x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 23 - MAZAN JIYA 4

  • 66001 words
  • 68055 words
  • Out of 68055 words

Category: Adventure Stories

Views 187

18 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
junansu. Shalbirat ta
dubeta ta ce nice gimbiya shalbirat yar
danuwanki, sarkin da kika kashe kika hau kargar
mulkinsa, sannan kika sa aljani Raugatul
Agwanu ya sace ni ya tafi dank can dajin darul
hushushul maut, ka rabani da uwata da ubana
tsawon shekara goma sha tara. Koda jin
wannan batu sai sarauniya Juzairat ta dada cika
da tsananin mamaki ta kura wa shalbirat idanu,
alokacin da ta dada kamuwa da tsoro jikinta da
baikinta suka hau rawa ta kasa cewa komai.
Shalbirat ta sake dubanta a karo na biyu ta ce ni
yanzu nazo maki da addinin gaskiya wato
addinin Musulunci, kuma na baki zafi ki karbi
388

TASKARNOVELS.COM.NG
addinin Allah ki tsira da rayuwarki, sannan ki
sauka daga kan matsayin da kike a yanzu ki
dawo talaka kamar kowa ko kuma yanzu ki rasa
rayuwarki? Koda jin Wannan batu sai sarauniya
Juzairat ta bushe da dariyar keta ta ce tsakanina
da addinin musulunci sai gaba.. Kafin ta gama
rufe bakinta gimbiya Shalbirat ta juyo cikin
tsananin zafin nama ta zare takobin jarumi
Hasnalu ta kuma juyawa ta fille kan Sarauniya
Juzairat, nan take jini yayi tsiri sama yayin da
kan nata ya gangaro daga kan karagar mulki.
Nan take Shalbirat ta kwala kabbara kuma ta
karanta kalmar shahada ta na mai umartar
gabadaya mutanen dake fadar da su biya
kalmar. Ba tare da wata gardama ba gabadaya
mutanen fadar suka maimaita kalmar shahada,
cikin tsananin farin ciki gimbiya Shalbirat ta hau
kan karagar mulki ta zauna alokacin da su
jarumi Hasnalu suka cika da tsananin mamakin
wannan gagarumar jarumtaka da ta yi. Zaman
Shalbirat akan karagar mulki sai idanunta suka
ciko da kwalla, har hawaye ya zubo mata a
lokacin data gama kare wa karagar mulki da
kuma fadar kallo. A sannan ne ta dubi wani
dattijo a fadar ta ce ya kai waziri Lamsanu mene
389

TASKARNOVELS.COM.NG
ne labarin mahaifiyata? Cikin tsananin mamaki
waziri Lamsanu ya dubi gimbiya Shalbirat ya ce
rankiya dade qshe ba zaki manta da kamannina
ba, kiyi sani cewa mahaifiyarki ta samu tabin
hankali, kuma tana can a tsare a kurkuku. Koda
jin haka sai bakin ciki ya turnuke Shalbirat har
hawaye ya sake zubo mata ta mike ta ce muje
ka kaini inda take. Nan take Waziri Lamsanu ya
wuce gaba Shalbirat dasu jarumi Hasnalu na
take mashi baya, haka suka yita tafiya a gidan
sarautar suna masu shiga lungu da sako na
gidan sarautar har sai da suka iso inda
kurkukun yake, aka kai su kofar dakin da
mahaifiyar Shalbirat take. Da zuwa sai suka
isketa a kwance tana bacci, gashin kanta yayi
buzu-buzu ba kyan gani, ga kuma furfura duk ta
rufeshi Hakazalika rigar jikinta ta yi dauda sosai
har tana wari. Su duka dai da suka zibar da
hawaye saboda tausayi, Shalbirat ta kira sunan
mahaifiyar tata har sau uku sannan ta taso
zaune tana mai kura wa Shalbirat idanu, kawai
sai ta bushe da dariya ta kama surutu irn na
masu tabin hankali tana mai kawo wa Shalbirat
duka. Koda ganin haka sai jarumi Hasnalu ya yi
sauri ya matsar da Shalbirat baya sannan ya
390

TASKARNOVELS.COM.NG
shiga karanta wata addu'a yana tofawa
mahaifiyar Shalbirat, aiko nan take wani
nannauyan bacci ya dauketa, jim kadan ta farko
tana mai tashi tsaye da kafafunta tana mai
binsu da idanu daya bayan daya, koda idanunta
suka yi arba da yarta Shalbirat sai ta kura mata
idanu har hawaye ya zubo mata, ta nuna
Shalbirat da hannu kuma ta kira sunanta tana
mai cewa Yata ashe kina raye a wannan duniya,
ashe zamu sake saduwa? Koda jin wannan
batu sai mamaki ya kama su Jarumi Hasnalu
suka yi kabbara a tare, nan take Shalbirat tasa
aka bude kofar dakin da mahaifiyarta ke ciki ta
ruga da gudu suka rungume juna ita da
mahaifiyarta tata suka fashe da sabon kukan
farin ciki. Suma su Imnal basu san sa'ad da
kukan ya kwace masu ba, saboda tausayi gami
da murna, a wannan rana aka kaddamar da
addinin musulunci a Birnin, gimbiya Shalbirat
kuma ta hau kan karagar mulki. Lokacin dasu
jarumi Hasnalu suka je yi mata bankwana sai ta
fashe da kuka, ta dubi Sadusa da dansa Halyal
ta ce kune farkon sanadin tsirata daga hannun
azzalumi aljani Raugatul Agwanu, bani da bakin
yi maku godiya face addu'ar Allah ya saka maku
391

TASKARNOVELS.COM.NG
da mafificin alheri. Ba tare da bata lokaci ba su
Hasnalu suka yi mata sallama suka tafi, ana isa
birnin sarki Dujalu nan ma aka kaddamar da
addinin musulunci amman gimbiya Hursiyya
bata karbi sarauta b sai aka ba Sadusa. Waziri
da jama'arsa kuwa suka bashi hadin kai. A
sannan ne aka shiga dakin tarihi na gidan
sarautar inda aka gano wannan littafin mai
dauke da tarihin kamannin mahaifin Hasnalu da
kuma inda kabarinsa yake, nan take aka
dunguma aka tafi wajen, koda aka tona saman
kabarin sai aka yi arba da fuskar mahaifin
Hasnalu lafiyarta sumul ko kwarzanewa bata yi
ba, kamar ma asannan ne aka binne shi, kuma
kamanninsu iri daya ne sak da jarumi Hasnalu
tamkar an tsaga kara, bambancinsu kawai na
shekaru ne. Koda jama'a sukaga wannan gawa
cikin koshin lafiya alhalin ta kusa shekaru
talatin a binne sai suka cika da al'ajabi aka
kama hailala da kabbara, aka kuma sallama Wa
Allah bisa ikonSa. Hasnalu ya kura wa
mahaifinsa idanu yana mai zubda hawaye ya ce
ya kai abbana ban taba ganinka ba sai labarinka
da mahaifiyata ta bani, rayuwarka gaba daya ta
gushe a cikin yada Addinin Allah, yau gashi
392

TASKARNOVELS.COM.NG
Allah ya cika mani burina naga fuskarka da
idanuna kafin mutuwata. Burina ya cika, fatana
nima Allah ya dau raina a irin wannan tafarki
naka, nan take ya mayar da kasar kabarin ya
rufe sannan yayi masa addu'a. Kamar yadda
aka kaddamar da addinin musulunci a birnin
Sarauniya Shalbirat da birnin sarki Dujalu haka
akaje birnin sarki Maharaz aka kaddamar da shi,
kuma duk d cewa jarumi Imnal da gimbiya
Mulaifa sun kasance yara a sannan aka daura
masu aure, akayi gagarumin shagalin biki a
gaban jarumi Hasnalu da gimbiya Hursiyya.
Lokacin da Hasnalu da gimbiya Hursiyya suka
zo zasu yi wa su Imnal da sarki Maharaz
bankwana domin su tafi izuwa can nahiyar su
jarumi Hasnalu inda acan ne Hursiyya zata
karasa sauran rayuwarta ta duniya sai su duka
suka kama kuka saboda bakin cikin rabuwa da
juna, sarki Maharaz ya rungume jarumi Hasnalu
yana mai cewa ya kai jarumin jarumai, kaine ka
tsamoni daga cikin duhun jahilci ka haskake
mana wannan nahiya gaba daya da hasken
musulunci, hasken ilimi kuma haske na
gaskiya, tabbas har abada ba zamu taba
mantawa da kai ba, kuma har mu mutu zamu
393

TASKARNOVELS.COM.NG
rinka tunawa da kai muna alfahari da kai, idan
ka amince ina so tun gabanin ku barmu a daura
aurenka da gimbiya Hursiyya a gaban idanunmu
domin mu zama sheda kuma ku tsira daga
dukkanin wani tsautsayi na sharrin shedan
dana zuciya, tunda zaku kadaita a cikin wannan
doguwar tafiya da zaku yi izuwa nahiyarku.
Koda sarki Maharaz yazo nan a zancensa sai
jarumi Hasnalu yaji matukar farin ciki, kuma ya
kama yin godiya ga sarki Maharaz bisa hango
masu abinda zai fiye masu alheri. Nan take aka
daura auren jarumi Hasnalu da gimbiya
Hursiyya bisa ka'idar addinin Musulunci, bayan
nan sai suka yi bankwana su sarki Maharaz
suna zubar da hawaye suma suna zubarwa, har
jarumi Hasnalu da Hursiyya sun juya zasu tafi
sai kawai sarki Maharaz ya kira sunan Hursiyya
ta juyo ta dubeshi ya ce da ita ya ke yata in da
tambaya a gareki? Tambaya ta farko ita ce
wane irin darasi kika samu a cikin hikayar
jarumi shaddadu, kuma wane ilimi kika gani a
cikin tamu rayuwar ni da fan uwanki sarki
Dujalu? Koda jin wadannan tambayoyi sai
hawaye ya zubo daga cikin idanun Hursiyya
domin babu wanda ya taba mata irin wannan
394

TASKARNOVELS.COM.NG
tambaya face sarki Dujalu. Hursiyya ta yi ajiyar
numfashi sannan ta ce ya kai abbana ka sani
cewa a cikin hikayar jarumi shaddadu na
fahimci cewar zalunci da son zuciya basa haifar
da komai face nadama da kaskanci gami da
dunbin wahala kamar yadda karshen rayuwar
sarki Laffaru ta kasance, tunda a farkon
rayuwarsa karfin mulki, dana jarumtarsa hadi
da na sihiri sun sa masa isgilanci har yana cin
zalin al'umma, ganin cewa babu wani da ya isa
ya taka masa birki, amma sai gashi ya mace ta
rabashi da mulkinsa, karfinsa da duk
daukakarsa, kuma ta jefashi a cikin tsananin
wuya da rashin kwanciyar hankali har izuwa
karshen rayuwarsa. Darasi na biyu a cikin
wannan labari shine abu ne mara kyau mutum
ya tsananta gaba a tsakaninsa da wani, kamar
yadda Sharlis da Laffaru suka tsananta gaba a
tsakaninsu har ga yayansu, wanda sai ga shi a
karshe yayan nasu sun kamu da son juna kuma
suka zabi su mutu tare dan kawo karshen gabar
iyayen nasu, abinda ya cusa wa iyayen bakin
ciki kenan suka kashe kansu, suka rasa komai
ba tare da burin dayansu ya cika ba. Dangane
da ilimin dana samu game da rayuwar dan
395

TASKARNOVELS.COM.NG
uwana Dujalu da taka rayuwar shine na fahimci
cewar wanda duk bai gode Wa Allah ba bisa
baiwar da yayi masa ta arziki da daukaka, har
yake harin ya samu wadda tafi wannan to
karshensa nadama gami da hasara, tunda gashi
kai da shi duk kunyi mummunar asara ta dukiya
da rayukan jama'a kuma burinku bai cika ba,
haka kuma na samu babban ilimi na kadaita
Allah, ikonsa da isarSa akan komai da kowa,
tunda gashi matsafa da aljanu sun kasa dauko
kayan yakin mazan jiya a cikin tekun bahar
Suffiya, amman sai gashi wanda yayi imani da
Allah ya kadaitashi ya dauko su salim alin,
kamar yadda ake cire silin gashi daga cikin
tandun mai, hakika ubangijin musulunci shine
buwayi gagara misali, wanda duk yayi imani da
shi ya kubuta kuma ya tsira daga dukkanin
sharri, wanda kuma ya bujire masa ya hadu da
masifa da halaka. Koda Hursiyya ta zo nan a
jawabinta sai sarki Maharaz ya cika da tsananin
murna gami da farin ciki, yace AlhamduLillahi
tabbas kin samu duk irin darasin daya kamata ki
samu a cikin wadannan labarai, albishir din da
zanyi maki shine kije ki nemi wani littafi mai
suna Tsatsuba tabbas zakiji labarin Sadauki
396

TASKARNOVELS.COM.NG
Hulkas na birnin Romaniya a cikinsa tunda dai
dan uwanki sarki dujalu bai samu damar baki
labarin ba ajali ya riskeshi. Koda jin haka sai
farin ciki ya lullube gimbiya Hursiyya ta ce aiko
in sha Allah duk inda Littafin Tsatsuba yake zan
nemeshi domin na karanta tarihin Sadauki
Hulkas mai hular lamsara n birnin Romaniya.
Nan take Jarumi Hasnalu da gimbiya Hursiyya
suka sake yi wa sarki Maharaz sallama suka tafi
suna masu waigensa har suka fice daga fadar
tasa, gabadaya suka nausa izuwa cikin daji
suna masu falfalawa da azababben gudu, cikin
yarda da huwacewa ta Allah suka nufi nahiyar
su jarumi Hasnalu inda zasu cigaba da rayuwa
bisa tafarkin addinin Muslunci.
AlhamduLillahi nanne karshen wannan littafi na
mazan jiya da fatan kunji dadin wannan littafi
wanda Abdulaziz Sani madakin gini ya rubuta ni
kuma Abubakar Saleh Alquyraemey na
jagoranci typing insa nake cewa mu hadu da ku
a wani littafin.

397


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels
End Ads