x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 23 - MAZAN JIYA 3

  • 66001 words
  • 68212 words
  • Out of 68212 words

Category: Adventure Stories

Views 190

18 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
yi wani abin da bai dace
ba.

Daga wannan rana Sharlisa ta ci gaba da koya
wa Shaddad yaki dare da rana ya zamana cewa
jarumtakarsa kullum karuwa take yi.

477

TASKARNOVELS.COM.NG
Wani lokacin tausayinsa ne yake kama ta idan ta
ga irin bakar wahalar da yake sha wajen karɓar
horon yaki, har ma ya kan suma sai dai Sharlis
ta ji kwallah ta zo mata saboda tsananin
tausayinsa amma duk da haka ba ta daina ba shi
horon ba.

Ba komai ne yasa Sharlisa take bai wa Shaddad
wannan horo mai tsanani ba face saboda ta yi
bincike ta gano cewa Sarki Laffaru ya auri
Gimbiya Ramlatul Siyam kuma suna nan a cikin
wani daji suna zaman rayuwar aure. Babu
yadda Sharlisa ba ta yi ba domin ta shiga dajin
Rauful Mausur amma abu ya gagara. Sau goma
sha daya tana yin gagarumin shiri ta je har
bakin dajin domin ta shiga amma sai ta kasa,
bisa dole ta hakura ta koma da baya.

A cikin binciken da ta yi ne ta ga cewa lallai
Sarki Laffaru da Gimbiya Ramlatul Siyam za su
haifi 'ya mace kyakkyawar da babu kamarta a
duk duniya, kuma za ta taso da gagarumar
jarumtaka irin wacce babu wani jarumi mai
irinta.
478

TASKARNOVELS.COM.NG

Babu wanda zai iya tararta da fada ko yaki face
danta Shaddadu. Shi kansa Shaddadun ba zai iya
hallaka ta ba face yai amfani da mashin Galilul
Haras.

Lokacin da ta daďa zurfafawa a cikin binciken
nata ne, sai ta gano cewa babban abin da zai
janyo rashin nasarar Shaddadu akan 'yar Sarki
Laffaru shi ne SOYAYYA.

Ko shakka babu in dai ya yi arba da 'yar Sarki
Laffaru sai ya kamu da tsananin sonta, in kuwa
ya kamu da tsananin sonta ba zai iya kashe ta
ba.

Koda Sharlisa ta gano wannan al'amari sai ta
rinka cusawa Shaddad kiyayyar mata a
zuciyarsa, ta rinka nuna masa cewa sharrin
mata ya fi na bakin kumurci.

479

TASKARNOVELS.COM.NG
A haka Shaddad ya taso da tsananin kiyayyar
mata, ya zamana cewa ya tsane su ainun komai
kyan mace ba ta birge shi.

Kai hatta sha'awa ma irin wacce kowanne da
namiji ke yi wa mace sai da Sharlis ta cire wa
Shaddad ita da karfin sihiri, a matsayin ba za ta
dawo masa da sha'awar ba sai bayan ya kashe
'yar da Laffaru ya haifa sannan ya kamo
Laffarun ye kawo mata shi sun gana masa
muguwar azaba tsawon kwanaki sannan su yi
masa kisan gilla.

A kwana a tashi, sai jarumi Shaddad ya cika
shekaru ashirin da daya a duniya. A sannan ne
kirar jikinsa ta ginu sosai, kai da ganinsa ka ga
gawurtaccen jarumi saboda murdewar da jikin
nasa ya yi da kuma tarin kwanji da jijiyoyi.

Ga shi Allah Ya yi masa tsananin kyan fuska da
kyan surar jiki. Karfin dantsensa kuwa ya wuce
a misalta saboda komai girman bishiya idan ya
480

TASKARNOVELS.COM.NG
naushe ta da hannu daya take ta ke tunɓukowa
daga cikin kasa ta fadi kasa.

Kuma komai yawan mayaka shi kadai yana iya
tarwatsa su ya kashe na kashewa, masu sauran
kwana su gudu. Idan kuwa yana yaki zai iya
kwana da yini bai gaji ba

A ranar da Shaddad ya cika shekara shirin da
daya ne, Sharlis ta kimtsa shi ta damka masa
mashin Galilul Haras sannan ta gargade shi akan
kada ya yi amfani da mashin face ya gamu da
'yar Sarki Laffaru.

Koda jin haka sai Shaddadu ya dubi
mahaifiyarsa Sharlis cikin tsananin damuwa ya
ce, 'Ya ke Ummina yanzu ya za a yi na gane
wannan babbar mikiya tawa alhalin ban santa
ba, kuma ban taɓa ganin irin fuskarta ba?

481

TASKARNOVELS.COM.NG
Ke da kanki ma kin yi iya bincike a cikin tsafi
domin ki ga fuskarta amma abu ya gagara
saboda tana cikin dajin da ba a iya ganin komai".

Sa'adda Shaddadu ya zo nan a zancensa sai
Sharlis tayi ajiyar zuciya har kwalla ta zo ma ta a
cikin idanunta, sannan ta yi murmushi ta ce,
"Kada ka damu ya kai dana, yanzu-yanzu zan ba
ka wata layar tsafi. Duk Macen da ka hadu da ita
in dai ka ga tana da jarumtaka gami da tsananin
kyau da zarar ka kara layar a jikinta za ka ga
layar ta sauya launi daga baka zuwa ja jawur.
Kana ganin haka ka yake ta da mashin Galilul
Haras ka hallaka ta.

A jikin wata sarka da ke wuyanta za ka ga hoton
dajin da mahaifinta yake. Ka cire sarkar ka tafi
da ita har can inda mahaifin nata yake ka kamo
shi ka kawo shi wajena domin mu cika burinmu
a kansa."

482

TASKARNOVELS.COM.NG
Koda gama fadin hakan sai Sharlisa ta rungume
Shaddadu ta fashe da kuka saboda ba ta son
rabuwa da shi koda na tsawon dakika daya.

Al'amarin da ya karya zuciyar Shaddad ke nan
shi ma ya kama kuka. Sai da suka dade a
kankame da una sannan suka yi bankwana ta ba
shi Tsuntsunta na tsafi, ya hau kan tsuntsun ya
zauna.

Nan take tsuntsun ya bude fuka-fukansa ya
tashi da shi sama. Sharlisa ta daga kanta sama
tana kallonsu har sai da suka kule a cikin
gajimare sannan ta sauke kanta a lokacin da
hawaye ya zubo mata ta wuce kai tsaye izuwa
fada ta zauna akan karagar mulki aka ci gaba da
tafiyar da harkokin mulki kamar yadda aka
saba, wato ta rikewa Shadaddu karagar mulki
kafin ya dawo.

*******

483

TASKARNOVELS.COM.NG
A can dajin Rauful Mausur kuwa, Gimbiya
Ramlatul Siyam da mijinta Laffaru sun ci gaba
da rayuwa cikin matukar farin ciki da kwanciyar
hankali har tsawon watanni.

A sannan ne Ramlatul Siyam ta sami juna biyu,
al'amarin da ya jefa Laffaru cikin tsananin farin
ciki ke nan ya ci gaba da kulada Ramlatul Siyam
ainun har cikin na ta ya tsufa.

A ranar da cikin ya cika wata tara ciť nakuda ta
zo wa Ramlatul Siyam ta fara ihu da shureshure. Nan fa Laffaru ya dimauce ya rasa abin da
zai yi domin bai san ma yadda zai taimaka mata
ba ta haihun. Ana cikin haka ne kwatsam! Suka
ga Aljeni Maruful Dauwaz ya baiyana.

Nan take Maruful Dauwaz ya rinka umartar
Laffaru bisa yadda zai taimakawa Ramlatu
Siyam, shi kuwa sai ya himmatu yana mai bin
umarnin.

484

TASKARNOVELS.COM.NG
Duk da haka sai da ta shafe sa'a biyar tana
nakudar sannan ta haifo santaleliyar jaririya
mai tsananin kyau na ban al'ajabi. Aljani Marufl
Dauwaz ne da kansa yaje ya wanke jaririyar.

Koda ya dubi fuskarta sai ya ga a duniya bai
taɓa ganin mai tsananin kama da masoyiyarsa
Gimbiya Rashmin sama da wanann jaririya ba.

Nan take ya ji ya kamu da tsananin son jaririyar
kuma yaji kamar an yaye masa dukkan bakin
cikinsa naduniya. Nan take ya rungume jaririyar
a kirinsa ya fashe da kukan farin ciki.

(BARKA DA DAWOWA SADAUKIN SADAUKAI
BABBAN MASOYI GA GIMBIYA RASHMIN)

Daga wannan rana Aljani Maruful Dauwaz ya
zauna tare da su Sarki Laffaru a cikin dajin
Rauful Masnur ya taya su rainon jaririyarsu.
485

TASKARNOVELS.COM.NG

Da aka kwana bakwai sai aka radawa jaririyar
suna ZIYA'UL HAK.

Haka dai Laffaru, Ramlatul Siyam da Aljani
Maruful Dauwaz suka ci gaba da renon Ziya'ul
Hak har ta fara girma ta shekara bakwai a
duniya.

A wannan lokaci Ziya'ul Hak ta shaku ainun da
Aljani Maruful Dauwaz fiye da ma iyayenta
domin kodayaushe tana tare da shi dare da
rana. Sau tari sai ta yi barci a kan kirjin Maruful
Dauwaz sannan Ramlatul Siyam take zuwa ta
dauke ta ta kai ta cikin tanti ta kwantar da ita.

Lokacin da Ziya'ul Hak ta cika shekara bakwai
ne Aljani Maruful Dauwaz ya fara koya mata
yaki da kansa kuma ya dinga ba ta horon fada.

486

TASKARNOVELS.COM.NG
Kullum sai ya ba ta horon sau uku. Nan da nan
Ziya'ul Hak ta taso da gagarumar jarumtaka.
Tun ba ta fi shekara tara ba ta ke fita farauta
daji ita kadai ta kaso manyan dabbobin daji, sai
dai ka ga ta ratayo Zaki ko Damisa a kafadarta ta
zo gida da shi.

Shi kansa Aljani Maruful Dauwaz sai da ya cika
da tsananin mamaki bisa ganin irin tsananin
jarumtakar Ziya'ul Hak.

Babu abin da ya fi ba shi mamaki face karfin
gudunta, domin shi kansa da suka kasa tsere a
kasa, kasa wuce ta ya yi, nan take ta ba shi
tazara mai yawan gaske.

Sa'adda Ziya'ul Hak ta shekara goma sha takwas
a duniya sai karfin dantsen nata ya wuce gaban
misali, shi kansa Aljani Maruful Dauwaz idan
yana yaki da ita da kyar yake iya kare hareharenta. Akwai lokacin da ta doki kirjinsa da
kafarta guda sai da ya fadi can gefe guda ya ji
487

TASKARNOVELS.COM.NG
kamar janye shi aka yi da majajjawa aka kwala
shi a kasa.

Tun daga ranar ya dada sallamawa
jarumtakarta, domin in ban da Aljani
Sharkamuza da sadauki Najwar ba, to babu
wanda ya taɓa yi masa irin wannan duka sai
Ziya'ul Hak.

A ranar da Ziya'ul Hak ta cika shekara goma sha
takwas ne Aljani Maruful Dauwaz ya kira
Laffaru da Gimbiya Ramlatul Siyam gefe daya
suka kadaita ya shaida musu cewa jiya ya fita
daga cikin wannan daji na Rauful Masnur ya yi
rangadi a cikin daji na gaba.

Anan ne ya yi bincike ya gano cewa Shaddadu
ya girma ya zama gawurtaccen jarumi kuma
Sharlisa ta mallaka masa mashin Galilul Haras
ya fito farautar Ziya'ul Hak domin ya kashe ta
sannan ya zo har nan dajin Rauful Masnur ya
kama Sarki Laffari".
488

TASKARNOVELS.COM.NG

Koda jin wannan labari sai hankalin Laffaru da
na Ramlatul Siyam ya dugunzuma ainun.

Ramlatul Siyam ta fara zubar da hawaye ta ce,
"Yanzu ya za a yi mu yi maganin faruwar
wannanal'amari?"

Aljani Maruful Dauwaz ya yi ajiyar zuciya
sannan ya ce, "Hanya daya ce za mu bi mu yi
maganin wannan matsala.

Dole ne ita ma Ziya'ul Hak ta yi shiri ta tafi
farautar jarumi Shaddadu domin ta hallaka shi,
amma fa idan yana tare da Mashin Galilul Haras
ba ta isa ta iya yi masa komai ba, amma tunda
shi yaro ne ai mun fi shi wayo da dabara.

Ni zan yi wa Ziya'ul Hak rakiya a cikin wannan
tafiya domin na zamo mai ba ta kariya da
489

TASKARNOVELS.COM.NG
shawarwari akan yadda za mu sami nasara akan
Shaddadu koda kuwa zan rasa rayuwa ta.

Ku sani cewa wanzuwar Ziya'ul Hak a doron
kasa shi ne abin da ya hana ni kashe kaina,
saboda ta dauke mini kewar masoyiyata.

Yanzu sai ku shirya mana wannan tafiya ku yi
bankwana da ita."

Nan take Ramlatul Siyam ta kirawo Ziya'ul Hak
ta sanar da ita duk abin da ake ciki.

Ba tare da ɓata lokaci ba Ziya'ul Hak ta yi
bankwana da iyayenta tana kuka su ma suna
kuka suka rabu suna masu yi mata fatan nasara.

Nan take Ziya'ul Hak ta hau kan bayan Aljani
Maruful Dauwaz shi kuma ya bude fuka-fukansa
490

TASKARNOVELS.COM.NG
ya tashi da ita sama suka luluka a cikin
gajimare!

A nan muka kawo karshen littafin MAZAN JIYA
na uku (3)
*****************

WANNE IRIN BAKIN GUMURZU ZA A YI IDAN
JARUMI SHADDADU DA JARUMA ZIYAUL HAK
HAR SUKA HADU?

SHIN SHARLISA ZA TA CIKA BURINTA AKAN
SARKI LAFFARU?

YAYA KARSHEN RAYUWAR JARUMI SHADDAD
ZA TA KASANCE?

SHIN ZAI YI SOYAYYA KUWA A RAYUWARSA?

491

TASKARNOVELS.COM.NG

YAUSHE NE ZA A JI LABARIN SADAUKI HULKAS
NA BIRNIN ROMANIYA WANDA SHI NE CIKON
JARUMI NA UKU DAGA CIKIN MAZAN JIYA?

Mu hadu a littafin MAZAN JIYA 4 (Kashi na
hudu) don jin ci gaban wannan kasaitaccen
labari mai matukar kayatarwa.

Muna neman afuwa ga makaranta bisa tsayin
labari, hakan ya faru ne sakamakon tsayin da
hikayar take da shi.

Daga mai debe muku kewa a kullum da ko
yaushe.

ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI
(The King of Adventure Story)

492

TASKARNOVELS.COM.NG
Ni Maiboko, ina rokon makaranta wannan
gawurtaccen littafin, da mu yi kokari mu
tasirantu da kyawawan dabi'un da suka siffantu
a cikin wannan hikayar.

Mu kalli dalilan da suka sa Maruful Dauwaz ya
yi nisan kwana sannan kuma yake samun
nasara a kan duk abin da ya sa a gabansa,
sabanin gagarumar nadama da tashin hankalin
da sarki Lafaru yake a ciki

Rayuwar aljani Maruful Dauwaz abar nazari ce
da kwaikwayo duk da ta kasance a cikin hikaya
ne.

Aljani Maruful Dauwaz, yana daga cikin dalilan
da suka sa nake wannan posting ďin.

A karshe, yiwuwar cigaba da littafi na huďu na
alakanta hakan da lissafin lokaci.

493

TASKARNOVELS.COM.NG

494


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels
End Ads