x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 18 - SHALELAN BABA

  • 51001 words
  • 54000 words
  • Out of 64847 words

Category: Love Stories

Views 90

02 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
wata daya

Alhaji Tahir yace saide kuma wani hanzari ba gudu ba kasan yarinyar tana ma karanta a yanzu

Daddy yace a a wannan ai ba abin damuwa bane, Nima yaran wajena University suke shirin tafiya, kaga kowa sai tayi karatunta a Dakin mijinta


Nan da nan kuwa kowa yayarda da wannan hukunci na daddy, aka sake gaisawa sannan suka tafiya gida domin yasanar wa dasu momy hukuncin dasuka yanke

Shima Alhaji Tahir yashiga gida domin sanarwa da hajiya hafsat abinda yake faruwa, yashiga gidan da goron sa da alawa nasaka Rana







(kuyi hakuri da wannan Banda chrgi ne wallahi ngd🙏🏻)




Sharhi, comment, share to others groups Dan Allah 🙏🏻



















Amnah El ✍🏻💕SHALELAN BABA💕
(Romance)

Writing by Amnah El yaqoub



41&42


Yau gidan anty jiddah anyi baqi, yanbiyu sunzo sai fira suke da sajida, kasancewar ba zuwa suke Sosai ba, sai zuwan nasu yayi Mata dadi

Anty jidda na waya da mijinta adaki, Bayan sun Gama takira Bilal
Tace doctor Har yanzu Baka zoba Akan maganar danace zamuyi shekaran jiya
Jiya kuma bakabimu gidan momy ba daga asbiti saika wuce wajan aiki

Yace eh wallahi, bansamu lokaci nazo ba, Amma yanzu Dama zanje gidan hajiya hafsat, kawai zan shigo tanan, daganan Saina wuce

Tace to saika zo


********

Yana shiga cikin falon yaganta a harde akujera, cikin fara'ah ya Bata goro da alawar hannunsa yace hafsat riqe wannan

Tasa hannu ta karba tana binsa da kallan mamaki

Na menene wannan Alhaji?

Nasaka ranar yayanki ne, ameer da haneefa, nanda wata daya insha Allah za'a daura musu aure, saiki fara shirye shirye

Wanne irin aure Kuma Alhaji? Yarinyar Dana maidata makaranta?

Ita hajiya Amina Aina fada Mata namaida yata makaranta abinda suka kasa yimata
Kwana da kwanaki tana zaune agidansu, amatsayin me aiki, sun zaunar da ita tana musu bauta, sannan ni da take musu aikinma bantaji haneefa tacemin tana karbar kudinsu ba, saide faman wahala datasha

Tsakani da Allah abban Afrah, gida de kamar gidan Alhaji bukar tayaya zasubar ma'aikatansu batare dasun sakasu a makaranta ba, aiko yar islamiya ce sa sakasu aciki

Kuma haka kawai saboda rashin adalci dason Kai irinnasu suzo dawata magana ta aure?
OK sai yanzu ma nagane, saboda dansu Yana kwanciya jinya saboda ita, shine za'a katsewa yarinya karatunta ace za'a Mata aure, bazai iyuba

Ajiyar zuciya yasaki, to yanzu hafsat me kike so ayi?

Kaje kafada musu cewa ni nan, nace bazan Bawa dansu auren yata ba, ai itama tanada gata ba marar galihu bace, shide ameer din tunda namiji ne kuje kuyi masa, Amma Banda haneefa


Yanzu ni din kike so naje nasamu shi Alhaji bukar da wannan maganar?

Cikin fishi taace toshi kuwa yazo yasameka da ita? Qarewa mafa Yaron nan zuwa yayi yadauki haneefa yafita qasar waje da ita, yarinyar Bata nuna masa korafin komaiba, sannan Bata samu iyayensa tafada musu maganar ba
Saikace wata marar gata, wallahi baban Afrah ko ameer dinane yadauki haneefa suka fita wani waje batare da sanina ba dole zan hukuntashi Akan haka

Idan yarinya bame kamun Kai bace wayasan mezai faru?saboda kawai suna taqamar cewa ita yar aikin su ce? Shin masu aiki basuda iyaye ne? Kokuma idan andaukesu aiki Hakan Yana nufin za'a iyayin komai dasu?
Kuma still yanzu azo ace Wai anbada ita, saboda me? Bazai iyu Bama Alhaji, kamaida musu kayansu, ta watsar da goron aqasa 🙆🏻😭

Hannayenta yakama yace hafsat, kiyi hakuri, nasan Yaron nan da iyayensa sunyi Mata laifi, kuma sunzo Har gida sun Bata hakuri kema kuma sunbaki, sannan sun sake neman yafiyarku
Kisani Allah mafa muna masa laifi kuma yayafe mana
Bare mu Yan Adam, yanzu hafsat idan kikace nakoma namaida musu kayan Saka ranarsu, mekike tunanin zai faru? Kina nufin suma zasu Bawa danmu ameer yarsu ne?
Hafsat bazasu bashi ba, saboda muma mun hanasu tamu yar

Alhaji Dan Allah kadenamin maganar wannan marar mutuncin Yaron 🤣🤣tatashi fuuuu tayi dakinta, Alhaji Tahir ya girgiza kansa sannan ya tsugunna yasaka hannu ya tsince goron da alawar

Cikin ransa Yana cewa nide bazance komaiba kiji babu dadi kice nayiwa Dan yar'uwarki maganar daba daidai ba🤣🤣🤣

********

Yana zuwa yadanna door bell, Sajida tatashi tabude, tana ganinsa tasaki murmushi laaa uncle ashe Kaine, sannu da zuwa
Ashe yau da babban baqo kazo mana, kawoshi, ta meqa hannu takarbi Aududu dake hannunsa
Tajuya tana cewa Bari nakira mama

Yace to Sajida, Yana qarasowa cikin falon

Akujera ya zauna, Safah takalleshi tace uncle sannu da zuwa Ina yini?

Cikin fara'ah yace Lfya Alhmdlh, Yaya school

Laaa uncle ai munyi candy

Yace to masha Allah, kice yanzu sai University

Kafin Safah tasake magana
Samah tace masa Ina yini, batare data kalli inda yake ba

Shima Yace lafiya ataqaice,🤣 wato wannan yarinyar shi zata gaisar asheqale ko,yagama lura bataso ma ta kalleshi, to menene da jikin nasa daza'a qi Kallansa?

Itama anata bangaren takaici ne yakamata, ita bazai tambayata ko Yaya gida ba? Batakai ba Kenan

Safah na kallan su tana Daria cikin ranta

Tasake dubansa tace uncle ashe kaima kana zuwa gidan anty jiddah

Ina zuwa mana, tunda yata tana gidan ai dole nazo

Daria tayi tasake cewa to ai yanzu Bata nan uncle, ko wajan wata kazo🤣🤣

Dasauri yace no, no, nazo wajan antynku ne, daganan kuma zan wuce wajan haneefa

Aikuwa uncle muma saimu bika muje muganta, rabonmu da ita tun shekaran jiya

No kusa driver yakaiku, bancika son damuwa ba wani lokacin 🤣

Haba uncle wacce irin damuwa kuma Ana zaune lafiya?

Kema de da shegiyar jaraba kike wallahi Safah, Ana yageki kina qara liqewa a'inda bakida kwarjini, cewar Samah 🤣🤣

Cikin fishi Shima ya kalli Samah din yace ke wato bakida kunya ko? Ba'a Isa dake ba, ba'a Isa asaki bako?

Dede lokacin anty jidda tazo tatarar da wannan rikicin nasu, Safah kuwa Daria kamar me, in Banda Abu irinna uncle Bilal meya Saka Samah din taqi yi? 🤣🤣

Harda cewa ba'a Isa asata tayi ba🤣🤣

Anty jidda tace sannu da zuwa babban doctor

Yawwa anty

(mamaki yakamata, yau Bilal dinne yace Mata anty🤭to inajin de da biyu🤣)

Ta Kalle su tace kutashi kukoma daki, zanyi magana dashi

Safah tace anty, sannan ta kalli Bilal tace uncle inkun Gama ka tabomu saimu wuce


Suna tafiya anty jidda tace Dr Dama zan Baka hakuri ne Akan komawar haneefa gidanmu, banyi Hakan dawata manufa ba, saide Inada babban dalili na nayin Hakan

Dr haneefa itace tafara son haneef, naji hakaanne lokacin dasuke fira itada sajidata
Nan ta bashi labarin komai
Sannan taci gaba da fadin nabarta Takoma can dinne saboda shaquwa tashiga tsakaninta da haneef Har Shima yasota, saboda a lokacin anriga da anyi masa Matan dazai aura
Kuma sai gashi alhmdlh yafara yimata sonda ita Kanta tasan Bata sonsa Har haka, likita cewa yayi zuciyar sa zata Iya samun matsala idan ba'a bashi abinda yake soba

Bilal tace subhanallah

Anty jidda tace to wannan ne dalili na, Amma ban karya alqawarin Dana dauka maba kayi hakuri

Aikomai yawuce anty, tunda anriga da ansa musu Rana ma

Rana kuma Dr? Yaushe?

Yace a a Wai baki saniba? Dazu fa su Alhaji Tahir suka kirani Wai naje manema auren haneefa sunzo
Ai anma Saka Rana nanda wata daya biki, itada ameer da Safah

Yanzu hakama zuwa zanyi gidan inji menene za'a fara shiryawa

Cikin mamaki tace to aikuwa su momy basu fada ba, kuma da alama ma yanbiyu basu saniba

Yace ansaka wallahi, inajin mu kadai ne iyaye muka sani🤣🤣

Tace a a doctor muma ai iyayene🤣

Yace to anty Bari natafi
Kituromin wadannan yaran

Tace to

Tana zuwa Dakin tace yanbiyu tahowarku kuwa daddy Yana gida?

Samah tace a a gaskiya yafita
Tace to kuje Dr Yana jiranku awaje

Duk suka futo, sajida da Samah Da Safah

Suna zuwa wajan motarsa sukaga Yana waya, aikuwa suka Bude suka shiga baya Dukansu, Aududu Yana hannun Samah

Yana Gama waya, yashiga yatada motar, yajuya ya kallesu, waiku driver Kuka samu kome? Duk kun shige baya 🤣🤣

Yakalli Samah data riqe Aududu, yayi tunanin Safah ce, saboda yasan cewa Samah bazata karbi dansaba, dan haka tunanin sa yabashi Safah ce yace, Shiyasa nace Miki banason damuwa😣

Cikin fishi ta kalli sajida da Safah tace Aidama Saida nace muku karmu shiga karmu shiga Kuka nace, aiga irinta nan
Tabude murfin motar tafice ko rufewa batayi ba

Owk Dama kece? Cewar Bilal

Sajida da Safah suka kama Daria qasa qasa
Sukaja murfin suka rufe

Ita kuwa tana tsaye, yaleqo ta window yace idan bazaki shigo ba kifadama na muwuce

Tace kuwuce kawai

Yace OK to Bani Dana inyaso saiki tazama awajan

Tace wallahi bazan bayarba, kuje kawai, driver anty jidda yakawoni

Nifa bance kishigo ba, cewa nayi Bani Dana,sai driver yakawo ki, Nima ai banqi Taki ba🤣🤣

Batace masa komaiba tajuya tafara tafiya da Yaron ahannunta 🤣

Kut lalle yarinyar nan, nizata maida mahaukaci Ina Mata magana ta kyaleni tatafi

Burum yabude motar yafuto, yanufeta gadan gadan, yasha gabanta yatsareta da ido, lokaci daya yayi Mata kwarjini taga yacika Mata ido

Idonsa cikin nata yace Bani Dana

Lokaci daya qwalla tacika idonta cikin muryar Kuka tace Allah bazan Baka Shiba

Iska ya firzar daga bakinsa, yau yaga karfin hali

Yanuna Mata hanya yace to wuce mutafi
Babu musu Tajuya tashiga motar suka tafi

Suna tafiya ahanya ta kawar da Kanta can gefen window, Bama ta kallan inda yake

Har sukazo gidan C.P, (commissioner of police)
Gidan hajiya hafsat Kenan

Yansanda basuda yawa yau a harabar gidan, yanayin parking su sajida da Safah suka futo, shikuwa ya dannawa motar lock 🔒

Samah tafara kici kicin budewa taji Mota arufe,tasan Sarai shine yarufe, Tajuya ta kaalleshi cikin mamaki


Safah tace sajida muje mana

A a Safah, Kinga mujirata mana saimu shiga gaba daya

Me zamu Jira? Da niyyafa yarufe motar, kibarsu su kashe kansu

Taja hannun sajida sukai cikin gidan









(da alama de hajiya hafsat tadauki fishi dayawa, abin yamata rauni🤣Dan yafi karfin ciwo)


Wannan page din nakune masoyan wannan littafi, nabaku shi kyauta🤗
Masu sharhi wallahi kunfi kowa birgeni, dan Allah adinga sharhi tahanake zanji dadi Har insamu qwarin gwiwar yin wani typing din 😊, sharhi Yana temaka wa Sosai, Amma wasu basayi saide acema tnx, wasu kuma suce godia, Wanda sukafi Bani Daria ma sune masu cewa t, Wai t , nide dakacemin t Har gara kacemin sannu wance😃😃, nasan ka kulani



Posting din yau zakuga baida yawa wallahi zazzabi nake, tun Daren jiya, dan yau banmayi tunanin zanyi posting ba, to Amma nasan za'a jirani, ajini shiru, Shiyasa nace bari naayi ko yayane yafi ace anji shiru din, babu sanarwa

Koda ace kunjini shiru to wallahi zazzabi ne yahanani typing, idan kuma kunjini shikkenan Dama haka akeso, gani nande under probability

Ngd Sosai 🙏🏻






















Amnah Muhammad El yaqoub✍🏻💕SHALELAN BABA💕
(Romance)

Writing by Amnah El

Jinjina gareku

Rabiat Mafida ibrhm
Khadeeman Othman
Khadeeja Bilal Sirdeeq
Zaenerb Abouberkhar
Bashirma Halima
Ayshat Abdulkharim
Fateemah Zarah Muhammad
Khadeeja fasih
Feenah Alwasa
Hafsat Aliyu
Abdurrahman(mmn mama novel)

D prince Abba
Princessiko
Maman maama
Samira Aliyu
Nawara Ahmad
Maman Ja'afar
Maman mee'ad
Fatima salihu
Maman Yasmeen
Samira Yahya(gaisuwarki tana samuna)

Ummu farouq

Kai bazaku lissafu ba, Amma Sarai nasan kowa😃🤣Har masu cewa T, nagode Sosai da yanda kuke bibiyata, dakuma Jin lafiya ta, Alhmdlh nagode da addu'arku agareni dukanku masoyana baki daya, zamu Dora daga inda muka tsaya🤗🤗

43&44

Zuba Mata ido yayi, ta kalleshi da tsananin mamaki a Fuskarta

Malam lafiya zaka rufeni amota?

Yaushe zakiyi aure?

Abazata maganar tasa tazo Mata, aure Kuma? Ta kalleshi, menene hadinka da aure na?

Meyasa ne ke kincika rashin kunya da yawa?
Tambayarki nayi, saiki amsa min

Dan Allah kabudemin kofa na fita, wannan wacce irin tambaya ce ta qwa qwa? Tambayar yaushe zaka mutu na auri maatar ka? Dan kaga budemin infice, inba hakaba...

Katseta yayi inba hakaba me?

Nide kawai abudemin kofa

zaki aureni? Yasake jifanta da wata Tambayar

Kallansa tayi ido cikin ido tace Aure de? Ni in aureka? Allah yasawaqe ko maza sunkare 🤣budemin kofa nafita Malam

Aikuwa aure dole, da kinqi da kinso saikin aureni, a Hakan kuma mazan basu qare dinba kinaji kina gani dolen dolenki ki zama tawa

Batace masa komai ba tafara kici kicin Bude kofar saide abin takaicin yaqara Bude Mata

Kanta tadafe 🤦🏻‍♀sai hawaye, lokaci daya jikinsa yayi sanyi, yace sorry, yamiqa Mata hannu yace Bani Abdallah na saina Bude Miki kifice

Tayi banza ta kyaleshi🤣

Yace, kibanishi mana, tasake shareshi, yasaka hannu zai daukeshi da kansa, Tariqe Yaron gam 🤣
Cikin fada yasake cewa nace kibani shi nabude Miki kifice kinqi Bani, kinzo kin tisani agaba kinamin ihu, mekikeso namiki? Yamaida hannu Kan Aududu Yana kokarin daukeshi

Itama tafara kici kicin rikeshi 🤣, Garin kokarin qwatar yaro hannunsu ya sarke da juna, lokaci daya wani irin shock ya kamasu, cikin sauri kowa ya janye hannunsa

Ta Dora Kanta a jikin Aududu tasaki Kuka, wallahi ka budemin

Yaya zaiyi? Yahadu da wadda tafishi masifa 🤣ai dole yabude

Bude Mata yayi, tasa kafa kuwa tafice da d'an ahannunta 🤣
Ajiyar zuciya yasauke yabisu da kallo cike da birgewa, kuma wallahi saita aure shi, azuba agani🤣

********

Suna shiga falon sai Mami suka gani ita kadai, cikin fara'ah ta kallesu tace a a yau yanbiyu ne a gidan Namu? To wacece ne acikin ku Samah ce ko Safah? 🤣

Safah aka sunkuyar dakai qasa, alamun anzo gidan surukai, 🤣

(um kuma da kinji ansa Rana fa 😲😲)

sajida tace Mami wannan Safah ce, nikuma sajidan anty jiddah

A a, sajida sannunku da zuwa, ta kalli Safah, kuma ke Banda abinki sai kiyi shiru🤣, aini ba sirikarki bace maminki ce, taso kidawo nan ki zauna, ta nuna Mata waje kusa da ita

Cikin kunya ta girgiza Kanta, murmushi Mami tayi tace tokushiga Dakin nasu, suma su Haneefan suna ciki
Sajida tace to Mami, suka miqe sukayi ciki

Mami tabi Safah da kallo, ita kunya ameer kunya, ko Yaya za'ai wannan Zaman aure 🤣🤣

Samah ce tashigo da yaro ahannu, mami ta kalleta taga alamun kamar tayi Kuka, ga kuma yaro a hannun ta, Amma Sai tayi shiru, Har qasa itama ta gaisheta cikin fara'ah Mami tace Samah sannunku da zuwa, wannan din Yaron Waye ahannunki?

Bilal ne yayi sallama yashigo, ta kalleshi, anan Mami tagane Kenan Dan nasane, Samah tatashi tayi hanyar Dakin da batasan ma ko shine nasu haneefa ba, sai tayi dace shine 🤣

Mami tace a a likita bokan turai, Saida yashafa sumar kansa yagaishe ta cikin murmushi

Tace lafiya kalau muke baban haneefa, Ina kasamo mana yaro ne?

Ina Tambayar Samah Naga tana kallonka, ga idonta kamar tayi Kuka

Mami Abdallah nefa, qanin haneefa, nakawo Mata shine, rannan munyi magana da ita tace tana so naganshi, nakawo Mata shi, shine Samah ta karbeshi

Kuka kuma saboda nace ta aure nine, shine take Kuka, waai ko maza sun kare🤣

Murmushi Mami tayi, Kai Bilal wannan fadan naku babu ruwana aciki, yafi karfina😃
Tatashi tsaye Bari naturo Maka abban afran Yana ciki

Shima yabita cikin murmushi yace to Mami

********
Tana shiga Dakin duk suka bita da kallo, sajida tace kaga masoya
Ku futowarku daban ce

Qyaleta tayi tanemi waje a gefen gadon ta zauna, ta ajiye Abdallah, shalele tasa hannu ta daukeshi cikin murna, ya kalleta yaga baisan taba aikuwa yafara Kuka
Takalli Afrah tace Kai kiga Yaron nan Afrah nizaiwa qiwa, Afrah tace ato Ina yasanki

Sajida tace wallah muma bai sanmu ba, Amma damuka daukeshi baiyi Kuka ba

Shalele tace aikuwa wallahi saide kayi, saina daukeka🤣
Yaro kuwa yasaki Kuka

Ta Kalle shi tace Kai Aududu, tsabar rashin m karasa wa zakayiwa qiwa saini?🤣

Afraah tace Dan Allah ki ajiye Yaro yaje gun Wanda yakeso anan,kawai kin matsa masa

Sajida tace kawoshi, takarbeshi, aikuwa yayi shiru, suna zaune Yana hannun sajida saiya koma wajan Samah, Kodan yaga ita tashigo dashi ne oho

Ita Kuma tana cike cike da haushin Bilal, kuma tashigo ma ba Wanda ya kulata🤣, saita shareshi, kawai tasaka Kanta acinya tasa musu kuka

Kunsan Yaro, idan yaga babba Yana Kuka Shima kukan yake, dan haka Shima Aududu yasaka Kuka

Duk suka juya suna kallan su, Safah tace a a me aka musu ne, dagake Har Yaro kuna Kuka

Afrah tace Samah meyake faruwa?

Tayi musu shiru

Shalele tace Samah kode keda uncle Bilal ne?

Duk tayi shiru ta Qyalesu

Safah na ganin haka tafara hawaye, tace Samah Wai miye na kukan,? Wallahi idan baki daina kukan nanba Nima bazan Dena ba, ai kinsan de abinda Hakan yake jawo mana

Sajida tayi murmushi tace um yau munga Yan biyu🤣🤣, wato muda ba Yan biyu ba, mune kukan baya jamana komai 🤣

Afrah tace sajida Dama haka suke?

Haka suke wallahi, daya na Kuka yanzu dayar ma zata fara koba dalili, aide yanzu kingani, tunda bataji komai ba tahau kukan itama🤣, idan jinya daya takeyi to itama dayar yanzu zakiga ta kwanta, Dama can haka suke, karku damu

Shalele tace haba sis sajeey yazakice karmu damu
Tatashi ta dawo kusada Samah tace Samah, dan Allah meyake faruwa?

Cikin Kuka tadago Kanta tace Wai cewa yayi wallahi saiya aureni, nace masa banaso banaso Amma yace shi wallahi saiya aureni, nikuma wallahi bazan yardaba yaje ya aureni yakaini gidansa yaita jibga🤣🤣

Shalele tace Waye? Wai uncle Bilal din kike nufi?

Ta daga Kanta alamun eh

Aikuwa suka kwashe da daria 🤣

Safah ta share hawayenta ta harari Samah, tashige toilet domin wanke idonta 🤣

Afrah tace kuma yanzu menene abin Kuka Samah?gayen baida matsala, kawai de kunsamu sabanin fahimta ne, ni banga aibunsa ba

Shalele tace nikam nayi murna, zanyi farin ciki idan kika aure shi, sannan ta kalli Afrah kekuma Afrah karki sake cewa babana Gaye, saikace wani Yaro?

Afrah tace to sister haneey tsoho🤣Kema Naga alama zamanki dashi yafara shafa Miki son girman

Tace eh naji

Sajida tace yanzu de Samah kiyi hakuri, Kinga dukanmu muna San abin nan, idan kika amince shikkenan zance ya qare

Safah data futo daga toilet itama tace ku kurabu da ita, tana Sansa gulma ce, gashi nan ta riqe masa da, idan Bata Bata Sansa ai bazata so Yaron saba

Afrah tace laaa waiji kuke dansa ne?qanin haneefa nefa, Yana son Yara ne kawai shiyasa ya riqeshi

Samah da sai yanzu tayi magana tace au dama ba dansa bane shine yaketa nuna min wani iko? Harda cemin nabashi dansa ni driver yakawo ni?
Wallahi DANA SANI tun a lokacin zan ce masa yabari saiya Haifa tukunna

Dukansu suka hade Mata baki sukace saikun Haifa de, 🤣🤣

Sajida tasake cewa Dama yanzu ga sister haneefa nan🤣

********

Yayi shiru a office dinsa shi kadai, ga ayyuka agabansa nan yakasa qarasawa, yarinyar nan tana so ta kashe shi,🤦🏻‍♂tun ranar dasukazo gidansu Har yau taqi Bude wayarta, Yaya takeso yayi? Hauka takeso tasashi kuma Bayan jinyar daya kwanta adalilinta?

Wayarsa tayi qara, yadauka yakara akunne, yallabai anturo design din takalman dakayi magana a kansu tun jiya Amma bakayi maganar meeting din da za'a yiba

"Zan nemeka Bayan naduba" abinda yace Kenan, daga daya bangaren akace Okey sir

Turo kofar office din nasa akayi, wani ma'aikaci ne, yace yallabai ga wadannan takardun Wanda zaka duba ne kafin a shiga meeting, anriga da angama aikin komai, saide dubawarka dasaka hannun ka da ake jira

Sannan
End Ads