can ba kawai mu kwanta a nan, yau ban bari ya fara min komai ba,ni na fara Sabo da nayi Missing din mijina da yawa,kamar zan cinye masa lips tare da tongue haka nake tsotsesu da zafi zafi, dadi ya gama rufe shi kawai wani nishi mukeyi,Bana iya cewa komai sai dai nace Miss u Baby,Shima haka can kasa naji yace yau Dan Ficici za a bani,Lokacin ina jin dadina ya min yawa bana hayyacina nace a'a yau kamfatowa zakayi,yace Allah? Nace ai Kwaso kawai, yace an gama,ba karya kuwa ya kamfanta dan yau nafi ko yaushe jin jiki a hannunsa,ba karamar wahala nasha ba,tun ina kuka dadi sai da na koma na wahala,sabo da ban wani saba ba,kadan na saba Bazan iya dauke yanda yake so ba ba tare da na dan sha wahala ba yanzu sai nan gaba,har yau sabon nawa ba wani me yawa bane sai kuri idan anzo kuma na fara kuka ido ya raina fata,shi kanshi Aayan ya san iya limit din da nake kaiwa ban gajiba,shine yake so dole na saba sai yazo wanda lokacin na gaji sai ya dinga Dragging dina,Kuma ko yaushe yana ganin ci gaba tunda kullum ina kara samun ci gaba.
Sai da ya samu nutsuwa muka yi wanka na gasa kaina sosai mun kwanta again yana Sa min Albarka yana jin dadi yace lallai yan matana yanzu ana ta girma kullum, tnx alot My Queen,jikinsa na shige nace ni ba wani sabawa karka kala min ina yar yarinyata.dariya yayi tare da kara kankameni yana shafa min gashina zuwa gadon baya na yace muyi bacci sai gobe kuma zanga wanne salon za a nuna min naji na yau ya hadu kin ba da style,dukan wasa na masa ina jin kunya na kara boye fuskata a kirjinsa ina dariya kasa kasa,wata Kalma na rada masa a kunne wacce saura kadan ayi second round da kyar na lallasheshi yace to ki daina kunna ni,nace kyis na kasheka to,Dariya mukayi gaba daya hannayensa suna saman Mazaunai na yana shafasu cikin Salo iri iri wanda ni kaina hakan yana min dadi.
Abbi ne kwance saman gadonsa yana nazarin duniya tare da mamakin canjawar komai da ya samesu a rayuwa,gashi har sun lalace suna ramewa sunyi duhu sosai kamar basu ba,dama ance duk wanda ya saba da rike kudi yana shan wahala idan karayar arziki ta sameshi,kuma dama can taimakon su akayi talakawane gaba da baya, duk gashi har sun zama abin tausayi duniya ta juya musu baya,wai sune a wannan matsayi, Hajja ce ta shigo dakin Abbi tana fada mene amfanin kwanciyarka a gida da tsakar rana haka baza ku fita neman na kanku ba,kudin hannuna sun kare saura Naira dari kamata yayi ko yar dubu biyu ina rikewa a hannuna ni bana iya rayuwa ba kudi,Abbi shuru yayi bai ce mata komai ba Sabo da bakin ciki da me zasu ji, Hajja tace au dan Iskanci kana jina ina magana kamar kaga Kashi eyee,ni na daura muku talaucin idan kudin banza ne me yasa baku yi zuciya kunyi ba, Haba Hajja me nace miki kuma,ya kike so muyi kina gani karatun su Sabeer ma nema yake ya tsaya,ba komai bamu da komai sai bashi ma da muke ci ki dinga tausayinmu mana,idan ba sata kike so muyi ba me zamuyi miki? Hajja Hawaye ta share wai an ci mata mutunci,ta fice fuuuu ta bar Abbi yana bakin ciki.
Haneefa ce ta fito ta cikin yan uwanta Maza da mata tace to Jama'a ku kalli atamfar jikina ta gaji da wanki har ta kode tana neman jemewa,dama kayan namu kadan muka ebo,Meenal ce ta fado da gudu tace Bazan ji kunya ba bayin Allah nasan masu hankali ne gaba daya dan Allah me Pad always ta san min ko a min karo karo na kudi na siyo,Sajeeda tace ai duk dan kwalayen Ka kayana sun kare a kunzugu rannan,sai dai kiyi amfani da dankwali, Mujaheed da Khaleel suna dariya suka ce kadan kuka gani Yara tun yaushe muke cewa kuyi aure tun da gatanku samari na rubibinku kuka ki gashi na pad ma ya gagareku.
Meenal ta kalli Khaleel tace dan Allah bani gajeren wandon nan naka da naji zaka jefar naga cotton ne sosai zai sha ruwa a jikinsa,Khaleel yace ko kunya bakwa ji wai a gabanmu kuke irin wannan kalamai ba tarbiya ba komai sai kije yana cikin bakar jakar nan ki dauka,Meenal da Sauri taje ta dauki gajeren wandon Khaleel wani me nauyi cotton tasa reza tare da yankashi kashi Kashi ta linka kamar dai Pad haka ta dinga sawa tana kunzugu dashi.
Matayen su Abbi talauci ne ya ishesu gaba daya suka ga gwara su tafi gida tunda yanzu ko sabulun wanka da wanki Rasawa akeyi a gidan,Nan suka tayar da rigima sai an sakesu,Umman Ameer tace ita dama tana jin Haushi an rabata da Danta Ameer ta gaji,Hajja tace ba shegiyar da za a saki kamar yanda akaci daula dasu dole Asha wahala dasu dama in sun koma dangin nasu ma dai talaucin zasu tarar Sabo da duk kanwar ja ce.
Yaji sukayi wai sun tafi gida sai sun huta zasu dawo,Yaran gida suka ce sama dawo idan sunji Wahala kar wanda ya hanasu,suna shiryawa suka ce mu munyi gaba,Su Mujaheed suka ce a dawo lfy Allah ya kiyaye Hanya,tuna ninsu yaran zasu damu sai suka ga kowa harkar gabansa yake,Sabeer yace mu ai Aayan da Daddy kadai ne zasu ce zasu yi yaji zuwa turai mu damu Amma kawai ba abinda ake tsinana mana ace za a damemu,common toothpaste mu muke siya,sabulun wanka da wanki ba a san a bamu ba,Abbi yace Kai rufe mana baki marasa kunya,Sajeeda tace ai wlh sai daĆ a godewa Allah Amma ya dace ace a cikinmu akwai Karuwai,akwai yan shaye shaye tare da kasurguman barayi sabo da Halin da muke ciki a gidan nan,kowa kansa ya sani kowa ta kansa yakeyi,Hajja tace ai duniya ce yanzu ma kofa a bude take zaku iya komawa Karuwanci da shaye shaye,sace sace kuwa na wanda kuka gani shi zaku dauka dan ni nawa yafi karfinkuš , Abbi Sani yace Haba Hajja addua ai zaki yi musu ba kice suje suyi ba ai yarane yanzu idan mune zaki so yaranki su dawo haka?.
Kai Sani ka rufe min baki shegen kunne kamar malafar Kwadi,Dariya aka dauka gaba daya har yaran Sabo da kunnen Abbi Sani kamar Malafa haka suke kuwa,Abbi Mustapha ne ya buga musu tsawa,shima Abbi babba yace zaku bar palon nan yan Bantan uban Yara.
Khaleel ne yake ta masifa a tsakar gida an sace masa sabulun wanki wanda da kyar ya hada kudin ya siyo na wanki dan Naira Hamsim wani kato zai dinga cancanawa yana wanka dashi,daga ajiyewa ya juya baya zai dauko bokiti kafin ya dawo har an dauke sabulun yan mintuna kadan,Nan ya fara fakon wanda ya dauka duk wanda ya shiga wanka ko me wanki sai ya duba sabulunsa mata da Maza,Meenal tana fitowa daga wanka ya ganshi a hannunta ashe ita ta sace ta wanke panties dinta tunda period take dole sai da wanka da wanki,Kamar zai cinyeta haka ya kwace abinsa,dan ya bar mata tace kazanta ta na wanke dashi fa period ne duk na shafa masa na wanke da kyar ake gane kalar sabulun dazu wlh dan baka gani ba yanda ya rine kamar jar color aka Sa,abin kyankyami har wari yakeyi, Khaleel ya gano so take ya bar mata shi du, yace ai ko a Abbatuwa mayankan dabbobi aka jefa shi cikin kogin jini bani abina dan Uwarki mayya wlh idan na kara ajiye abina kika dauka sai kin gane kurenki,Meenal tace jaraba akan sabulun wankin?Yace ae din,to yi hakuri dan Allah ka bani na karasa wanke daya pant din nawa yanzu na tuna ban gama ba kaima kasan sanda muna daula bakwa sanin ma time din da muke period yanzun ma babu ce tasa ba yanda zamuyi dole muke yage yar kunyar.
Khaleel yace ungo badan halinki ba dan dai kawai kina san min Vaseline dinki ne Allah gashi nan saura ki karar dashi,Na gode cewar Meenal ta koma toilet ta gama ta fito ta bashi sabulunsa,Mujaheed ma da shi yayi wanka haka mata da mazan kaf ba yanda Khaleel ya iya haka kowa ke zuwa yana rokarsa dashi sukayi wanka,Abbi ma yace kai Khaleel bani sabulun sodar nan naka zan cude jikina dashi ina so na fita neman Ameer ruwa a jallo dan ubansa ya zai manta da iyayensa,Khaleel yace kune fa kuka koreshi ai ni ya birgeni wlh,gashi sabulun dan Allah nasan wankanka dadewa kakeyi karka silleshi Abbi.
Harara Abbi ya zuba masa ya wuce yayi wanka sannan ya kwalawa Meenal kira tana zuwa yace Bani Toothpaste naji ance kece me shi a gidan nan,Meenal tace Vaseline gareni ni Katon gaske wlh ko wanka zaka yi dashi ina dashi kamar tulu yake Sabo da girma saurayina nasa ya kawo min shi maganin gidan yawa,Meenal Me Vaseline kenan,Abbi yace dauko min shi na shafa,wace to me abin goge baki?Haneefa ce me su manya manya ita take matsowa kowa da kanta duk yanda kuke da ita sai daĆ ta Matsa ma da kanta kar ya kare da wuri,Abbi yace kirawota ta bani,Tunanin Abbi ai shi Babbane Haneefa zata bashi ya matsa da kansa yanda yake so sai kuwa yaga tace kawo Brush din,da mamaki ya kalleta ta kuwa bude ta dan difara masa kadan tare da cewa kar ka raina Abbi rayuwar sai da tattali,Hajja ma tazo tace Haneefa ashe kece me makilin matso min a nan na goge bakina,Haneefa tace rayuwa sai Imani Hajja ku tsofaffi har wani goge hakora kukeyi idan ba iyayi ba da ganin arahar Sa me zaki goge hakora kamar Tsinken tsire duk sun zube saura dai daiku kici goronki shima yana wanke muku baki tayi tafiyarta,Hajja tace ni me na tare musu da aka rainani,ta fara kiran Khaleel sai da yazo jikinsa ba riga, tace wai kai kullum baza ka Sa riga ba kai kenan daga dogon wando sai gajere,Khaleel yace Am too sexy ne Hajja wlh shi yasa nake nuna muku baiwa ya fada yana dariya,Hajja tace ina wata baiwa a nan Da Ameer dina ne ya fada sai na yarda dalla bani sabulu na wanke jikina, Khaleel yace Rayuwa sai Imani Hajja wa zaki wa wanka ke ba miji ba,yo ko miji gareki me zai ci da ke ki sha zamanki haka da Allah wannan Asarar sabulu zaki mana,Hajja ta balbale shi da masifa ko wanne dan iska bani da iko nayi magana sai yace wani Rayuwa sai Imani wata sara kuka samo kuma ko kuwa ni kuka raina.
Khaleel dai yayi tafiyarsa,Mujaheed ne yazo ya wuce Hajja shima ba Riga sai 3qtr ya tattaro hantsar Wando ya rike gaba daya yana tattalewa yana tafiyar yan gayun samari ga uwar suma duk ta cukurkude,Hajja tace haka dai aka iya yan iskan Yara ayi aure tun tuni kuka ki yi sai aikin rike hantsar Wando Sabo da jarabarbu ne ku mayun mata,Hajja bata san gayu bane ta dauka sha'awa ce ko Iskanci ne ke damunsu,Mujaheed yana Jinta yace Hajja sai Imani ai ko Ya kika ce,Tsaki ta ja tare da tauna
Goronta,Sabeer da Aliyu ne wanda sun kai 24yrs yanzu su kuma boxers ne dan karami suka Sa da yar Singlet ga abar tasu nan a Wando ana gani duk ta mike da wata yar kwarababbiyar waya karama a hannusu suna dannawa suna kallon pics din yan matan turawa kusan tsirara suke,Hajja nan ma ta rasa uwar da suke sai kus kus suke suna dariya suna kallon waya,ta kalli wandonsu a ranta tace na shigesu ni Hajja kar fa a fara cikin shege a gidan nan ayi yar gida tunda ga yan mata nan kuma ba muhararram juna bane wasu to matan ma ya suke bare Maza,Ganin Hajja na Sa musu Ido Sabeer yace Allah wadaran karamin gida sanda muna gidanmu babba wa yasan me wani yakeyi Amma yanzu komai kayi akan idon wani,Aliyu yace muyi maganinta suka samu Hajja tare da cewa Hajja kinga wasu dan Allah sun hadu? Nan Hajja ta kalli waya ai sai taga Mata kusan tsirara,Sabeer yace wannan zan aura Hajja tayi? Duka Hajja ta rufeshi dashi tare da cewa wlh in dai ina raye baka Isa ka auri wannan ba,Aliyu yace musulma ce sunanta Rasheeda,Hajja ta dauka da gaske ne ta dinga tsine tsine ba a Isa ba,kuma tace sai ta fadawa su Abbi,Sabeer yace Hajja masu kudi ne fa yar gidan shugaban kasar Ethiopia ce fa kinga mun washe,sabo da son kudi Hajja sai tace ya sunanta kace? Yace Rasheeda,Hajja tace ayyo yanzu naji zance ai tun daga sunan ma kasan musulma ce,a ina kuka hadu a Internet din naku?Sabeer yace ae tace kwanan zata zo ma kuma zata Aiko min da yar million goma na sha ruwa,kirji Hajja ta dafe tare da cewa kace ina gaisheta kakarka Hajja sunana,yaro kayi dabara wlh kafi su Khaleel hankali ina kallonku yara ashe kune manyan,Aliyu yace Hajja kinji tana kira ma a waya kash Amma bamu da kudin Sa kati kuma dole sai da kati so muke mu tura mata accnt Number tace Sauri take zata turo kudin gashi bamu da sisi,Hajja da Sauri tace zan baku rance ina jin kamar Ina da dubu biyu a hannuna nawa ne Katin da zai isa? Sabeer yace tab ai sai dubu biyar yanzu kuma babu sai daĆ ayi asarar milliyan goma kenan Hajja ki taimaka idan ta turo zamu baki milliyan Uku a ciki kyauta,Hajja dadi ya rufeta tsohuwa da son kudi nan tace to dama dubu shida ce ta ragemin a duniya ga biyar sai na rike daya ni kuma,Nan Hajja ta zaro dubu shida a jikinta wanda da haka kawai ne sai daĆ a mutu a gidan baza ta iya siyan ko sabulu ba.
Sabeer suka karbe dubu biyar da Sauri suka dauki dubu daya daya,dubu Uku kuma suka siyowa kowa na gidan sabulun wanka da wanki,suka bawa matan kudin kitso,mazan kuma na aski,har pad aka siyawa matan kowacce biyu biyu Sabeer yace gashi naga Alama boxers dinmu an fara sace mana ana kunzugu dasu, har da Sauran dan abinda ba a rasa ba duk sun dan siya me araha,karshe dai Sabeer dari biyu biyu ce ta rage musu,Duk yaran gidan sunji wayon dasu Sabeer suka hadawa Hajja sai dariya akeyi a boye kowa ya washe yau a gidan har kifi soyayye suka Dora a saman shinkafa da wake kowa daya,su Abbi da Hajja basu san me akeyi ba,dama matayen su Abbi sunyi yaji su Haneefa ke girki duk da basu wani iya ba wahala tasa har sun saba.
Kwana biyu Hajja taga su Aliyu shuru ba 5k dinta ba milliyan Uku sai nemansu take Amma sunki yarda ma su hadu wasan buya sukeyi.Idan taje dakinsu sai su Khaleel su boyesu kowa yace basa nan sun fita,Hajja ta koma me gadin dole a Palo take kwana wai zata ga wucewar Aliyu ko Sabeer amma sai su wuce ma bata ganesu ba.
Washe gari da Safe ma sai da Aayan ya kwashi Harka ba daga kafa kamar ma baya tausayina, kamar yanda su Meenat suka saba haka sukayi komai girki da gyaran gidan su ma yan aiki suna nasu,sai 11am muka fito bayan Aayan ya shirya ni yayi min komai,ba su Meenat gidan shuru sai guntuwar paper na gani sun ajiye min,.......wai mun tafi gidan Ammah tare da Ameer sai dare.
Aayan yace ina suka je? Gidan Ammah na bashi amsa a takaice, da kansa yayi Feeding dina muna hira sama sama yana tsokanata wai jiya naji dadi na fara sabawa,na fara Kukan shagwaba ina Ni ba wani dadi,yana mun dariya har muka gama,yace je ki shirya muje gidan Ammah sauri ya furta ba alamar wasa,da Sauri na tashi na je sama nasha wata dakakkiyar shadda yar Senegal tasha aiki Dark purple aikin kuma da light blue and pink na fito kamar wata Hajiya,Shi kuma shadda Light blue kamar munyi ango sosai muka yi kyau.
Jerawa mukayi wow yau abin kallo ne mu, nace muje wajen Daddy mu gaisa,Daddy ba karamin farin ciki yayi ba da ya ganmu haka sai albarka yake sa mana sannan yace mu gaishe da Ammah, yau ba Driver bane zai tuka mu kuma ba escourt mu biyu kawai,da kansa ya zagaya tare da bude min gaban motar yace ranki ya dade Allah ya taimakeki shiga,Kafadarsa na dan buga kadan ina dariya na shiga ya rufe sannan shima ya zaga ya shiga yaja motar cike da nutsuwa muka bar gidan,Ba wani nisa me yawa bane sai gamu a wani gida dan babba me kyau sosai yayi kyau gaskiya,me gadi ne ya bude mana gate ya Cinna hancin motar Sa cikin gidan,gidan yasha tiles da flowers yayi kyau sosai,jikin wata katuwar Bishiya muka hango su Meenat tare da Ammah zaune a katuwar tabarma suna hutawa,Ameer da Yarima suna gefe suma,Hajja da Katon tire a gabanta tana kwada musu zogale da Kuli yaji hadi sai nishadi sukeyi abinsu.
Aayan ya kalleni yaga ina murmushi ni kadai ina ta kallon Ammah muryarsa naji yace muje ko? Da sauri na dawo hayyacina na daure fuska irin ba dadi naji ba,murmushi yayi yace kinfi kyau a haka muje dama naji jiya Ammah tace duk tafi so taga kina fushi dariya kike bata,da Sauri na washe bakina nace na fasa fushin tunda tana so,na fito ina ta fara'a ina murmushi wai Ammah ta gani kar taji dadi ma,Aayan yana ta dariya a ransa,a hanya yace Ammah tace tana so taga kina fushi kinki gaisheta,nace aiko sai na gaisheta din,Aayan yace ke duk abinda bata so shi zakiyi ko? To ki daure dan Allah ki nutsu tana son ta ganki a nutse cib dake,Nace haka tace?Yace ae,na girgiza kai nace za a gani wlh Bazan nutsu