta san yanda zata yi dan kar ma a gano ta sai tattara ta gudo Nigeria da dunbin dukiya a wancan zamanin.
Ni kuma ina wajen Babana hannun Hafsat Balarabiyar matarsa ta Jordan tana rikeni Amana da gaskiya,tun kuma daga kaina Babana bai sake haihuwa ba har aure ya kara amma Bai kuma haihuwa ba a duniya,bayan shekara Uku da sakin Karimatu ta samu wani mutum da take matukar Kauna da gaske amma bashi da ko sisi can cikin wani kauye yake shima a Taraba state Fulani ne sosai,sabo da tana sonsa ta gina katafaren gida na more rayuwa a cikin birnin Taraba,ta aure shi suke zaune tare da shi.
Dama ni bata son Babana sai don kudinsa,bare da asiri ya karye ya wulakantata sai ta kara tsanarsa bata da makiyi sama dashi sabo da kudin basu isheta ba tafi so ta yashe shi tas, sabo da wannan har ni da ta Haifa ta tsaneni kiyayyar Mahaifi ce ta shafeni nima bata kaunata da abinda ya shafeni, shekara biyu da auren Yusuf ta Haifi danta dashi Namiji Mustapha shine da kike ji ana ce Masa Abbi a gidan nan, bayan 2yrs ta kara Haifar kaninsa Sani shine zaki ji ana ce Masa Abbin Ameer, sai dan Autanta Awwal shine Abbin Khaleel tare da kannensu. tana ta juya dukiyarta amma basa wani karuwa sosai sai rufin asiri,Katsam Mijinta sai ya rasu Baban su Abbi kenan,ita ta Sha wahala dasu ta dauki nauyin karatunsu har iya Secondary da komai sabo da tana masifar sonsu kamar ranta sabo da yanda take kaunar Mahaifinsu,ni kuwa Abbin London kenan ko waiwayenmu bata kara yi ba,har dai iyayenta suka rasu sai dangi,haka Iyayen Babana ma sai dangi ana ta karewa.
Na gama Degree da Masters dina duk muna London,Babana yana ji dani sabo ni kadai gareshi,Har ya hadani Aure da wata budurwa Balarabiya yar Jordan cikin yan uwan matarsa Hafsat lokacin ya Damka min dukiyarsa baki daya da komai ga kuma aikina ina yi,na zama hamshakin me kudin da nayi suna a duniya kaf a wancan lokaci,Muna zaune lfy da Matata Asiya Wacce ta Haifar min Dan Albarka na Da daya tamkar da dubu Aayan kenan,dukkanmu a london muke rayuwa,har Aayan ya gama Primary lokacin kuma Su Abbi su Uku suma da matansu sun Haifi yaransu Maza,Abbi Mustapha mijin Hajiya Saratu Mami shine Baban Mujaheed,Haneefa,Sajeeda,da kuma Minal karamar yarinya,Awwal mijin Hajiya Zarah Ummi suna da Yara su kuma Biyar Khaleel,Farida mate din su Haneefa shegu Uku,Maryam,Nura sai dan Auta yaro mate din Minal wato Ahmad. Sani mijin Hajiya Haleema Anty yaransu uku Ameer fitinanne, Zahraddeen dan Wiwi,sai Yusrah.
Yanda iyayensu suke da hadin kai haka suma yaransu suke da hadin kai ba a jin kansu, Sabo da Hajja ko yaro taga yana bijire mata sai ta tafi gidan boka ta kai sunansa cewar Danta wane baya jin maganarta ayi masa magani ya koma sai yanda tayi dashi,haka Matan yayanta ta gama dasu sai abinda tace,jikokinta ma haka, ni ne kadai da Dana muka gagareta, kuma a halin yanzu hausawa haka suka koma,wai ko dane sai iyaye suyi masa asiri su mallake abinsu sai abinda suka ce,sai kaji ana in ka zauna yanzu zaki haifawa wata ta gaje miki da,ko shaye shaye,ko dai wani banza idan yana yi maimakon ayi masa addua wai sai a tafi gidan malam,dana wane ko Ya ta na rasa yanda zanyi tana Kaza a canja mata ra'ayi,ko miji ne bata son auren sai iyaye su kai sunanta kaga kawai ta koma sonsa,yana karyewa kuma shike nan Allah kyauta.
kin san yaro tarbiyyar daka dorashi da ita zai tashi,ni da Dana da basa sonmu har yayansu basa sonmu,shi yasa ko yaro yana ma kallon Banza maybe sunji iyayen su sunce wani abu a kanka,wasu ma in kaga suna daraja ka to iyayensu ke yabonka gabansu a kula iyaye,daga kun samu matsala da yan uwanki ki kwashe ki fadawa Yara wane dan uwana ko yar uwata tayi min Kaza sai kiga har abada baza su sota ba,ko kin dawo kin gyara bazai gyaru ba,a guji gulma da zagin yan Uwa da mutane gaban Yara.har Matan su Abbi basa kaunarmu kuma nine nake musu komai na rayuwa har daukan Nauyin karatun yaransu da komai na duniya har yau har gobe har yanzu da aka kawoki gidan nan yata.
Lokacin da Aayan yana secondary ya gama lokacin Allah ya karbi rayuwar Jabeer Babana tare da matarsa Hafsat sunyi Hatsari a jirgin sama.
Muna zamanmu da Dana har ya shiga University lokacin Nazo Nigeria neman Mahaifiyata Hajja don Babana ya bani Address kafin ya rasu,bata yi wani farin ciki ba Amma ganin nine yanzu me kudin sai ta saki kuka tace dole sai mun dawo Nigeria da iyalina ko ta tsine min nabi duniya,ba yanda zanyi da dukiyata da komai nawa na dawo Nigeria tare da Gina katafaren gidaje har Biyu a Abuja nace daya na dana Aayan daya nawa,ga motoci na Alfarma,har karatun Sojoji nayi shi yasa kike ganinmu da Securities a gidan nan harda jiniya in ta kama Sabo da nayi aikin soja na shekara Uku a kasar nan da Babban matsayi Sabo da tun ina yaro soja nake so shi yasa nayi aikin.
Ni da Matata Asiya mun dawo Nigeria dasu Hajja tare da kannena su Abbi duk na kwashe mu muka koma katafaren gidana dake Abuja,kudin Hajja data sata sun kare dama,ni na dauki nauyin su Abbi duk da sun girma suma da iyalansu sai da na Sa su sukayi Degree,na basu aiki a Company na nake biyansu albashi me tsoka,na siya musu motoci still ban fasa daukan nauyin iyalansu ba,amma sam ko me nayi musu basa taba Cemin ko an gode hasali ma sai daà su nuna bana musu komai a duniya,ko yaushe burinsu suga na tsiyace na talauce,burinsu ace a cikinsu ne daya yake da wannan arziki,haka Hajja ma komai nine me laifi su basa taba yin laifi Sabo su take so,abu kadan in nayi zata fara zagina,tana min baki,amma su ko me zasuyi baza ta musu Fada ba,kullum burinsu su ganni cikin halin bala'i, ba irin asirin da basuyi min ba Sabo da na talauce su gaje dukiyata Amma Sabo da karfin addua tare da tsoron Allah da kyakyawar zuciya,bana nufin kowa da sharri,bana shirka sai Allah ya kareni duk abinda zasuyi a banza,tunda na gane halinsu na dage da addua,ita kanta Hajja bata so ace nine me kudi ba cikin yaranta ta fi so ace Awwal,Sani ko Mustapha sune masu kudin ba ni ba,sabo da dama bata so na da ubana kuma bugu da kari ba ita ta raineni ba, sam babu wannan shakuwar ta raino tsakanin Uwa da Danta,nima ban damu da ita ba nafi son matar Babana Hafsat data rasu nafi Jinta a raina Sabo da mun shaku ta rikeni da Amana.
Makirci kulla tsiya ba wacce basa min,har Hajja ke Goya musu baya ana bin malamai akan dukiyata ta koma wajensu,kawai dai Hajja bata yarda ayi min asiri na cutar da lfy ta ba,tace duk da haka ni Danta ne na cikinta ko bayan ranta idan suka cutar da lfy ta ko raina bata yafe ba,duk abinda zasuyi na karbe dukiyata sunyi Amma ba abinda ya faru,su kuma Sabo da ita tasha wahalarsu suna jin maganarta amma shedan yafi karfin zuciyarsu don ko taya ma so suke suga bayana,hassada suke min ta gaske,ni kuma da yake dama a goge nake na waye nasan me nakeyi bana kulasu duk wata hanya na tosheta wacce zasu iya samun dukiyar tawa ko kadan ne sai daà in ni na basu da kaina, Aayan yaro ne me hakuri da kawaici tare da danne bacin rai Amma ta wani fannin yana da zafin zuciya,tun yana secondary na fuskanci yana da karfin sha'awa har cuta yake kwanciya a asibiti Sabo da sha'awa.
Saura shekara daya ya gama Degree a London mu muna Nigeria lokacin Hajja su Abbi sun zugata dole tace sai na dawo da Aayan Nigeria nayi masa aure mun zauna gaba daya Sabo da suna bakin ciki shi yana waje yaransu basa kasar waje bayan har saudiya da Dubai na kai yaransu sosai baki daya,da kudinsu ma suna fita kasashe suke duk ta silar arzikina, Asiya Matata kullum cikin kuntata mata suke tana ta hakuri har Mari tasha a wajen Su Abbi ban taba ce musu komai ba,wahala ba wacce bata gani ba,duk aikin gidan nan na abinci ita ke dafawa shi yasa ta iya girkin hausawa sosai,Hajja ta wahalar da ita sosai tare da matan su Abbi suka hade mata kai kamar zasu kasheta kullum kalar abinda zasuyi mata daban.
Ganin matsalar Aayan ta sha'awa gashi kyakyawan gaske kuma tana turai ina tsoro kar ya lalace sai na yarda nace ya fito da mata zan aura masa idan ya karasa Degree ya dawo Nigeria,ya kawo min wata musluma yar turkysh yana so,Amma Sai Hajja tace ban isa ba idan har na aura masa ita bata yafe min ba,nayi masa bayani ban boye ba,da yake Aayan akwai biyayya sai yace ya hakura to kar mamana tayi fushi da ubansa.
Su Abbi ne suka zuga idan Aayan ya auri Jar fata zamu kara yin kudi mufi haka arziki,dan danan suka nemo wata budurwa kyakyawa Bilkisu yar gidan Minister itama budurwar Khaleel ce,suka hada baki dasu Abbi domin a aurawa Aayan sai ta san yanda zatayi ta yashe mu tas,koda suka ce ga mata sun samowa Aayan sai da na bincinka na tabbatar ba yarinyar kirki bace Amma Hajja tace sai an aura masa ko ta tsine min,haka na hakura aka daura auren Bilkisu da Aayan yana London nace Hajja tayi hakuri Bilkisu tabi mijinta ya gama karatu sai su dawo tare,kafin Bilkisu ta tafi sai da suka gama tsafeta a gidan boka yanda zata mallake Aayan ta samo musu kudi,to na rigada na sani ina Yiwa dana addua shima kuma akwai addini yana yi na kara ja masa kunne kan rike addua,koda Bilkisu taje baiji yana sonta ba,ya kasa kusantarta,har ya gama Degree lokacin ya dawo Nigeria kullum da sha'awarsa muna hanyar asibiti ga na Hausa muna yi,kuma ya kasa kusantarta,har ya gano cewar tana fasikanci tare da khaleel,bai sake ta da wuri ba sai da ya tabbatar da ita ta gane kurenta,su kuma su Abbi ganin bata samo kudin ba ta kasa komai sai suka tsaneta suka koma azabtar da ita,duka zagi ba abinda basuyi mata ba har Aayan yaga zalunci yayi yawa ya bata hakuri tare da kudi me yawa suka rabu,yanzu haka ta dade da aure harda yaranta biyu.
Lokacin kuma Asiya Matata bakin ciki yayi mata yawa,lokacin kuma Hajja da kanta taje gidan boka ta samu nasara wajen Yiwa Asiya asiri tace dole sai na saketa,naki yarda don ina sonta,rigima mukeyi sosai,ta daina kula Aayan sam ta tsani Danta,tace indai ban saketa ba sai ta kasheni haka Aayan na rokarta tayi hakuri yana kuka nima haka na saketa saki daya ta ta koma kasarsu,bayan asirin ya karye na maida ita ba tare da kowa ya sani ba har Aayan,Shine ma dalilin da yasa yake jin haushin mahaifiyarsa har yau,na fada masa gaskiya Amma yaki fahimta yata,muna tare shekara daya da dawowarta ta samu ciki wajen haihuwa ta rasu Allah ya karbi abarsa,munyi kuka ni da Aayan sosai haka muka hakura.
Daga nan Hajja da kanta tace ta samowa Aayan matar aure Nafisa ita kuma yar talakawa ce Amma bata da tarbiya ni kaina tasha zagina a gabana,lokacin Aayan ya hakura bai sonta Amma dole ya bata hakkinta na matarsa,a lokacin kuma su Abbi sun masa asiri kwata kwata ya daina sha'awar mata ko kadan dan kar ma ya haihu a duniya zuriarmu ta yadu mu kara arziki,ba asibitin da bamuje ba,akace lfy yake,har na Hausa da addua anyi Amma sam,ganin haka yasa Nafisa ta bude bakin rashin mutunci wanda akan Aayan take saukeshi ya kasa Control dinta zagi da komai ba wanda bata yi,su