na taƙura maka"
da sauri ya fara tattaɓa jikin yaron yana cewa "meyasa baki kirani ba? zazzaɓi ke damunshi? bari na kira ayi mishi allura"
tace "tom na gode"
kira yayi dr mace ce ta shigo har ɗakin, yana zaune kusa dasu ta shigo da sallama, tashi yayi ya fita bayan ya mata bayanin yaron ne babu lafiya, yana fita rahama ta kalli dr tace "baiwar Allah dan Allah ki rufamin asiri kada ki faɗa mishi gaskiya wallahi ɗana lafiyanshi ƙalau"
murmushi kawai dr tayi sannan tace "kinyi wayo"
bata kara magana ba bayan wannan maganan data faɗa mata rahama se juya maganan take a ranta, me take nufi da nayi wayo? wannan tambayan take yiwa kanta, saida ta ɗan jima kafin ta fita Allah yasa shima ya fita baya nan kawai ta tafi.
ido rahama ta zubawa nawal, wannan yaron ko dai kyawunshi ze zame mana bala'i ne ya rabbi?
meyasa yake da kyau haka? kodai na fara ɓoyeshi ne?"
rufe ido tayi tace "ya Allah kaine kake halitta Allah kasan dalilin wannan kyawun daka baka ɗana, ya rabbi nima kyawuna jarabtata kada kasa shima ya zama kyawunshi jarabtarshi Allah ka bani mafita ka tsaremin ɗana"
wayar daya siya mata ta ɗauka tasa numbern data haddace tun a kauye yauma a kashe kamar kullum, nana kanwarta itace ta bata shawaran kada ta bari ta rabu da numbern daya alakanci Alhaji Alhasan hakan yasa ta haddace wannan numbern kuma kullum saita kira taji a kashe, bata karaya cigaba take da kira, sauka tayi a gadon ta rufe kofan da makulli sabida nawal yanzu tana tsoron barinshi a ɗakin, girki tayi musu bayan ta dawo ta tarar ya tashi, murmushi tayi ta zauna kusa dashi tace "yaron Ammi ka tashi?"
rungumeta yayi yace "na tashi ammi, amma nayi mafarki wai wani mutum ya kasheki ni kuma inata kuka sai babanki yazo ya rike hanunki kuka tafi wani waje me flower da apple da abu masu kyau ni kuma na zauna anata bani wahala anata dukana ana kona ni da ruwan zafi"
ido kawai ta zuba mishi ta kasa daina kallonshi, kawai ta rungumeshi ta fashe da kuka, tashin hankali ta kuma shiga akan wanda take ciki, yace "ammi ki daina kuka"
share mata hawayen yayi, ta fara bashi abincin, ta daure ne kawai amma kuka take ji sosai, ya karɓa shima ya fara bata, zatayi magana abincin yabi kanta take ta fara tari, da gudu ya sauka a gadon ya fita domin ɗauko mata ruwa, yaje fridge ya buɗe ya ɗau ruwan gora ya juya da gudu ze kai mata, kafa akasa mishi ya faɗi kasa akan tile ɗin tim, azaba yaji a jikinshi har ya kasa ihu, yaron dake harɗe da hannu a kirji yace "kana agola shine zaka fi ɗan gida gata? kai yanzu har ka kai ka rinƙa yawo a gidannan kamar ɗan da dady ya haifa? wallahi munyi sake da muka bari ma ka samu waje, kana shege mara uba kuma agola kazo gidanmu harda ɗaukan ruwa a gora?"
tashi yayi jin tarin Ammi yana karuwa, ruwan yasa hanu ze ɗauka aka taka hanunshi akan ruwan, ihun azaba yayi, wani ne daban shima ɗan alhaji ne, duka suka fara mishi kamar ba yaro me shekara tara ba, duka suke mishi sosai ɗayan yace "har dady ze fi sonka a kanmu? sabida ka fimu kyau ne ko? to yau sai mun lalata wannan kyaun, habib ka ɗauko acid a ɗaki"
jin haka ya fara rokansu "dan Allah kuyi hakuri...."
da duka suka rufe mishi baki, ɗayan me suna habib ɗin yaje ɗauko acid ɗin ɗayan kuma yana rike dashi, ganin zasu cutar dashi su lalata mishi fuska, ya ciji kafanshi, ihu yayi yana duba ƙafan ɗaukan goran ruwan yayi yasa gudu yana shiga ɗakin ya rufe kofan, ammi har ta galabaita bata iya magana ruwa kawai take so, ruwan ya bata tasha sannan ta fara dawowa hayyacinta, a gefe ya rakuɓe yayi shiru yana tuna abinda suka mishi, kallonshi tayi duk a firgice yake ga kuma shatin duka a duk jikinshi, da hanu ta mishi alaman yazo, zuwa yayi ta rungumeshi kawai tayi shiru, tun daga ranan ta fara rufeshi a ɗaki bata taɓa bari ya fita ko makaranta bata bari yaje yana ɗaki.
Alhaji Umar ne ya shigo yace "rahama yau anyi rasuwa kuma dole sai kunje keda matata"
ta kalli nawal dake karatu sannan tace "to zamu je"
yace "banda nawal ze zauna da ƴan uwanshi a gida"
shiru tayi jikinta ya mutu, tace "gara dai na tafi dashi sabida..."
tsawan daya daka mata yasa tayi shiru, cikin ɓacin rai yace "baki yadda dani bane?"
shiru tayi kanta kasa, yace "shikenan tunda baki yadda dani ba, na lura ɓoyeshi kike bakya so ma yana zuwa wajena, tunda haka ne babu komai zan fita harkan ɗanki"
tace "kayi hakuri ba haka bane shima kamar ɗa yake a wajenka zan barshi"
yace "ba komai ki tafi dashi"
tace "a,a ai gaisuwan rasuwa babu jimawa zamu dawo"
yayi shiru kawai ya fita, ta tashi ta shirya tasa hijabi sannan ta ɗau makulli tace "nawal bari muje muyi gaisuwan zan kulleka a ɗaki karka kuskura ka nuna kana ɗakin nan kaji?"
yace "to Ammi"
rufeshi tayi sannan ta fita, matarshi har ta shirya ta watsa mata harara sunkuyar da kai tayi yace su tafi, a motarshi suka tafi shi yake driving hankalinta ya kwanta da tare suka tafi dashi, gidan suka shiga shi kuma ya zauna da maza a waje.
yana ganin sun shiga ya tashi ya shiga motarshi ya koma gida.
babu kowa a gidan sabia ya bawa habib kuɗi yace suje suyi shopping idan sun tafi, hakan kuwa akayi ya rage daga shi sai nawal, knocking na kofar yayi, ba'a buɗe ba, yace "nawal ka buɗe kofa mana"
shiru nawal yayi ya ɓuya a bayan gado yaki yin ko motsi, Alhaji Umar yayi dariya mara sauti sannan ya koma ɗakinshi, da spare key ya dawo ya buɗe kofan, nawal dake ɓoye a can bayan gado ya rufe baki sabida amminshi tace kada ya amsawa kowa, yace "nawal dadynka ne fa yake kiranka meyasa ba zaka amsa ba?"
nawal yayi shiru yana kallonshi amma shi baya ganinshi, yace "to shikenan tunda ba zaka amsa ba zan tafi"
yi yayi kamar ya tafi, nawal ya fito daga ɓuyan yana cigaba da rubutunshi ganin ya tafi, ashe be tafi ba ya ɓuya ne shima, ji yayi ana shafa bayanshi, a tsorace ya juyo yana kallon dady daya cire duk kayan jikinshi ya rage haihuwan uwarshi, ihu zeyi ya toshe bakinshi, yace "kar kayi ihu zan siya maka sweet zan siya maka ice cream sannan duk abinda kakeso zan rinƙa baka idan ka yadda mukayi abinda nake so, kada ka faɗawa kowa zan kaika makka kayi karatu acan sannan zan siya maka jirgi sabida tunda na ganka na kasa samun nutsuwa hakan yasa na fara bibiyan rayuwarka har Allah ya kawo ranan da amminka ta faɗi na kaita asibiti, nawal kai yaro ne har yanzu baka san komai ba, wannan kyawun naka shine zai janyo maka abubuwa dayawa a rayuwa ciki harda sa'a da rashin sa'a, mutane dayawa suna addu'a amma basu san wannan addu'a da sukeyi basa yinsa akan daidai ba, kowa cewa yake Allah ya bashi yaro kyakkyawa kamar wane ko yarinya kyakkyawa, saide suna manta cewa idan har kyawun alkhairi ne, akwai kyawun da babu alkhairi a cikinta, kaga kai zakayi saurin janyo hankalin mutum a kanka kamar yadda ka janyo hankalina dana abokai na, da kasan yadda suke bani manyan kuɗaɗe sabida na kai musu kai koda na rana ɗaya ne da kayi mamaki, amma nima ban samu abinda nake so ba sai yau zan samu, yawanci yara masu kyau suna yawan rashin lafiya sabida bakin mutane idan sun gani sun yaba wani bakinshi babu kyau, yara masu kyau basu fiye samun abinda suke so ba a rayuwa, bama yara ba har manya, mace idan ta fiye kyau bata sakewa a cikin mutane zata rinƙa tsarguwa, ba wannan ba yanzu idan mun gama zan siya maka sweet"
kuka yake yi yana kwace kanshi be san me zaiyi ba amma yaga yana sauke wandon jikinshi da ammi tasa mishi, cizon hanunshi yayi ya sakeshi, gudu zeyi ya kamoshi akan gadon ya wurgashi ya juyo dashi ta baya yake harinshi, jin wani abu me zafi yana ratsa bayanshi yayi ihu yana tureshi, Alhaji Umar babu tausayi yake nema gadan gadan yayi luw*ɗ* da nawal, ya gama yage duk kayan jikin yaron, nawal cikin tashin hankali da zafi ya ɗau dustbeen dake gefe ya kwala mishi, sakinshi yayi, da gudu yaje ya ɗauko kwalban dake gefe yazo ya kwala mishi aka, faɗuwa yayi a kasa jini ya fara zuba daga kanshi yana sauka kan tiles na ɗakin, jikin nawal yana rawa ya rasa yadda zeyi ganin jini ya durkusa yace "dady ka tashi, dady? dady?"
rasa yadda zeyi yasa ya zauna ya fara kuka.
rahama tana gidan mutuwa amma hankalinta akan gida, tashi kawai tayi ba tareda ta jira matar Alhaji ba ta fita daga gidan, ganin babu motarshi taji bugun zuciyarta yana karuwa, mashin ta tara sannan ta tafi gida, tun a bakin kofa ta fara jin tsinkewan rai, shiga ciki tayi ta wuce ɗakinta, ta ciro makulli zata buɗe da mamaki taga kofan ya buɗe, shiga tayi nawal yana ganinta yazo da gudu ya rungumeta, ta kalleshi ta kara kallonshi sannan tace "meyasa ka cire kayanka?"
yace "dady ne ya ciremin"
jikinta yana rawa sai yanzu taga Alhaji dake kwance cikin jini, da sauri taje ta buɗe wayarta data aje kafin ta tafi ta kunna recording ɗin taji duk abinda ya faru, jikinta yana rawa tace "juya bayanka nawal"
juya baya yayi, ta fara duba bayanshi ta juyo dashi tace "ka gayamin gaskiya babu abinda yayi maka?"
yana kuka yace "naji zafi a nan"
ya nuna mata bayanshi, zama tayi daram a kasa tana maimaita kalman "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un"
hanu ta ɗaura a kanta tace "na shiga uku, ya Allah wani irin jarabawa kake min? ya Allah wani kuskure na aikata bayan wanda na aikata a baya?"
rasa yadda zatayi yasa ta zuba musu ido kawai tayi shiru, nawal a gefenta ya zauna yayi shiru, muryan hajiya asabe uwar gidan Alhaji taji tun daga bakin gate tana bala'i, kallon gawan sannan ta tashi da gudu ta fita, dawowa tayi da ashana a hanunta, akan gadon ta casta ashana nan take katifa ya kama da wuta, ɗakin ma ya fara karɓan wutan, nawal ze gudu ta rike hanunshi tace "kayi hakuri ɗana dole sai mun ƙone sabida gudun zargi ya zama dole na kona komai domin ba zan iya bari a kama ka da laifin kisa ba, ni uwace dole na kare ɗana"
yana kuka yace "ammi wuta, wuta fa ammi zamu mutu"
shiru tayi tana damƙe da hanunshi duk yadda yake so ya kwace taki barinshi, har wutan ya kama kasan riganta ya fara ci.
*Shima ɗa ne complete is ₦400 via 8144818849 hauwa shuaibu mapi moniepoint, evidence via 08144818849*
~Ammi yana fita daga madaidaicin ɗakin ta ɗaga wayan da take amfani dashi kullum ɗan karami ta kalli wayan sannan ta kalli sama tace "ya rabbi ina kara rokanka kamar kullum ya Allah ka taimakeni na samu me wannan numbern sabida rayuwar ɗana nawal na gaba, Allah kaga halin da nake ciki ina kara gode maka, ya rabbi dan darajan fiyayyen halitta ka taimakeni, dan tsarkin mulkinka dan girman al'arshinka, dan darajan sammai da kassai guda bakwai, dan darajan kowane abinda ka halitta me tsarki, Allah kasa na gano inda mahaifin nawal yake, Allah banaso na mutu ban haɗashi da kowa nashi ba, Allah ka amsa min addu'a ta"
share hawaye tayi ta kira numbern kira biyu ba'a ɗauka ba, ta kara kira na uku kenan ba'a amsa ba, jikinta a mace ta aje wayan tana kallon kofa tayi tagumi, kamar a mafarki taji wayan yana ruri da sauri ta ɗauka tasa a kunne tace "hello hello hello? kuna jina? kuna iya jina?"
wanda yayi magana babban mutum ne yace "wa ke magana?"
tana farin ciki tace "bawan Allah dan Allah daga ina kake?"
yace "kamar yaya daga ina nake ke ɗin wacece?"
tace "am dama ni ɗin tsohuwar matar Alhaji alhasan ne ya aureni a kauyenmu to yace min duk lokacin dana tashi nemanshi idan na sameka kaine babban abokinshi kaine zaka haɗani dashi"
yace "Alhaji alhasan?"
tace "kwarai Alhaji alhasan medara"
yace "tabbas ya faɗa miki gaskiya amma a baya ne yanzu bana tare dashi mun rabu kuma banaso a kara min magananshi domin banida alaka dashi"
ze kashe wayan tace "dan girman Allah kaji kaina ka faɗamin inda yake dan Allah ba dan halina ba"
yace "ba komai zan tura miki address nashi"
tace "ban san wani abu address ba bawan Allah ka faɗamin da baki ta yadda zan gane"
yace "sunana Alhaji sammani karki kara ce min bawan Allah"
kallon wayan tayi da mamaki jin kalman jahilci daya fito daga bakinshi, tace "to"
yace "yana garin Abuja unguwan low-cost"
kashe wayan yayi bai kara yin wani magana ba, bin wayan tayi da kallo, wani irin murmushi take yi haɗe da hawaye, ɗaga kai tayi ta fara jera godiya wa Allah, hawaye take yi na farin ciki sabida ta samu mahaifin nawal.
washe gari nawal yazo ya durkusa ya gaisheta, daga masallaci ya tashi, tace "zauna anan nawal"
zama yayi a gefenta, yana kallonta, tace "nawal yau zamu tafi Abuja, yau zan haɗaka da mahaifinka"
a razane ya kalleta da tsananin mamaki akan face nashi, da kyar ya harhaɗa magana yace "babana? dama yana raye?"
jijjiga kai tayi tana hawaye tace "tabbas yana raye kuma yau zan baka amsan daka jima kana tambayata"
sunkuyar da kai tayi dan kunyanshi take ji, tace "nawal ba ta hanyar aure na haifeka ba, nawal ka yafemin kuskure nayi na haifeka babu aure ka yafemin...."
rufe bakinta yayi da hanu, kallonshi take yana girgiza kai sannan cikin sanyin muryanshi da rashin son surutu yace "karki nemi yafiyata ammi na jima da yafe miki komai"
tace "na gode nawal amma yau nake so mu tafi abuja acan zan sauke nauyi na nuna maka wanene mahaifinka"
yace "duk abinda kikeso shi zanyi Ammi, amma idan har hankalinki be kwanta da hakan ba na hakura zanyi rayuwa dake kawai sabida dake na saba"
girgiza kai tayi tace "nawal girma nake yi, idan na mutu ban haɗaka da kowa naka ba zan cutar da kai kuma zan barka cikin kunci na rashin mahaifi zan kaika na nuna maka mahaifinka"
yace "to ammi"
tace "kaje ka shirya"
tashi yayi ya fita, yana shiga ɗaki ya daka tsalle yace "zanga babana nima za'a daina min gori zanga babana"
cikin murna ya harhaɗa kayanshi marasa kyau sun tsufa sosai ya haɗa na Ammi wanda ya siya mata a akwati yasa sannan ya ɗauki kuɗin da yake tarawa ya rike, keken daya siya mata na guragu yaja sannan ya shiga ɗakin ya shiryata ya zaunar da ita akai, fita yayi a tasha sukaci abincin safe, motan Abuja suka shiga suka ɗauki hanya, farin cikin data gani akan fuskanshi ya tabbatar yana son mahaifinshi kuma ya jima yanason ganinshi.
sun iso Abuja lafiya ya tari taxi suka shigar da ita kafin ya shiga suka kama hanyan unguwan Alhaji alhasan wato low-cost, nawal sai bin gidaje yake da kallo wasu irin manyan gini yake gani kamar a london, komai a tsare gashi unguwan shiru babu hayaniya, murmushi yayi sabida bayason waje me hayaniya, me taxi yace "hajiya banji kunyi magana bafa mun jima da shigowa"
ta kalli kerarrun gidajen sannan tace "malam nima ban san gidan ba dole sai mun tambaya ka taimaka tunda kaga halin da nake ciki ka tayamu neman gidan"
wani tsakin da yaja saida nawal ya kalleshi, yace "dama neman gida kuka ɗaukoni nayi muku?"
tsayawa yayi yace "ku fitamin a mota"
shiru tayi, ya daka musu tsawa yace "ku fita nace"
nawal ne ya fito ya buɗe marfin motan ya fito da ita, kayansu ya ciro ya rike ya biyashi kuɗinshi baiyi magana ba ya fara jan ammi akan keken suka fara tafiya ba tareda sun san inda zasu je ba.
a kofan wani babban gate tace "nawal mu tsaya muyi tambaya anan gidan"
yace "to Ammi"
knocking yayi, ba'a buɗe ba ya kara knocking, megadi ya buɗe ya kallesu yace "su waye ku?"
tace "dan Allah"
matsa musu yayi yace "ku shiga ciki"
nawal ya turata suka shiga ciki sannan yace "kune ƴan uwan Alaji na kauye da kuke zuwa ku addabeshi da roko ko?"
Ammi tace "A,a wallahi mu tambaya muka zo..."
muryan me gidan sukaji yana kiran driver, har ya iso wajen yana masifa yace "ina kiranka ba zaka amsa ba baka jina ne?"
ya durkusa kasa yace "kayi hakuri dan Allah wannan ne suka ɗauke min hankali"
kallonsu yayi nawal ya ɗan durkusa ya gaisheshi, ɓata rai yayi yace "su waye ku? daga ina kuka fito?"
ammi tace "tambaya muka zo yi dan Allah...."
cikin daka tsawa yace "munyi muku kama da waɗanda zaku zo tambaya a gidannan?"
shiru sukayi, yace "zaku fita ko sai nayi maganinku?"
ganin suna tsaye yace "bingo"
karenshi ne ya fito, jikin ammi ya fara rawa ganin karen yana nufo su, ta rufe ido tace "nawal ka fita dani kare"
nawal yaja keken suka fita yama manta kayansu a gidan, karen yana gudu suma suna gudu har suka yi nisa kafin ya koma, hawaye ta fara tace "nawal ba zamu samu mahaifinka ba wannan mutanen masu kuɗi basu da imani nawal gara muje mu zauna cikin talakawa ƴan uwanmu koba komai idan mun mutu za'a sallacemu"
yace "kada kiyi saurin karaya ammi muyi ta addu'a"
tafiya suke yi har dare basu samu gidan ba, a kofan wani gate suka kwana sabida babu kuɗi a wajensu komai nasu ya ƙare, asuba yaje masallaci yayi salla yayi mamaki da babu wanda ya buɗe gate ɗin domin zuwa salla har gari yayi haske kafin aka buɗe gate, megadi yace musu ku su waye?
ammi tace "dan Allah muna neman gidan Alhaji alhasan medara"
yace "lafiya kuke neman gidanshi?"
nawal zaiyi magana tace "eh lafiya ƙalau ni kanwar mamanshi ce daga kauye"
yace "okay wancan shine gidanshi"
ya nuna musu, kallon nawal tayi shima ya kalleta, rungumeta yayi yace "ammi mun samu"
murmushi tayi haɗe da hawaye tace "alhmdllh na godewa Allah"
turata yake akan keken har suka isa kofan shi yayi knocking, buɗewa akayi megadin