x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 18 - HEEDAYAH

  • 51001 words
  • 54000 words
  • Out of 115649 words

Category: Love Stories

Views 138

22 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
labarin abinda Mami tayi mata ta sanar masa tana matsar kwalla, tace "A gantale fa ta barta gun mai aiki dake naso uwa an tuttula mata jarkan man gyada, ynxu hka fa ga Mai aikin can na sa ta wanke bandaki na, kuma ban amince ta shiga bandaki na ba sai da tayi wanka wllh, to mata daga dawowa kuma sai ki dauke min yarinya haka kawai, yini fa muka yi tare da yarinyar bbu wanda ya ji kanmu, muna ta hira fa in gaya maka" Junaid yace "Gaskiya bai kamata....." Kaka tace "Allah ya maka albarka, daga shigowa gida sai ta fara fito da mugun halinta da wuri wuri hka tun ba aje ko ina ba, ni sai nayi tunanin ma ko tasan uwar yarinyar ne wnn isa haka da ta nuna min...." Junaid ya d'an yi murmushi yace "Xan je in dauko maki ita ynxu kaka" kaka tace "Amma fa kar kace nace maka komai, ba ruwana kar ta kullaceni, kawai dai kayi mata nasiha ta canxa halinta, wannan ba halin xaman gidan miji bane..." Ya mike still smiling yace "In sha Allah kaka, bari in je in dawo" Kaka tace "Allah maka albarka, ni dai gwara min kai a kan kowa ma a gidan nan" Kaka ta kalli Khadijah da sauri tace "Ke 'yar banxa kin gaishe sa ma kuwa da ya shigo? Ku dai 'ya yan Amadu baku da hali tirrr" turo baki Khadijah tayi tana ci gaba da abinda take, shi dai Junaid tuni ya fita ya rufe mata kofa, part din Mami ya nufa ya sameta xaune parlor ta daura kan Heedayah a cinyarta tana mata gyaran gashi, Heedayah ta mike xaune da sauri jin muryarsa, ya xauna saman kujera ya gaida Mami, Mami ta amsa tace "Na xata da Farida xa ku xo" yana kallon Heedayah yace "Aa, Uncle said she should stay" Mami tace "Okay, how are you" yace "Alhmdllh, ya aiki" tace "Mun gode Allah" Ya mike ya koma kujeran da suke ya xauna gefen Heedayah yana kallonta yace "How are you Heedayah" Ta wara ido tace "Fine, me yasa baka xo ba jiya har da shekaranjiya" Yace "Ae gani na xo yanxu" Ta laluba fuskarsa tace "To ka dinga xuwa kullum ka ji?" Mami dai ta tabe baki tana harhada kayan gyaran gashinta, Junaid na murmushi yace "Mami kaka tace a maido mata da Heedayah" Mami na kallonsa kafin tace komai ya kara da cewa "She wants her to be staying with her, bata ji dadin xuwa da kika yi kika dauketa ba daxu" Mami ta rike ha6a tace "Tohhh, ikon Allah" Junaid yace "Yess allow her ta koma wajen ta Mami, since ita ta bukata" Mami tace "Toh ai naga kamar wani nauyin Heedayah xata xame mata, baxata iya da tsirfan Heedayah ba" Junaid tace "Tunda ita ke son hakan ki bar mata kawai Mami" Mami tace "kai yaushe ta gaya maka haka?" Yace "Yanxu, har da kukan ta" Mami ta bude ido tace "Ahh to dauketa ka kai mata ita" Heedayah dake jin su tace "Mami wajen kaka xai kai ni?" Mami tace "Ehh" Heedayah tace "Amma xan dawo koh?" Mami tace "Ehh xa ki dawo" Junaid ya mike ya kama hannunta suka fita parlon, Mami ta bi su da kallo.... Mumy dake xaune parlor kamar dai ko da yaushe ta bi su da kallon gefen ido har suka wuce dakin kaka, Kaka na ganin Heedayah ta washe baki tace "Deedayah, ga kaza Junaidu ya kawo min, ai kin iya cin kai da kafar kaza koh?" Heedayah tace "A'a ni lap na iya ci" Kaka ta kalli Junaid tace "Meye lam kuma?" Yyi yar dariya yace "Cinya" Kaka ta kalli Heedayah da sauri tace "To sai ki kwata ai, ka ji min dai" Ya xaunar da ita gefen kaka yace "Kaka xan je Masallaci in dawo" Kaka tace "Toh yi maxa gashi can an fara kira" a hankali Heedayah tace "Are you coming back?" Ya juya yana kallonta yace "Yess" Yana fadin haka ya juya ya fita, Kaka tace "Toh ko wnn lafiyayyen turancin da kike ai ya ci kowa ma ya san ba daga gidan gantalallu kika fito ba, da kyar idan baki fi Shureen iya turancin ba don ni tunda nake ban ta6a jin ma yyi turancin ba, ga dai makaranta me tsada uban ya sa shi yana karami amma bai jin turanci, ko wnn kwam din da kowa ya sani baya ji" Heedayah ta kyalkyale da dariya tace "Kaka to sai in dinga koya masa mana" Kaka tace "Atoh, bari dai Allah ya shigo da shi mu ga ko xai yadda" Heedayah tace "Kaman ni yake?" Kaka tace "Ka ji ki wannan a haihuwar kaji ai yyi jika da ke, Shureen fa nace maki" Heedayah tace "Ni ban san shi ba" Kaka tace "Idan ya shigo xan Kai ki ki tattabasa ki ji" Heedayah tace "Toh" Tare Junaid ya shigo cikin gidan da Baffa, Baffa ya xauna parlor shi kuma ya shiga wajen kaka yace "Kaka Baffa ya xo" Kaka tace "Waye kuma Baffa, uban wa yace masa Ina nan, Kai ni dai gaskiya ana shiga hakkina, to me ya xo min kuma kamar dai wata yar karamar yarinya" Junaid na murmushi yace "Ya xo ne ya tabbatar nan din kika xo" Kaka ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana wllh" Bude kofar dakin aka yi sai ga Hajiya Amina da Hajiya Hauwa sun shigo da sallama, Kaka tace "Su waye wannan kuma" Hajiya Hauwa tace "Sannu kaka" Kaka tace "Yauwa, daga ina haka kamar an koro ku, ko daga anguwa ku ke?" Hajiya Amina tace "Daga gida muke kaka, mun xo biko...." Kaka tace "Yaji Maryam din ta kara yi ina gidan bani da labari??" Hajiya Hauwa tayi dariya tace "A'a kaka, kawai sai mu ka ga ba ki a gida" dai dai nan Mumy ta shigo dakin, kaka tace "Wllh na so shiga in maku sallama amma sai nayi tunanin bacci ku ke don na San ku da baccin safe, tashi nayi yau da tunanin Amadu a raina shine nace bari dai in je shi ma ya sami lada na...." Baffa ne ya shigo da sallama, kaka tace "Ikon Allah, har da kai Umaru, to me ya faru ne wai? Ba fa kai kadai na haifa ba da xanyi ta xama gidanka, shkkn kuma shi Amadu ba mutum bne da baxan dinga xuwa nasa gidan ba, Kar ka xama me son kanka mana Umaru, ka so ma d'an uwanka abinda kake so ma kanka, shima ka barsa ya dinga samun ladan uwarsa" Baffa yace "Nayi tunanin ko an 6ata maki rai ne ai Baaba" Da sauri kaka tace "Aa wllh, baku ta6a min komai ba, idan nace ma kun mun sai Allah ya kamani, matan ka ai mutanen kirki ne tun ma ba Mai jidda ba, tamkar ynda xa su yi ma iyayen su suke min, to sae in masu sharri ince sun min wani abu?? Aa kawai ni dai na xo gidan Amadu ne shi ma ya samu lada...." Kallonta kawai junaid yake with surprise, Mumy da hawaye ya cika idonta tace "Amma fa kaka cewa kika yi kwai suka soya maki duk karni sannan basa baki abinci da wuri kawai sun gaji da ke ne...." Kaka ta saki salati tace "Yau naga abinda ya isheni jama'a, Maryam ke da wa ku ka yi haka??? Lalacewar ta ki ta kai haka bani da labari? To ke ina ruwanki ko danyen kwai suka kawo min, ba gwara su sun kawo min kwan duk karni ba, ke me barina da yunwa fa??" Baffa yace "Toh kaka tunda dai bbu wani matsala shkkn sai dai mun yi waya" Kaka tace "Bbu ko wani matsala Umaru Allah yyi ma kai da matanka albarka..." Baffa ya amsa da Ameen ya fita....Mumy dai hawaye ya ki tsaya mata, Hajiya Hauwa sai danne dariyar ta take, daga karshe ita ma tayi ma Kaka sallama ta fita haka ma Hajiya Amina, Mumy ta bi bayansu xuciyarta na tafarfasa, Junaid dai kansa na kasa, kaka tace "Ka ji min mata dai xata min sharri da rai na" Tuwo da miyar egusi Sajida ta kawo ma kaka, Kaka tace "To ba gwara ke ba kan wannan mata da Rakiya ta dauka aiki duk wari.... Tafi ki kawo min flet da cokali" Mai aikin ta fita sae gashi ta dawo, Kaka ta amsa ta bude warmer din tuwon ta diba, ta ajiye ma Junaid, Junaid yace "Kaka ni fa a koshe nake" Kaka tace "Aa ni ba ruwana gashi nan ka ci, kana da Inda xaka je ka ci abinci ne da ya fi nan...." Ta kalli Heedayah tace "In xuba maki kema" Heedayah tace "Na koshi" Kaka tace "To wlh baxan baki Kai da kafar Kazan ba ma" Heedayah ta mike xaune kamar xata yi kuka tace "Toh in ci da Yaya" Kaka ta kalli junaid, Tashi yyi ya koma kusa da ita da plate din tuwon yace "Toh mu ci" Kaka ta ta6e baki tana xuba nata, Heedayah ta d'an fincili tuwon bayan ta laluba plate din ta kai baki, Kaka tace "Wllh haramta maka tuwon xata yi, meye kuma na mintsilin tuwo kamar kaza??" Dariya junaid yyi ya deba a cokali kadan ya tabbatar ya huce sannan ya kai bakin Heedayah, Jin cokali a lips dinta ta bude bakin ta amshi tuwon, a haka suka dinga cin tuwon, aka bude kofa sai ga Shuraim ya shigo, kaka tace "Shureen wai xaka dinga koyon turanci gun Deedayah" Shuraim ya kalli Heedayah da ta tankwashe kafa a gaban Junaid, ajiye ledan hannunsa yyi nan gefe ya fita dakin, kaka ta kalli Junaid tace "Kila kunya ya ji, da ban masa magana a gabanka ba" Dariya sosai Junaid yyi... Sai kusan karfe tara yayi ma Kaka sallama Heedayah har da kukanta wai xata bi sa, ya samu dai ya lallabata ya fita, Kaka tayi tagumi tace "Toh wai a gidan ubanwa kika ta6a sanin Junaidun idan ba gulma ba?? Sai kace shine Amadu? Ai ni da Amadu ne dolen ki..." Wajen karfe sha daya Mami ta shigo da eye drops din Heedayah, Kaka da har ta kashe wuta tace "Kinga Rakiya, abinda xai faru ba sai kin dinga ba kanki wahalan shigo mana tsakar dare ba mun fara bacci, kawai ki nuna min ynda xan dinga sa mata a idon, Amadu fa ya fi awa daya a dakin nan sannan ya fita, tun daxu ya kamata ki xo ai, ni na xata kin gaji kin kwanta ne" Mami tace "Aa ban kwanta ba" kaka tace "To nuna min ynda abun yake in dinga yi mata da kai na" Mami ta nuna ma kaka ta tabbatar ta gane din tana kuma tsaye ta diga ma Heedayah dake bacci drops din dare sannan tayi masu sai da safe ta fita... Har kaka ta kashe wuta aka sake bude kofa, Mumy ce ta shigo kaka ta kunna wuta tace "Amma dai bakwa tsoron Allah matan gidan nan, bakin cikin baccin ake mani cikin daren ma" Mumy tace "Yi hakuri kaka, naga baki bacci da wuri ne ban san kin kwanta ba, kankana na yanka ma Barrister shine na dibar maki" kaka tace "Ki sa min a firiji, amma wnn ae shiga hakki ne, meye kuma kankana tsakar dare jama'ah kamar ana yunwa" Mumy ta bude fridge dake dakin ta ajiye tana kallon eye drops dake ajiye saman fridge din, lkci daya ta kwashe su tace "Toh sae da safe kaka" bata jira cewarta ba ta fice daga dakin, kaka ta ja tsaki ta kashe switch din wutan.... Har wani murmushi Mumy take ta wuce dakinta da sauri, bandaki ta shiga da wayarta ta doka ma Sadiya kira, Sadiya na dagawa tace "Toh ga dai eye drops din na samo Sadiya... Kin yarda Allah na tare da ni?? Wllh cikin ruwan sanyi na samu, ban ta6a xaton hka ba...."




Heedayah isn't free, do not read for free, subscribe and read happily....

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....




Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very affordable.... 😍


Hajiya Sadiya dake sauraren Mumy tace "To kin dauko cikin ruwan sanyi maidawan fa Maryam?" Mumy tace "Aa ni maidawan ba wani damuwa ta bace, minti nawa ne, abinda dai ba makulli take sa wa a dakin ba...." Sadiya tace "Toh shkkn, amma wajen bude maganin kiyi ta ynda fa baxa a gane ba, a nutse xaki yi komai" Mumy tace "Toh shkkn sai mun yi waya Sadiya" Daga haka ta katse wayar ta fito, handbag dinta ta nufa ta bude ta binciko wani kwalba irin na magani dake karkashin jakar ta ciro sannan ta rufe jakar, kokarin bude eye drop din ta dinga yi amma ta kasa, tayi tayi amma ya ki buduwa, wuka ne ya fado mata ta Kalli agogo taga sha biyu saura, ta d'an yi murmushi ta ajiye drops din a drawer ta nufi saman gado ta kwanta tana jiran karfe daya yyi don wnn lkcn ta tabbatar kowa na gidan yyi bacci, tana ta kwance idonta kyar ko digon bacci bbu har agogo yyi struck din karfe daya dai dai, ta mike a hankali ta saka hijab dinta har kasa sannan ta dau drops din da kwalbanta ta fita daga dakin, cikin Hijabin nata ta boye hannunta me dauke da eye drops da kwalba, kitchen ta nufa direct ta kunna wutan, sannan ta juya baya ta ciro abubuwan cikin hijab dinta ta dau wuka ta fara gwada bude eye drops din a nutse, she was so careful kar saman yyi shaidar da xai sa a gane an bude, bude kofar kitchen din taji anyi, a rikice ta boye komai cikin Hijab, muryar Shuraim taji yace "Baki kwanta ba Mumy, what are you doing" kin juyowa tayi ta dinga kawar da plate da cups din karya duk a rude, amma lkci daya ta dake tace "Me ya hanaka bacci har war haka??" Yace "Shayi xan hada" Mumy ta hade rai sosai tace "Wannan shan shayin dai ya xame maka jaraba, wani shayi ne baka sha ba tun wayewar garin Allah sai tsakar dare kamar maita ka tashi wai xaka sha shayi? Shayin me? idan baka sha shayin ba mutuwa xaka yi ko me da baxaka hakura ba tunda dare yyi" Shi dai bai ce mata komai ba, har sannan hannunta daya na boye hijab dinta, ta nufi kofa a fusace ya bi ta da kallon gefen ido, cup ya dauka ya bude flask ya debi ruwan Lipton ya bude kayan shayin xai hada, Mumy tayi still ganin kaka a parlor, lkci daya gabanta yyi mugun faduwa kaka ta karaso Inda take tace "Amadu yyi bacci ne?" Cikin rawar baki Mumy tace "Lafiya Kaka, me ya faru?" Kaka tace "Ina fa lafiya, idonsa biyu ko yayi bacci?" Mumy da hankalin yyi mugun tashi don cikin d'aga murya kaka ke magana tace "Kaka ban san ko yyi bacci ba daga kitchen...." Abba ne ya fito parlon jin muryar mahaifiyar tasa, Kaka na ganinsa tace "Amadu wannan wani bala'in ka kawo wa mutane gida, ya xa a dinga shiga hakkina Ina bacci, to gata can ta hanani bacci wai shayi xata sha, meye kuma shayi kamar buxuwa tsakar daren nan" Mumy bata san lkcn da ta sauke wani bayyanannen ajiyar xuciya ba, Kaka tace "Ni dai ba ruwana, tun wayewar gari bata gama shaye shayen shayinta ba sai ynxu bayin Allah na hutawa, kawai ta cuceni ta tasheni" Abba dai bai ce mata komai ba, kaka tace "Ga ta can xaune kamar yar mage ta ki bacci wai shayi, to ni siyar da shayi nake xata tasheni ta dameni" Abba yace "Kiyi hakuri, bari a maida ta gun Rahinah" Kaka ta kallesa da sauri tace "A maida ta kuma? A kan me? To sai kayi ta maida ta din ae, daga tace xata sha shayi sai a maida ta gun Rahilah" Duk wnn abun Shuraim na tsaye rike da cup din shayinsa yana kallonsu, Mumy tace "Kiyi hakuri kaka bari in hado mata shayin yanxu" Shuraim ya karaso cikin parlon Kaka na kallonsa tace "Waye wnn kuma?" Mika mata cup din hannunsa yyi ta amsa tace "Toh ba shkkn ba dai, amma xaka wani ce a maida ta gun Rakiya, meye hadinta da Rakiya, Kuma waye bai san yaro ba Allah na tuba" Daga haka ta wuce dakinta rike da shayin, ta gefen ido Mumy ta dinga hararan Shuraim da ya juya ya wuce dakinsa shi ma, Abba ya girgixa kai ya koma bangarensa. Mumy ta tabe baki don har yau ba wani shiri take da shi ba, dakinta ta koma ta sa makulli ta ci gaba da aikinta, da kyar ta bude drops din ta wuce bandaki ta tattular da maganin ciki ta dauraye empty container din da ruwa a nutse sannan ta dawo daki, kwalbanta ta bude ta xuba content din ciki wanda kalansa shi ma fari ne a robobin eye drops din, snn ta rufe gam da murfi... Ta ajiye robobin su bushe a gaban madubi tana yi tana kallon agogo, sai biyu da kusan minti goma ta kwashe magungunan ta bude kofarta a hankali ta fito parlor, kwance ta ga mutum saman kujera yyi rub da ciki, duk da wutan parlon a kashe yake amma wutan compound ya d'an haska har cikin parlon, ta yi still a Inda take don ta san baxai wuce Shuraim ba tunda ya saba kwanciyar parlor, yawanci ma nan yake kwana, tana daga Inda take tsaye ta dinga leka fuskarsa
End Ads