x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 19 - MAZAN JIYA 2

  • 54001 words
  • 55701 words
  • Out of 55701 words

Category: Romance Story +18

Views 206

18 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
suna
tattauna, inda ya dubeta ya ce yake jarumar
315

TASKARNOVELS.COM.NG
jarumai kuma kuma sarauniyar kyawawa yq
akayi kika samu irin wannan gagarumar
jarumtaka haka ta karfin damtse alhalin a zahiri
babu wani alamun sadaukantaka a tare da ke.
Koda jin wannan tambaya sai Gimbiya Rahila
tayi murmushi tace inda zamu kwana uku ina
baka labarin yadda aka yi na samu
sadaukantaka ta lokaci ba zai ishemu ba har na
gama baka labarin, amman gaba idan muna raye
kuma da dama zan baka labarin, yanzu sai ku
tashi mu cigaba da tafiya domin mu riski rukuni
na biyu dana uku na wannan mugayen aljanu
mu gama da su sannan mu shiga manyan
dazuzzukan guda biyar wadanda daga su sai
kogon darul ikisina.
Sa'adda Rahila ta zo nan a zancenta sai boka
Muzafar ya dubeta ya ce haba yake jarumar
jarumai shin bakya ganin gabadayanmu babu
mai kwarin jiki a jikinmu face wadanda
tsautsayin bai rutsa da su ba, ke kadaice mai
cikakken lafiya a cikin wadannan jaruman
wannan tafiya, ai dole ne mu zauna anan muyi
jinyar jikinmu koda tsawon kwana biyu ne
kuwa.

316

TASKARNOVELS.COM.NG
Lokacin da boka Muzafar ya zo nan a jawabinsa,
sai sarki Lafaru dake daf da shi ya ji hankalinsa
ya tashi, ya ji kamar ya fashe da kuka. Cikin
tsananin ya dubi Muzafar ya ce ya kai babban
boka shin mantane cewa ka ce dole ne na auri
Gimbiya Ramlatus siyam a cikin kwanaki da
baza su haura sittin ba, dan kuwa har muna bata
lokaci a cikin wannan tafiya haka to gabadaya
shirinmu zai wargaje.
Koda jin haka sai boka Muzafar ya daka wa
Lafaru tsawa ya ce ya kai wannan sarki kayi sani
cewa halin da muke ciki yanzu ba na tunanin
yadda burinmu zai cika bane, muna kan tunanin
yadda zamu tsira da rayuwarmu ne.
Sarki Lafaru ya dubi boka Muzafar a fusace ya ce
wace irin magaana kake haka, ai rai ba a bakin
komai yake ba muddin akwai biyan bukata.
Boka Muzafar ya sake fusata ya daka wa Lafaru
tsawa a karo na biyu ya ce idan kai baka damu
da rayuwarka ba, mu mun damu da tamu.
Saboda haka idan zaka iya sai ka kama hanya
kayi tafiyarka kai kadai, na fuskanci ka manta da
cewa idan buri y cika babu rai sam bashi da
wani amfani.
317

TASKARNOVELS.COM.NG
Koda gama fadin haka sai boka Muzafar ya
koma gefe daya ya kishingida yana mai duban
raunin dake jikinsa, shi kuwa sarki Lafaru sai ya
matsa daf da gimbiya Rahila ya dubeta y ce Ya
ke jarumar jarumai me zai hana ki zo mu cigaba
da wannan tafiyar biyu rak, dan na fuskanci
cewar ke kadai ma zaki iya maganin dukkan
wasu masifun dake kan hanya.
Da jin wannan batu sai Gimbiya Rahila ta dubi
Lafaru cikin tsananin fushi ta ce indai haka kake
tunani to ka yaudari kanka, ina tabbatar maka
da cewa idan har muka kuskura muka shiga
wadannan dazuzzuka guda biyar babu jaruman
can to sai mun halaka, domin ko wanne daji
akwai jarumin da zai iya ceton rayuwarmu,
dukkansu can da kake gani kowa da irin tasa
baiwar da kuma sadaukantarsa, gama fadin
hakan keda wuya sai Rahila ta je ta zauna nesa
kadan da kowa, sannan ta kwanta domin ta
huce gajiyar da ke jikinta.
Wannan shine abinda ya faru ga su sarki Lafaru
bayan sun tattaro abokan tafiyarsu sun nufi
kogon darul ikisina.

318

TASKARNOVELS.COM.NG

Acan birnin Kufa kuwa a ranar da kwanaki
arba'in suka cika, tunda duku-dukun safiya aka
hango dakarun sarki Nurwas sun durfafo,
saboda yawan rundunar idan mutum ya
hangosu daga nesa sai yayi zaton cewa sun
tokare da sararin samaniya, saboda ba a iya
hango karshensu, karar kofaton dawakansu da
rakumansu kuwa ya cika kunnunwan mutane
har ta kai cewa sun haddasa karamar girgizar
kasa, ya zamana cewa gabadaya gidajen birnin
Kufa sun kama girgiza kamar zasu ruguje. A
lokacin da wannan al'amari ke faruwa sharlis na
cikin bangarenta da danta Shaddadu a zaune
tana koya masa yadda ake fada da takobi. Koda
taji sukuwar dawakan abokan gaba sun durfafo
birnin sai ta yi sauri ta shiga daki ta cire tufafin
jikinta ta saka fararen sulke sannan ta saka
wasu siraran takubba a kugunta na hagu da
dama, kuma ta saka hular karfe sannan ta saka
wasu dogayen takalma na fata iya gwiywa,
hakika shigar da Sharlis ta yi ba karamin kyau ta
yi ba, kuma ta yi kwarjini ainun. Da fitowarta
daga cikin dakin sai kawai ta dauki danta
Shaddadu ta goyashi ta daure tamau a bayanta,
kawai sai ta ji Shaddad ya ce da ita Ya ke
319

TASKARNOVELS.COM.NG
Ummata ya zaki tafi da ni yaki ban dauki
takobina ba.
Koda jin haka sai sharlis ta yi murmushi ta ce
kada ka damu ya kai dana lokacin fara naka
yakin bai yi ba, yanzu dai in so kaga yadda nake
nawa yakin ne dan ka koya. Tana gama fadin
hakan sai ta fice da sauri ta nufi bangaren Sarki
Lafaru, ga dakaru tsaitsaye a bangaren sarki
Lafaru amman babu wanda yaga Sharlis da
danta har ta isa can cikin turakar tasa. Da isarta
sai kawai ta yi arba da Sarki Lafaru a tsaye yana
shirin fita yaki har ya daura damara ya soka
takobinsa, al'amarin da yayi matukar baiwa
Sharlis mamaki kenan.
Koda Sarki Lafaru yaga sharlis tsulum a gabansa
sai ya ja da baya a tsorace ya cw da ita Mene ne
kuma ya kawoki wajena tare da danki?
Da jin wannan tambaya sai sharlis ta yi
murmushi sannan ta ce Na fito ne domin taya ku
yaki, ka sani cewa idan aka rushe daularka an
cuceni dan haka bazan samu damar daukar
fansa akan ka ba, sabida haka dole ne na bada
tawa gudummawar a wannan yaki domin kare
wannan birni. Sharlis ta sake duban sarki Lafaru
320

TASKARNOVELS.COM.NG
cikin mamaki ta ce Yanzu kai saboda me kake
shirin fita yaki, alhalin kasan cewa na cire maka
dukkanin karfin damtsenka tun daga ranar da
ka sadu da ni?
Sarki Lafaru yayi murmushi ya ce Ai abin kunyq
ne a gareni ina sarki amman ace yau gashi an zo
yaki kasata na buya ban fito ba, gwara na fito
koda kuwa za a yi mani kwab daya ne na mutu.
Sa'adda Sharlis ta ji wannan batu sai ta bushe da
dariya sannan ta ce ai indai abin kunya ne ka
gamu da shi, sai nan gaba ma idan dana shaddar
ya girma ya zama gawurtaccen sadauki da babu
kamarsa, sannan ne zaka wulakanta
mutuncinka ya zube, kimarka ta watse, duk
dukiyarka ta salwanta, sannan a karshe ka rasa
mulkinka da rayuwarka bayan dana yayi maka
kisan gilla irin wanda kayi wa kakanni na da
iyayena, lokacin da Sharlis ta zo nan a zancenta
sai kawai taga sarki Lafaru ya takarkare ya
bushe da mahaukaciyar dariya sannan ya ce Ni
kuwa zanga yadda dana na cikina zai zamo
abokin gabana har ya kasheni.
Da jin haka sai Shaddad da ke goye a bayan
sharlis ya leko sannan ya dubi sarki Lafaru ya ce
321

TASKARNOVELS.COM.NG
Ya kai abbana tabbatas zakaga yadda zan
wualakanta ka a duniya, na tarwatsa kwanciyar
hankalinka da dukiytarka, sannan da sannu na
zama sanadin ajalinka.
Da jin haka sai Lafaru ya sake bushewa da
dariya a karo na biyu, haka yayita wannan
mahaukaciyar dariyar kamar ba zai daina ba,
al'amari da yayi matukar baiwa Sharlis mamaki
kenan ta fara zancen zuci ta ce "Anya kuwa
wannan sarki Lafaru ne wanda na sani, a sanina
tun daga ranar dana cire wa sarki Lafaru
Sadaukantakarsa yake tsorona kuma ya tsorata
da lamarina, shin mene ne yasa yanzu ya daina
shakkata har ma yake magana cikin gadara, ya
zama dole a gareni bayan na gama wannan yaki
nayi bincike a cikin hallarar tsafina na gano ko
shine Lafaru na gaskiya.

Marubucin yace wane bangare ne zai samu
nasara a wannan azababben yaki da za'a fafata
tsakanin mutanen sarki Nurwas da mutanen
Sarki Lafaru?

322

TASKARNOVELS.COM.NG
Shin idan sharlis ta yi bincike a cikin hallarar
tsafinta zata gano cewa Lafaru dake tare da ita
ba na gaskiya ba ne, idan ta gano hakan wane
irin mataki zata dauka?

Wace irin bakar wahala su boka Muzafar zasu
sha a cikin wannan doguwar tafiyar dake
gabansu ta zuwa kogon darul ikisina?

Su waye zasu rasa rayukansu a tafiyar?

Shin aljani Maraful Dauwas zai amince da
bukatar su sarki Lafaru?

Shin sarki Lafaru zai samu mallakar Gimbiya
Ramlatus siyam har ya aureta?

Shin Gimbiya Rahila zata cika burinta na samun
daukaka da matsayin da take nema?
323

TASKARNOVELS.COM.NG

Marubucin ya ce mu hadu a Littafin Mazan jiya
na Uku dan jin karshen hikayar Jarumi
Shaddadu da kuma hikayar Sadauki Hulkas na
birnin Romaniya.

Daga mai debe maku kewa a kullum da koda
yaushe
Abdulaziz Sani Madakin Gini.

324


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels
End Ads