x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 22 - KASUWANCINA

  • 63001 words
  • 66000 words
  • Out of 176000 words

Category: Romance Story +18

Views 183

30 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
cikin kudinki gobe zamu fita shopping da kaina zan kaiki.

Ai kuwa farin ciki ya kamani nace Allah ya kara budi Ranka ya dade,a hankali nace Yanlabai a Sa nayi bacci cikin kudina ka zame dubu Uku tunda na saka aiki nima,dariya abin ya bashi yace to shike nan cikin kudinki na Kasuwanci zan cire kudina tunda yanzu ke kika nema,nan ya fara min wasu Salo a kunne na yana lallabani kamar masoyan gaskiya,na kara yin wata mika yace har naci dubu biyu,nace a'a ai banyi bacci ba dubu daya da dari biyar kaci dai,Dariya yake ta min ni ko lokacin hankalina baya tare dani ban san sanda nayi bacci ba.

Washe gari da Safe Hajja tayi shiri sosai ta je wajen Daddy yana kwance ta dinga zuba masa masifa da zage zage karshe tace wlh wannan yarinyar da kasa ya auro mana Sabo da mugun halinka Sabo da baka kaunar yan uwanka to wlh sai nayi fata fata dasu,ka fadawa Danka tunda ka Isa dashi tun wuri ya fara shirin sakin wannan matsiyaciyar ko kuma kai ka fuskanci fushina,kar ma kasa ya saketa kyaleshi da kaina zanyi maganin abin ka sanni kuma ba a taka ni a zauna lfy,haka Hajja tayi ta sambatu har da na mahaukata ma kamar sabon kamu,ficewa tayi a fusace sai wajen Matar Abbi nan ma tana takama da gadara tace Karimatu jiya wanne yan iskan ma'aikata ne suka dafa min cabbage soup dinn nan me bauri Maggi har saman kaina,ke kuma da yake shashasha ce kika bari suka kawo min Sabo da kun rainani,nice na Haifa muku Mazajen da kuke aure dai baku Isa kun canja musu Uwa ba yan iskan surukan Zamani mutum da yayansa ace za ayi maka iko dasu,matar Abbi da yake Hajja ta shanyeta haka ta durkusa tana ta bata hakuri,tsaki taja ta figi Jakarta tare da fadawa kitchen ta dinga cin uban yan aiki kamar zata yage bakinta sai da ta gaji tace ta canja dokar gidan taga cewar yan aiki suna nema a hada baki dasu a kasheta jiya an mata girki da farin Maggi me hawa kai dan ta kusa suma.
Tana gama masifarta ta hau mota Driver ya kaita har Airport sai Taraba state can kauyensu zata je wajen bokayenta wanda take ganin kamar malamai ne na Allah ka h.










Bakwa Sharhi fans








AsmaBaffa
[1/15, 8:41 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

KASUWANCI NA






61-65






Official







By
AsmaBaffa









Page nakine Zainabsanusi78 Allah ya bar kauna.


Godiya da jinjina me tarin yawa TASKAR SURAYYARHMS na gode da Sharhi kuna kokari, haka ake son gp.







Bata zarce ko ina ba sai wani kungurmin kauye wanda mota bata shiga sai dai ka sauka ka hau machine a karasa da kai wata hanyar ma sai dai ka karasa a kafa,wata yar bukkar kara ce kamar ta Fulani, daga kofa Hajja ta tsaya tare da cewa Gafara dai Malam,yace Allah ee Mana Hajiya kece tafe yau? Hajja tace ae Wlh Malam ta furta tare da shiga dan karamin dakin,gefe ta zauna suka gaisa yana ta faman washe baki,tsoho gashi wani mugun kazami bakinsa duk goro yana yauki,hakora Yellow dasu shar in banda wari ba abinda yakeyi, farcensa zako zako kamar na kanti duk dirty a ciki,suma duguzum da wani lalatattun kayansa,yace Hajiya da Alama wata rigima ta taso ko,Hajja tace kwarai kuwa abinda ya kawoni kenan da waya zan maka Amma zuwa da kai yafi Sako, ko ina a dakin wasu litattafan ne na sunayen taurari da Alama taurari yake bautawa dasu yake aikin shirkarsa.

Hajja tace Malam kasan idan aiki babba ne bana bukatar a duba min,bana bukatar a hango min meke akwai dan kar ma naji wata matsala,kawai aiki na kawo cikin Uku ayi daya,wannan takadarin jikan nawa Aayan,kasan yayi aure to matarsa naga tafi karfina irinsa ce bata da kirki,nan take yace ba sai kin karasa ba na san komai, tace to aikin da nake so shine ko Ya saketa har abada kar ta dawo hannunsa,idan bai yuwu ba ya kara aure ta koma baiwa,idan bai yuwu ba ya tsaneta inda take kar ya raba ko ita ta tsaneshi da kanta,Malam ya dago yace me sauki kenan Amma bari muji abinda su zasu ce ayi wato aljanun da yake aiki dasu kenan,littafin taurarinsa ya bude da carbi sai wata kwalabar turare yayi shuru yana kallon littafin sai daí kaga bakinsa na motsi yana magana shi kadai yana to..to...ae...yawwa...ae...uhum...uhum..suna bashi Umarni kenan.

Sai da ya gama sannan ya dago yace Hajiya baki taba kawo aiki me wahalar wannan ba,da farko dai sunce jikanki kullum cikin addua yake baza su iya shiga jikinsa ba ko sun shiga wahala zasu sha,na biyu kafin ma su shiga jikin nasa zasu kwashe shekaru suna fakonsa sai ranar da ya shagala da duniya sannan su shiga,ko sun shiga din dole fita zasuyi da kansu, aikin kuma bazai yuwu ba sai dole an shiga jikinsa,sannan ita yarinyar idan an Sa ta bar gidan Jikanku shi zai sha wahala ta dalilinta zai iya rasa ransa ita kanta yarinyar ba a zaune take ba kullum Azkhar take ba fashi,kuma kin san asiri ma yana tadda hali wannan taurin zuciya ce dasu gaba daya idan ma anyi suna da karfin zuciya,amma abu daya za ayi shine a hanasu kwanciyar hankali da zaman lfy idan kin yarda idan kuma kina ganin bai miki ba to fa a wannan lokaci sai daí kije wajen wasu duk rashin Imani na wannan yaron yasha kaina,dama kuma nasha fada miki,Hajja ta nisa tace ita yarinyar a batar da ita ko a haukatata mana gaba daya in yaso Shi ya kashe kansa dan ubansa,Malam yayi dariya yace Hajiya har yau kina nan da Halin nan naki na mugunta Amma kije zamuyi iya kokarinmu,ni kuma har India zan kira manyana dole ko ta yaya ne sai an miki abinda kika ce kina so,tunda kin yarda ko mutuwa ma jikan naki yayi baki da damuwa, Nan Hajja tace da dai yafi a dage sosai ta zube masa makudan kudi ta bar wajen,tayi waya da malamai da dama duk akan aikin sannan taje wajen wasu ma sunfi biyar Sabo da a hada karfi da karfe kuma sun bata tabbacin ba matsala.

Makara mukayi don har rana ta fito bamu sani ba muna manne da juna muna bacci,lokacin Meenat har ta hada Breakfast da komai,Maeesha kuwa gyaran gidan ta fara kasancewar yau Ba schl,ni na fara bude ido na da kyar na iya zare jikina cikin nasa sabo da gaba daya ya makalkaleni ta ko ina ko juyi bazan iya ba,wannan ne ya tashe shi daga bacci,muna hada Ido na runtse ido, kawai sabo da kunya,Murmushi ya saki har ina jin sautinsa da sauri na sauka daga Bed din na shige hadaddiyar toilet dinsa nayi Brush da wanka kana na dauro Alwala na fito dan guntun Towel dinsa na daura na fito ina goge gashina,yana Saman Bed ya tsaya sai kallo na yake sannan ya mike shima ya shiga wanka,kafin ya fito na idar da Sallah na shafa Lotion dinsa tare da turarukansa har gashina na gyara shi sosai ina haka naji muryarsa yace kawo min Towel dina ko ki bude Wardrop ki miko min new, wai dan kar a bata kaya da yawa nayi Sauri na dauko Jallabiyarsa fara nasa dan tight short dinsa na Sa Jallabiya ba karamin kyau nayi ba duk da tayi min yawa kowa ya kalleni yasan nayi kyau.

Toilet din na nufa na manta kawai na murda Handle na shige gaba daya da Sauri ya juya min baya yana ta masifa ban kalleshi ko daya ba na fito da gudu nace kayi hakuri mantawa nayi wlh na kara dan tura kofar na dan tura hannu na tare da mika masa ya karba ya zuba su a washing machine sannan yace miko min wasu ki bude part din karshe,da Sauri na bude na dauko tare da kara miko masa ya amsa ya daura sannan ya fito ina dariya nace na gani dai abin tsoro ma, murmushi yayi yace ke kika sani kuma,Wajensa na karasa kawo na tayaka Allah na iya ni nake shirya su Meenat ma fa, na zuba Lotion a hannuna nace to juyo mana ni ko dama wayo zan masa dan na taba masa jiki ne Sabo da yana birgeni,shafa to kiyi kuma Sauri sallah zanyi na fara murza masa Lotion ina ta murmushi dan fatarsa sai laushi kawai,nazo waist dinsa na tsokaneshi Sabo da naga baya so a kalle masa tsaraici nace kwance towel din nayi Sauri mana dariya yayi yace a'a ki kwance da kanki kai.

Ina gamawa yace saura kaya to ya dauko wani Yadi shara shara fari me shegen kyau karamin dinki fitted na Maza yan gayu,da Singlet sai short ya miko min karasa aikinki, na karba kuwa ya dauka zan wani kasa sai ya karbe yasa Boxers dinsa,nasa masa singlet yasa wandon kayan na Sa masa rigar, da Sauri ya gyara sumarsa tare da fesa turaruka ya tayar da Sallah,ni kuma na fita tare da sauka kasa na duba na ga me su Meenat suka dafa idan basuyi ba nayi,tea suka sha da Doya da kwai kawai,sai farfesun kaji,na dinga masifa kun san dai bazan fito da wuri ba dan Iskanci sai kuyi wani Doya kawai da tea mijina yana ci ne? Ba sosai yake ci ba,Meenat tace au bamu birgeki ba a hakan? Ke da kika ce hira zaki je kuyi kawai ki dawo sai yanzu zaki fito duk hirar ce tun jiya? Shike nan bacci bazai kwasheni ba nama kwana din ina ruwanki ke zaki tsara min abinda ya dace nayi kece gaba dani ko nice gaba dake? Daga yau ma acan zan dinga kwana sai me kuma? Dariya Meenat tayi kawai tace ah mun gane, to gyaran gidan fa? Ya kika gani ya miki ko shima mijinki bazai masa kyau ba? Dubawa nayi nace wannan ai nasan kun iya dama kuma na gani kunyi kokari,bari to zo ki tayani muyi masa Kunun Gyada,da su muka shiga kitchen din suka taimaka min Dan danan muka shirya lafiyayyen kunun gyada,na fara soya dankali suka ce sun gaji su nace to kuje ku huta,suna fita sai ga Aayan ya shugo kitchen din a bayana ya tsaya kamar zai shige jikina ina jin kamshinsa a saitin kunne na yayi magana a hankali yunwa nake ji fa ki danyi Sauri,yana fadan haka ya fita ya barni nan ina jin jikina wani iri.

Tunowa nayi da zan fara yanga ta na daina cin abinci a gabansa da yawa Sabo da kar ya rainani gashi kuma bana koshi da wuri sai na shirya dabarata yanzu duk girki sai na samu na zuba a kitchen din in ci abina na koshi sai na rage space kadan idan anzo ci a dining sai aga ina ta yanga naki cin abincin da yawa sai dai na dan ci kadan,
Cikin rashin Sa'a yau nace zan fara tunda tare zamu ci a dining,na zauna na ebi chips din na zuba kunun gyada ta,farfesun kajin dasu Meenat sukayi nan ma na zuba Naja gefe ina cin abina a nutse,Kawai Aayan yazo zai shigo kitchen yaganni kicif ina cin abina,nan take ya gane me zanyi don Allah ya zuba masa basirar gane abu,dariyace ta kamashi me karfi ya danneta,ya juya palo dan kar na ganshi naji kunya.
Saida na koshi sannan na sha ruwa na gyara lips dina na fito na shirya Dining na gyara kitchen din na fito,Aayan yana Dining yana jirana nazo na zuba masa ni kuma na zuba komai dan kadan kamar dan yaro ne zaici irin yar gayun nan, yaga ina ta wani juya cokali a ciki ina tsakura,shiko yana ta cin abinsa har farfesun,ya kalleni yace kici mana wannan dan abincin nufinki zaki ci? So kike ace bana baki abinci ko so kike ki rame? Baki na tabe ina yatsina fuska na ce ya isheni haka,ya kalleni tare da danne dariyarsa yace me yasa kika daina cin abinci ko baki da lfy? Na shagwabe fuska nace ni...yanzu bana son wani ciye ciye da yawa,yace to kiyi hakuri kici kinji yanda ya zage yana ta lallabani sai naci abinci ni kuma ina botsewa haba sai naji wani dadi nace lallai Aayan ya fara sona sosai ji yanda yake ta kula dani yana damuwa sai naci abinci,ni kuwa sai yanga nake wai ni a dole na masa wayo ban san shike min wayon ba.

Kusa dani ya dawo yace Dole sai ya bani da kansa nafi ci na koshi yaga wasa nake da cikina so nake cuta ta kamani,nan take na Tsorata Sabo da na koshi taf cikina ya cika,ina ji ina gani ya zauna ya dinga dura min abinci da kansa,kamar zanyi amai Amma yaki saurara min,Dankali da Kunun gyada ya dinga danna min,ya dawo kan farfesu,tun ina dannewa nace dan Allah na koshi Amma dama Sabo da mugunta ya shirya min yace sai na cinye ya san ina da ci,Idona ya kawo Hawaye na fara kuka ina bashi hakuri Amma yaki yarda sai cusa min yake,sai da naci me uban yawa wanda kwakwaran motsi nayi sai nayi Amai,ya miko min yatsun Sa da ya bani farfesu dasu yace tsotse abinki,haka na tsotse yatsun tas shi kuma yanda nake tsotsar yatsun ne ya tayar masa da hankali nan take ya birkice,Sha'awarsa ta motsa da kyar ya dan danne yace ku shirya da yamma zamu fita zan dawo na daukeku,hararsa nayi nace to ina turo baki akan dura da yayi min.

Ameer dasu Mujaheed ne zaune a katafaren Palonsu suna game suna hira,Mujaheed yace ni fa guys wlh ina son beb din nan kanwar matar Aayan Meenat take ko wa? Khaleel yace ai yarinyar tayi ne ina fada ma gaba dayansu Allah ya zuba baiwa Barin ma matar Aayan gaskiya Ameer Banga laifinka ba,Ameer yayi dariya irin ta yan duniya sannan yace baza ma ku gane ba sai nan gaba,ni na hango abinda na hango,kullum da ita nake kwana nake tashi,Sajeeda dake gefensu taji haushi dan ita Ameer take so yanzu, rai bace tace haba Ya Ameer mene haka wannan cin fuska ne ina wajen fa wlh zan fadawa Abbi kasan dai yace Aure zai mana,Ameer ya kalleta shekeke ke dalla rufe min baki me zaki kaimin gidan nawa? Har daki kike bina muna aikata abubuwa zaki zo kice wani na aureki,Amma kasan dai ai kaine kace ba komai zaka aureni tunda kaine ka lalata ni,Mujaheed yace ko kunya bakwa ji ku rufe mana baki Hajja in ta dawo ku fada mata mana a fasa can da matsalarku,Cousins kenan dama haka akeyi ko mai ace cousin dina ne Kaza Kaza kullum kayi tunanin yan uwan ashe ana nan ana aikata masha'a tare,Mata har gidan kani ko wan babansu zaka ga sun tafi hutu an samu Cousin mace ko namiji ana ta shekewa,su kuma iyaye tunaninsu zumunci akeyi sai suyi ta jin dadi Allah kyauta.

Hajja ce sanye da glass dinta na ido ta zauna a Cikin jikokinta nan Fa Sajeeda tana kuka tace Hajja kinji wai Ameer bazai aureni ba, Hajja ta gyara zama fatarta duk tayi yaushi tace shi din banza,ya Isa ma,shi waye shi wlh wlh Allah daya sai anyi wannan aure kwanan nan ma kuwa ko sama da kasa zata hade,waye kai? Ka Isa nayi magana nasa doka da hukunci ka tsallake ko Ubanka Mustapha bai Isa ba bare kai karamin shege,nan Hajja tayi masa tatas yayi shuru yana ji Amma ya rantse indai Sajeeda ta shiga gidansa sai ya kusa hallakata da muguntarsa ita kuwa Sajeeda murna takeyi don tun da ta taso a duniya take son Ameer sosai Sabo da ya hadu shima ba laifi.

5:30 muka gama shirinmu tsaf mun hadu karshe yau kamar wata Sallah haka muka dau wanka,Aayan kuwa bamu san a inda ya shirya ba haka muka ganshi ya shigo cikin dakakkiyar shadda sea blue yanda yayi kyau ya zarta hankali ma,Maeesha ya kalla yana zuba kamshi yace kinfi kowa kyau yau,nan take naji haushi ni bai yabeni ba ai ni ya dace yace nayi kyau ba su ba,Meenat kuwa yace Yau kamar Queen haka kika koma nan take Meenat ta fara dariya tana tnx Yaya,Ma'eesha kuwa ta makale a jikinsa,ni da yau nafi kowa haduwa yanda nayi kyau har ya wuce misali Amma bai ce nayi kyau ba sai su Meenat,kasa danne fushina nayi sai kumbura nakeyi haka na karasa Sa sarka ta na dauki mayafi na da jaka nace muje Meenat da Ma'eesha suka yi waje ni kuma zan fito yana Bedroom din namu ya jawo hannuna na fisge abina,ya kara jawoni na fado jikinsa gaba daya,na sadda kaina kasa a saitin kirjinsa,hannaye biyu yasa ya dago da fuskata yana kallon lips dina tare da cewa wa kika sawa jambaki kuma? Nace masu sona na cikin gari idan mun fita nake Sa ran zasu kalla suji dadi, bakin ciki ne ya ziyarce shi me tsanani Amma sai ya danne ya hade bakina da nashi ya dinga sha,sai da ya shanye jambakin tas sannan ya dauki wipes a saman mudubi na dinga tsalle ina son guduwa amma ya rikeni tam da kansa ya goge min fuska tas ba abinda ya bari na kwalliya ta,hakan ma yaga baiyi ba sai ya jani toilet fuska ba walwala ya danna kaina a saman sink yasa soap ya wanke min fuskar tas ya goge min da towel nayi wani mugun Fresh jajayan lips dina suka fito natural sai na kara wani kyau kowa yasan Natural kyau na gaske nayi,ga kayan sun hau jikina,dankwalin dana kafa kamar gogoro ya zame ya jefa shi saman Bed ya dauki Hijab ya sa min duk da haka nayi kyau sosai sai ya cire Hijab din ma tare da cewa baki da kyau sam
End Ads