ba,Itama Mommyn Mujaheed sai da ta mallaki katon gida da Gold ubanka Mujaheed yaje ya lallabata amma ta hanashi sai ko Hajja ta hadata da malamai sai gashi ta dauki komai Nata na dukiya ta basu tun kuna yara,ana zuwa wurin Umman Ameer ta fashe da kuka tace ai wlh tunda har suka iya korar min dana daga gida bazan koma ba,Aayan da Mufeeda Allah yayi musu albarka sune suka rike min shi da tuni ko ya fada shaye shaye amma gashi yana wajensu lfy shi yasa nace yaci gaba da Zama a can,ai zalincin dasu Hajja tare da Yayanta suka yi mana bazai irgu ba,ni dai na gane gaskiya tsakanina dasu sai Allah ya isa,Haka nazo da Kudina Dubu Dari Babana ya bani Naja jari na fara business ina Amarya Abbi uban muguyen gidan kaf ya lallabani yace na kawo na shiga Dashi,sai da na shiga Ashe tuni ya lallaba da daukana yazo ya karbe kudin sai da nace a bani uwar dashi tace wai nice daukan farko mijina ya karba yace nice nace a bani,naji takaicin Abin nan haka na dinga zubin dashi ba dauka har aka gama,bayan nan Babana ya kara aiko min da Dubu Hamsim ya lallaba ya sace,banda sauran abubuwa wanda muka sani da wanda bamu sani ba na zalinci da suka dinga gwada mana wanda Hajja ke sasu komai.
Mujaheed yace to a bamu yaran mu tafi dasu sabo da schl,haka aka basu su Omar su uku yara yan 5-6yrs suka tafi dasu sabo da schl kar su tashi ba ilmi me kyau.
Su Abbi kuwa basu da mataye yanzu sai dai suci su sha su sa sutura me kyau,gasu gwauraye illarsu daya rashin kudi babu kudin da za ayi bariki amma duk da Haka Suna yi sama sama neman mata tunda Suna matsawa dole Ameer yana basu kudi,haka su Khaleel suna Jin tausayinsu su basu Ashe ana basu sai su Kama Hotel su kai mace ciki musamman Abbi Sani yafi kwarewa a wannan fagen.
Haneefa ce ta shigo main Palo taci uban wanka ta Sha kyau sai masifa take,Sabeer takewa fada wlh duk me wulakanta abinci watarana abinci sai ya wulakantashi,ba ku kadai abin bala'in zai shafa ba har mu gaba daya,taya dan Iskanci baza ayi abinci dai dai kowa yaci baiyi kadan ba baiyi yawa ba amma sai kuje kusa ayi ta dafa abincin iri iri kuma a kasa cinyewa,a zubar dashi ko ina kaca kaca daga karshe a watsa a dustbin ga masu aiki kuna sasu wahala,wannan ba dai dai bane,kalli yanda muka Sha wahalar rayuwa amma ko tunawa bakwa yi,wannan bai dace ba babu kyau,Allahu Akbar yaran suka saki kabbara gaba daya Haneefa ta Zama Malama,su Kansu masu aikin gidan yanzu dadi suke ji yaran gida sun nutsu, Hajja ce kawai dasu Abbi ba a shirin tuba sunyi nisa, Haneefa tana gama wa'azinta,Sajeeda ta Mike tace ya kamata mu nemo mazaje,Maza su nemo mataye muyi aure sai ihu yeeeeeee wlh kuwa gwara a dama damu,Sajeeda kinfi kowa iya kawo shawara Cewar Khaleel, Abbi ne ya fito ya daka musu tsawa baku da aiki sai kullum ku cika mana kunne da surutu da ihun banza,zaraf sai ga Hajja tace aikinsu kenan yanzu kullum sai sunyi zaman Palo suna surutun banza da wofi wai su yanzu a dole sun Zama na gari nan wai nutsatsu,Sai kunci ubanku wlh a gidan nan sai na tattaka ku cewar Abbi,Hajja tace gwara haka ai wanda basu San ciwon Kansu ba kwandala bana morarsu gasu nan dasu gwara babu a gidan nan,ni fa takaici nakeyi Ameer baya gidan nan nasan shi kadai ne dan albarka kullum sai ya bani kudi ya siyo min kayan dadi,Abbi yace ai nace masa ya dawo mu zauna yaki yarda wai yafi son wajen yaron can me Jan kunne,ai idan Ameer ya sake sai na masa baki watarana,da Sauri Hajja tace baka isa ba Ameer dan albarka ai duk yafi wannan banzayen,Ameer dina wlh duk Wanda ya ko zageshi bazan yafe muku ba a gidan nan,da dinma da na bari kuka koreshi nayi ne dan ya gyara halinsa badan wai bana sonsa ba. Tabe Baki Khaleel yayi yace mu da kice kina sonmu da ki tsane mu duk daya a wajenmu,kai marar kunya kaji nayi magana da kai shegen Hanci kamar kana Mura kai fa Hasken fatarka na banza ne sabo da bame kyau bane shegiyar Suma kamar ta zabiya,Ameer ne kamar Balarabe,Wannan kuwa ta Nuna Mujaheed ido kamar na dan giya manya dasu,dariya sukayi Sabo da Khaleel Hasken sa da yawa, Mujaheed ma yana da haske amma yafi kowa Dara daran idanu sune ma suke kara masa kyau,duk da Dama su duk gidan kyawawane sosai,Aayan ne yafi kowa ba a hada kafa dashi sabo da shi jinin turawa ne sai Ameer, Hajja ta Gama masifarta ta wuce.
Su Aayan da dare sunje gidan me magani yace sai sunyi sati daya a wajensa,suna dawowa Aayan ya bani lbr kawai na taho gobe,Ammah kuma ta kara Min warning kar na sake na zo taji labarin Aayan yace zan biyosu,Na roki Ammah ta yarda nazo tace bazan zo ba,Aayan na sanarwa yace tunda Ammah ce shike nan mu hakura haka har mu dawo,kullum tare muke dasu Ma'eesha tare muke girki da komai da ya dace muna zuwa schl dinmu ni da Ma'eesha abinmu lfy, kwanan su Aayan Uku alhmdllh Daddy yana samun sauki domin har yana iya motsa hannayensa da kafafu.
Muna zaune tare dasu Ma'eesha,Ameer yana Shan Ice Cream dinsa,Meenat tana kusa da Ameer wai sai ya San mata Ice cream dinsa bayan ta shanye nata, wayata tayi kara naga Kawata Nawwara ce rabon da ta kirani tun ranar da tazo su Haneefa suka kwala mata robar ruwa tace Bom ne sai yau naga kiranta bayan ta tafi na kirata amma taki dagawa,ina dagawa nace kin huce kenan?dariya tayi muka gaisa tace Anjima zan shigo Insha'allah,Nace to bari na tura miki address din mun canja gida ba wanda kika sani ba,da sauri tace da gaske?yanzu ba gida daya kuke da yan iskan nan ba?nace ae ya canja min gida,to Alhmdllh gani nan zuwa anjima,misalin 5pm sai ga Nawwara ta rafka Sallama,muka amsa yau ma tayi kwalliyarta,muna ta hira ta gaji sai naji tace ina mijinki?nace yayi tafiya,nan take naga ta bata fuska,nace lfy? Dariyar yake tayi lfy alhmdllh kawai tambaya nayi,bari naga gidan naku gaskiya kinyi dace Hajjaju wannan uban gida haka haduwa,Su Ameer suna jinta tana ta zuba surutu,bari na shiga garden nasha kallo,nace bari na nuna miki,a'a jeki ki dafa min me dadi ni zanje da kaina kawai ba sai kin biyo ni ba,Mamaki ya kamani ni da gidana mace ta nuna ta fini saninsa zuwanta na farko kuma,Jeki to kawai na shiga kitchen na kyaleta,Maeesha suna kallonta suna jinta ta fice abinta ta gama Shan kallonta tana zagaye,Ameer daga baya yabi bayanta amma yana fita yaga kallo takeyi tana Selfie abinta tana tsinkar su Guava a lambu sai ya kyaleta ya dawo,ita kuma Meenat sai aka fara fushi dan me Ameer zai bi bayanta,bayan Nawwara ta gama kallonta sai ta dawo taci abincinta muna hira ta gama sa idonta ta Mike tace zata tafi,na rakata har gate na dawo.
Sameera yar daba da yaranta su har yau suna can a kulle basu samu damar fitowa ba,iya cin hancinta ta bayar ta hakura tana gidan kaso ana fafatawa da ita ko a prison Sameera tana cikin shegun matan da suka gagara.
Bayan sati Muna waya da Aayan yace kinji wai sai mun kara sati daya zamu dawo,ni kaina banji dadi ba na matsu Mijina ya dawo,nace amma na kira Daddy a waya fa yace min yana takawa,ae Malamin ne yace wai sai ya karasa mikewa da Saura,ajiyar zuciya na ja nace to ba damuwa Allah ya nuna mana,baki damu dani ba Babyna ko naga ko a jikinki ni ina nan cikin wahalar rashinki,nima na marairaicewa haba Mana karfin Hali da dauriya kawai nakeyi Allah amma bari na kira Ammah idan ta yarda gobe zanzo,da sauri yace yawwa yar albarka tambayeta muji,ina kashe wayar na Kira Ammah,ita kanta ganin Aayan har yar rama yayi yasa tace kizo goben to,Murna kamar me amma dan kar na fadawa Aayan ya sa rai yasa nayi masa shuru nace Ammah bata yarda ba,washe gari cike da zumudi nayi Shiri na barwa Su Meenat komai nasa Driver ya tafi dani Kauyen,Munje lfy kauyen Driver na ajiyeni nace ya juya ya koma,na dauki jakata sai kallona akeyi anga yar gayu ga kyau na shiga gidan Yar Uwar Ammah wato Inna tsohuwa,Ammah ta kalleni tana dama fura tace ai nasan sai kinzo dole,dariya nayi na rungumeta Ina gaisar da Inna tsohuwa,Mufeeda sai yau za azo mana ana can ana cin Amarci wlh kinyi dacen miji yaron kirki sai yabonsa akeyi a garin nan,Inna ai da gani kin San ya iya kiwo ma yanda na koma kalli fa,Dariya mukeyi da Inna tace ai naji kin cika mana gida da kamshi,yana ina ma Wai Inna?Ammah ce ta zuba min duka a baya baki da kunya Mufeeda yaushe kika dawo haka?dariya nayi tare da mikewa na kai jakata dakin Inna nayi Alwala tare da sallah,sai Ammah tace ga ruwa can kije kiyi wanka,Haka na fito nayi wanka da sauri na shafa lotion na sake kaya Atamfa me tsadar gaske Black and Green nayi kyau riga da skert kamar a sace ni,turare na fesa na fito sai mukayi ido biyu da Aayan wanda shugowarsu kenan tare da Yarima,Har zanje na fada jikinsa na tuna su Ammah na wajen,sai kawai na gaida Yarima tare da Aayan,Yarima yace au saida kika biyoshi kenan ko?daki na koma da Sauri sai ko Aayan ya biyo bayana, na juya baya ina murnar ganin mijina sai jinsa nayi ya rungumeni ta baya yana sakar min kiss a wuya ta ko ina,Ajiyar zuciya kawai muke saki,Kamar zai cinyeni haka yake tura kansa ko ina a jikina, yatsu na ya kamo yana kallon yanda nasha zanen lalle ba karamin kyau nayi ba,Dankwali na ya zame yana shafa gashina yana kissing dinsa,kallona yake kamar ya hadiyeni yace kinga kyan da kika kara kuwa?Ni ina nan tunaninki ya hanani sakewa,Bana iya bacci sosai fa,Murmushi nayi ai gani nazo to,amma baki fada min yau zaki zo ba Ashe Ammah ta yarda kizo,Ido na lumshe masa nace zo muje makwaftan Inna wata Tsohuwa ce tukuf sai tsaftar Masifa tana mugun so na ita kadai ce a gidan Masauki me kyau zata bamu a gidanta sai muna kwana a can tare,Ina Daddy fa? Daddy ya Zama dan gari har yana fita majalisa a kauyen nan,yanzu ma yana cikin dattijai can wata bishiya suna hira,Murna Nayi tare da Hamdala,Muryar Ammah naji tace ga abincinku Mufeeda,Yarima yana zaune kusa da Ammah suna ciye ciyensu,Abincin na fita na dakko a tire Fura lafiyayya da kuma Shinkafa da miya da salat,da yake Ammah na nan girki me dadi take shirya musu iri iri ba kamar farkon zuwansu ba da Aayan ke korafi ba dadi,shi yasa Ammah take musu komai da kanta.
A jakata na dauko Soyayyan Nama na zuba mana saman abinci,na kaiwa su Ammah nasu sai Dariyar Kwadayina Aayan ke yi,yace to ai ga nama nan a abincin amma sai kin kara wani,Nace ai wannan suyar tasha maggi,dariya ya shiga yi yace sarkin kwadayi yau zamuyi bacci tare gobe bazan tashi da wuri ba sai tsakar rana,Murmushi nayi masa me matukar kyau,Yau da kaina na bashi abinci har ya koshi ina lallabashi yana ta shagwabarsa,5pm yace bari nayi wanka muje gidan tsohuwar taki daga nan muje yawo,Ruwa na hada masa na kai masa har Toilet,Ammah tana ta jin dadi yanda taga ina kula da mijina gwanin sha'awa,ina kusa da Toilet din ya dinga min magana kasa kasa wai shugo ki min wankan,nace Ammah zasu kama mu yana gama wankan ya koma dakin da suke kwana ya shirya cikin 3qtr da yar riga fara yayi kyau,Na yafa mayafi na da Handbag na bishi muka fita,shi kuwa Yarima Bacci kawai bacci yace zaiyi ya gaji,Hannuna cikin nasa iska na kadawa muna tafiya cike da nishadi tare da jin dadi,sai da muka dan zaga a garin ko ina sai kallonmu akeyi Yace ana kallona shi mu tafi gida,Gidan tsohuwa Iya Makwafta da gidan Inna muka ya da zango,daki ma sai da na zabar mana,ya kasa hakuri dare yayi muje tun da yamma ya takura yana rokona Na bashi ko dan Kucili ne,Iya muka yiwa wayo wai bacci zamuyi Jiki na rawa ya fara sarrafa ni,Nima haka,yana kukan da karfi na toshe masa baki Iya zata gane mu fa,yace ke wannan Sirri ne Allah yana sawa abin Hijab,kin taba ji an kure mata da miji?sai dai a kure kwarto na bashi Amsa muna dariya,Iya muka ji tace ba kyau baccin bayan la'asar ki fito da dare sai kuyi,Nace Iya ba bacci mukeyi ba Wasu yakardu muke dubawa na sirri,Iya tace yawwa yan Albarka a barwa dare sai ayi baccin haka da kin fito ma kin tayani yanka Kubewa,Nace Da Karfi Iya bazan iya aiki ba yau na....Aayan yasa bakinsa cikin nawa Iya taji muryata ta wani shake tace yau ko yar Hirar ma baza kizo muyi ba kin kule daki da mijinki,Iya taji Shuru dadi ya tafi dani ko jinta bana yi tana ta Surutu ba wanda ya kula ta dama ga Iya da surutu bata iya shuru da bakinta,Yau kam Alhmdllh mun gwangwaje juna,munji dadinmu abin ba a cewa komai yau naji dadin da ban taba ji ba,Cike da nishadi yace to wankan ne matsalar,nace sai yanzu ka tuna Gashi har Magrib ta wuce,Fita nayi wajen Iya nace Iya za a samu Ruwan Zafi kafarsa na ciwo zai gasata,Iya ta gane amma sai tace gashi can na dora har ya tafasa cikin katuwar tukunya zai isheku gaba daya,shuru nayi Iya kuma ta wuce dakinta tare da cewa in kin gama abincinku yana kitchen,nace to Iya,Ruwa na hada mana tare muka yi wanka sannan muka tsarkake jikinmu, mun dan ci abincin Iya sannan nace zamuje mu dawo,Gidan Inna muka koma,Ammah tace ina kuka shiga haka?Nace muna gidan Iya,Yarima kuwa tun daga kallon da yakewa Aayan suna dariya yasan me muka je yi,Daddy yana dakinsa masauki tare da Aayan Mukaje na gaisheshi da murna ganin ya dawo lafiyayye,ina ta murna ina masa sannu,Daddy yanzu yawo ko ina,yace Alhmdllh Mufeeda Ashe kema kinzo cike da kunya nace ae Daddy.
Daddy yace Alhmdllh kafin Mu bar garin nan Iyayen Yarima zasu zo tare da dangin mahaifinku za ayi maganar auren Ma'eesha,tunda sun shirya Kansu sai kawai a tsayar da ranar biki,nace Alhmdllh tunda Ammah ta yarda ai ba damuwa,Aayan kuma yayi min zancen Meenat da Ameer ina so na wakilci abin ina tunanin Abbi Baban Ameer da kyar in zasu yarda musamman Hajja,amma idan mun koma gida zan tuntubesu da kaina naji.dadi naji nace to Daddy Allah taimaka,mun dan jima muna hira sannan muka fito.
Bayan kwana biyar Saura kwana biyu mu dawo gida dangin Abbanmu suka zo tare da iyayen Yarima nan aka bada kudin Aure aka sanya rana nan da 4Months,Daddy yace ya wakilci Ameer ai shima Ubansa ne idan mun dawo zai san yanda zaiyi dasu tare da Hajja har su yarda,Nan ba tare da Sanin Ameer da Meenat ba aka sa Rana suma Daddy ya bada kudin auren da komai,Sannan yace kar wanda ya fadawa Meenat da Ameer kawai ace na Ma'eesha da Yarima kawai za ayi.
Ana gama komai suka tafi cikin aminci,muma ranar tafiyarmu na zuwa Driver yazo da katuwar Mota muka musu sallama cike da kewar juna,Sunsha kyauta wurin Daddy musamman Malamin da yayiwa Daddy magani.
Mum dawo da kwana biyu Daddy yaje gida wajen Hajja kowa yasha Mamaki ganin Daddy ras dashi ya shigo da kafafunsa,Yaran gida Su Haneefa murna kawai sukeyi suna kwasar gaisuwa ana masa Congrat,Hajja ma taji dadi danta ya dawo fes,Su Abbi ne ko a jikinsu basu damu ba,an gaisa sunyi Hira,Daddy daga shi sai Su Abbi da Hajja yace Idan baza ku damu ba naga Ameer yana son kanwar matar Aayan suna son juna da sai ayi musu aure,kaga sai a hada ma dana su Khaleel su Ukun,Dafe Kirji Hajja tayi tace Ameer dinne yace yana sonta?Daddy yace ae har Kuka yake min kullum,Hajja dama tana son Ameer a rayuwarta nan tace bana son Matar da zai aura bana kaunar danginsu Amma da ace Ameer yana kuka a kanta gwara a aura masa ita,da Ameer dina ya zauna cikin damuwa gwara ko ma wace a bashi ita,ina Ameer din a nemo min shi karfa ace yana can cikin bakin ciki,Daddy yace ki kwantar da hankalinki Hajja,Abbi yayi tsalle ya dire ba wanda ya isa ya aurawa Dansa dangin Mufeeda dangin jaraba.
Hajja tace wlh baka isa ba ni kaina bana kaunarsu Amma akan Ameer ya shiga damuwa gwara a aura masa ita,tunda Ameer yana so na yarda ko wace ce a bashi farin cikinsa,Abbi zaiyi Magana Hajja tace kana kara magana ban yafe ma ba,kuma duk Wanda yaki yarda ayiwa Ameer dina Aure da wacce yake so ban yafe masa ba duniya da lahira.
Abbi yayi shuru yana Hararar Daddy yace ai sai kaje kuyi komai kuma kwandalata babu a ciki,Daddy yace ai gaba daya yaran nan kowa mata da Maza ko ba raina Aayan zai musu komai.kafin Daddy ya tafi sai da ya bawa Kowa na gidan kyautar makudan kudade musamman Hajja dasu Abbi,Su Mujaheed ranar sunsha Gori da zagi wajen Hajja tayi Kudi.