lokaci ɗaya ta buga ƙara sakawa tayi kamshin da bakin ta yake lokacin da tayi mafarkin wannan mutumin yana taɓa mata jiki..
ba shiri ta jefar dashi tare da zunduma ihu da sauri ya shigo kuka ta saki tace '' wallahi aljanin nan da yaka taɓa ni indan dare yayi shi ya ajiye wannan mouthspray din kamshin da baki na yake yi lokacin da lips dina ya kumbura shi wannan yake yi..,
kallon kasa yayi har ya fashe rasa ma me zai ce mata yayi dan haka ya kamo hannun ta suka fito danka mata bowl yayi yace '' jeki ki shirya idan lokaci yayi sai mu tafi..,
ɗaukan hijabin ta , tayi ta zura ta fita.
cin karo tayi da uncle Mukhtar shi da ya saif da kallo ya bita, gaishe shi tayi cikin kulawa ya amsa mata gaisuwar ta , tare da cewa daughter me ya faru naga fuskar ki duk hawaye..?
kwabe fuska ta ƙara yi tace " bugewa nayi shi ne abincin ya zubu yaya yayi min faɗa...,'"
tsintar kan'ta tayi da yin wannan karyar saboda baza ta iya faɗa mai me ya faru ba..
gaskiya yaya be kyauta ba sannu kin ji ya faɗa yana shiga cikin mota saif ya zagaya mazaunin driver ya zauna da yake dukkan wata dukiyar sa saif ne akai..
dan haka duk inda za su tare suke zuwa key yayi wa motar yana cewa ashe meeting yaya ya zo yi garin nan n nayi mamaki be dade da zuwa ba kuma again ya ƙara dawowa..
Dad wallahi ina tausayin yaya ba ruwan sa abubuwa sun mai yawa ta ko ina harin rayuwar sa ake yi kwanaki fa ankak mai hari akan wata Shari'a da yayi ta ɗan gidan Alhaji Ibrahim me kudi dan sa farid da yayi rep din wata yarinya me tallah so su kayi su kashe shi kasan HARIS Jami'in tsaro ne shi yake bani labari ashe dadewar nan da yayi a austria ba hutu yake ba , neman lafiyar sa yake kasan poison aka saka mai a gurin taron ƙarawa juna sani na kungiyar lauyoyi ta duniya kubace me hatsari shaƙar ta yayi yanzu haka yana kan magani ne naji yace kamar ta taɓa mai hunhu..
idon sane yayi red colour yace '' saif ya isa na tambaye ka ni me ya shafe ni da wannan labarin nan naka..?,
juyowa saif yayi yace "amma Dad, he's your son you shouldn’t say something like that about someone who concerns you directly. That statement isn’t right...,
ambassador Mukhtar yace " "Saif, I swear, if you don’t quit saying that to me, you’ll seriously piss me off..,
kai hakuri Insha'Allahu bazan kara ba..
ya fada yana fara tafiya a hankali..
Wannan kenan
Jahar Adamawa.
*BINYERI GUNDUMAR MAYO-BELWA*
duka ta saka mai baya tana cewa wai kai baka jine tun dazu naka ce maka ga a inda zaka sauke ni amma shine kai kunnan uwar shegu ko..?,
mai mashin din faka mashin din sa yayi sauka tayi tare da sauke buhunta kwance habar zaninta, tayi ya ciro wata matacciyar naira dari da hamsin tace '' ungo karbi sauri nake ina jin ba haya..,
wani kallo yayi mata tsaki taja ta zura mai aljihu cikin masifa tace ''' ya zaka tsaya kana kallo na kamar ka samu matar ka to Allah ya isa ka kalli haramun..,
wullama taya yayi yana cewa bana son rainin hankali nayi miki kama da wanda za ki bawa wannan kudin..? na dauko ki tun daga kasuwa shine don rashin mutunci zaki dauki wannan ki bani bana so kije Allah ya isa daman na lura ki tsohuwar banza ce...,
cire mayafin'ta tayi tace "' kan bala'i lallai ka taɓo tsuliyar dodo har ni zakai wa Allah ya isa to dan Allah idan ka gamu da wani a hanya kace wacece inna magajiyar karuwai..,"
Kedai baki ji dadin halin ki ba Wallahi.
aehiriri ta saki wata uwar buda tare da durkuwa ta dauki kudin ta tace "' wa ai kayan Allah ya isa yafi dad'i wallahi ni gaba ta kai ni yaro bara na faɗa maka idan ina. Cin kayan Allah ya isa wani dad'i nake ji domin da be isa ba , ba zai yi uwar ka ba dan durun uwa ware ko yanzu na saka a yi gunduwa dakai sa'arka ɗaya yanzu ba da bane da yasin na zuke maka jini to yanzu na karbi Musulunci amma da nanu maka ni jinin ƙabilar *CHAMBA ce* "
jan mashin din sa yayi yana mata Allah ya isa ganin tana kokari dauko huka a kugunta..
shiga cikin gidab tayi dore da jakar babko dinta saukewa tayi tana cewa ina yan iskan gidan nan suke..to wallahi ga kaya nan na kawo na shaɗana amma kudi hannu sai da na zabi giredi sannan na saro..
wacce take zaune akan kujera tana duba fuskar'ta, ta ajiye mudubin hannun ta , tace '' mu gani..,
da sauri ta rarumi jakarta tace "' lah lah ban faɗa miki ba amma jeki ki gayyato yan uwan ki..,"
ke wallahi baki da yarda ki bari na gani mana sai kace zanci ba kowa a cikin gidan duk sun tafi nema nima yanzu zan tafi..
Oh to gani dubu ɗaya ɗagawa a gwada dubu biyu sakawa ana neman zaɓi dubu uku...
kai jama'a wai dan Allah inna ina zaki kai kudi ne haba ni ban taɓa ganin wannan lukutar masifar ba wallahi..
taikun ubanki ta faɗa rarumar jakar ta a guje jujal ya shigo yana shiga bayi.
da sauri ta suri jakar ta , tana shiga uwar daki tare da rufo kofa daga labule tayi wani dogon tsaki tayi ta fito tana cewa malam lafiya baka san nan gidan matan aure bane...?
Hajiya kiyi hakuri na sani danki jujal anyi kittifakin duk wata dabba da take area nan shi ke sace ta jiya ya sace wani katon zakara..shine aka kawo karar sa..
kuttumar ubancan kai jaburu fito fito ashe yanzu ka fara ha'inta, ta ban sani ba..
dan kato dagora yace '' wallahi hajiya sai addu'a lamarin ya'yen nan kiyi hakuri karki yi mai baki dane ka haifa amma baka haifi halin ka ba..,
jaburu da yake leƙowa yana sanda yace '' na fito ba zaki danka ni gurin sa ba ko..?,
kai wannan kai ta shafa akwai wani dan durin uwar da ya isa ya zo cikin gidana ya daukar min yaro na fito wannan case din da nake dakai daban ne..,
ta fada tana kwance damarar da tayi mamaki ne ya kama dan kato da gora Allah me iko ya kasa fahimtar ina zancen ta ya dosa.
fitowa yayi yana cewa gani nan..
kai dan kwal ubanka ashe jiya ka kama katon zakara shine ko yanka daya ka bani inma siyarwa kayi ai ka bani ladan ganin ido..
zaro ido dan kato da gora yayi yana cewa Hajiya zakaran sata ne fa..
yatsuna fuska tayi tace '' ni na sata..?,
ta fada tana zaro ido..
fita yayi yana cewa a wannan tafiyar sai na dauko bataliya da uwar da danta duk halin su ɗaya..
dariya inna tayi ana cewa Wallahi jaburu kaban mamaki wannan abin kamar lagwani zaka gudarwa me makon ka tafasa mai jiki da duka ko yasan ruwa ba sa'an kwando bane ba..
uhmmm wallahi inna wannan da kike gani yasin yakai ni gurin su na shiga uku sai sun fasa min fatar jiki da duka..
Mtssww yar uwar ka jawa ita , ta gado halina wallahi kai kaga nan namiji amma ba kamar ba namiji ba tur da halika tun kafin na daga maka nono ka fito min da kudin da kasiyar da zakaran nan..
kai inna gaskiya na siya kaya dasu yanzu ba ko sisi ya faɗa yana fito mata da aljuhun sa..
jaburu bazan fa yarda ba sai ka fito min da kudi kai din duk wata hanyar cuta ka santa dan haka fito min dashi ko yanzu wallahi ranka ya ɓaci......
KARUWAN CIKIN GIDA
Ga channel dina kuyi min subscribe Dan Allah wai ina masoya na suke.
https://www.youtube.com/@nasreenminallah
https://vm.tiktok.com/ZSBRtRQmN/
Domin samun update kuyi following dina
Book ¹
EPISODE ¹⁸
Haba inna zan miki karya ne nace miki babu su lamma ne suka ce muci abinci da kuɗin.....
tashi tayi ta tsaye tana cewa shikkenan ka cuce ni jaburu me makwan ka kawo ko sululu (taliya ) ne na dafa mana muci kasan mahaifin ku baya cas baya as sai fakewa da yake a kofar gida da suna malimta ba tafiya nema shi kuma ba zai iya bugun kasa ba wai a cewar sa haramin ne shi ya zauna inda Allah ya ajiye shi,
Raliya da ta sheka uwar kwalla ta fito tace '' to na tafi karki bawa , wani dakina zan dawo..,
to masha Allahu bani kudin kwanan yau da kika yi.. ta faɗa tana me ko mata hannu
Raliya tace '' haba INNA wallahi kinsan ba wanda yazo jiya bani da kudi ki bari idan na dawo nayi miki balance..,
tab lallai baki da hankali a'a uwar balance za kiyi min ba balance ba maza jaburu fito mata da kayan ta.
waje zuwa anjima nasan wani zai zo ya kama..
shigowa malam yayi da buta a hannun sa da alama alwala ya zo yayi domin an kusan kiran sallar la'asar idan ya daura alwala zai zauna ya yi karatu kafin lokacin sallah yayi jin abin da take faɗi yace '' wai fauziyya ban hanaki tara min mutanen banza a cikin gidana ba...?,
wani kallo tayi mai tare da cewa ke raliya zo ki fice karki dawo min idan ba kudi kika zo da shi ba yauwa haɗa har da kayan ki..
ganin bata kula shi ba ya debi ruwa abuta ya shiga bayi yana nema mata shiriya a zuciyar'sa.
Raliya tace '' inna dan girman Allah kiyi min afuwa wallahi jiya na wanda na kwana dashi ke kanki sheda ce..,
wani uban salati ta saki tana tafa hannaye tace '' uhmm fito fili kice ina zargina ina yi muku laɓe..,
wani numfashi ta saki ta buɗe jakar ta. ta ciro dubu ɗaya tace '' gashi nan wallahi da ita , na tashi sai ki riƙe zan ciko miki dari biyar..,
amsa tayi tana juyawa alamar ta raina tace '' ke wai ban tara ku ba na faɗa muku na kara kuɗin dakunan gidan nan to shinkafa ma ta ƙara tashi da sauran kayan masarufi dole nima na ƙara farashin kwana a cikin gidan nan duk ƙaruwar da taga zata iya to , ta lalemin kuɗi ta bani kalas....
to shikkenan Insha'Allahu zan ciko nawa ne..?
kwana ya koma dubu biyu..
okay ashe ma ba tsaɗa ta fada tana fita zama tayi tana cewa jaburu naji ɗazu kana cewa yar uwar ka , ta bugo ko..?
ciro wata matacciyar waya yayi yana cire batirin cikin ta , tare da sakawa a baki ya mai da yace '' eh ta bugo na ma bata shawara ba sai kin kirawo ta ba..,
fisgar wayar tayi tace '' da yake kai ka haifa min ita ai dole kace ka bata shawara matsa min daga gurin nan ko yanzu na bajeka a gurin nan..,
matsa mata yayi yana fita waje..
number jawa ta lalubo ta dannawa kira sai dai a kashe taji wayar tsaki taja tana ajiye wayar a kan taga fito da kayan da ta siyo tayi tana ɗagawa tana ajiye wa.
★★★★★
kuka sosai tane Hajiya zuba mata ido tayi ta kasa cewa komai kwantar da kan'ta tayi a kan cinyar Hajiya tace '' wallahi bana son komawa Hajiya ke baki ga abin da suke ba ko kunya ta basa yi musamman ma jawaher shi kuma yaya ya dinga biye mata.
dan murmushi tayi ta matsar da kalbar da ta rudewa Najlah fuska tace '' ban da abin ki najlah matar sa ce fa me ruwan ki da wannan, wannan ba dalili bane ba me ya saka bakya son zama a gurin yayan ki..?,
shiru tayi ta turo baki Hajiya tace '' maza tashi ki shirya biyu da arba'in..,
ƙasa koda motsi tayi hajiya sai da tayi mata jan ido sannan ta , tashi gaba ki ɗaya kayan ta , ta haɗa mata driver ya zo ya ɗauka jawad sai da yabi ko ina na cikin gidan yayi musu sallama sannan ya shigo saminta yayi ta zuba ta gumi fuskar nan duk hawaye ta kasa riƙe su, mene dalilin da najlah ke gudun sane..? ya tambayi kansa bashi da me bashi amsar nan dan haka dole ya kawar da ita sallama yayi ɗago kan'ta tayi a razane tamkar taga wani dodo batare da ta amsa ba hajiya da take cikin daki ta fito tana cewa najlah maza tashi ku tafi kin dai san jirgi baya jira Allah ya kiyaye hanya..
tashi tayi fuskar'ta duk ta kumbura kallon ta yayi yace '' a haka zamu tafi ki saka mutane su dinga kallon mu maza jeki ki wanke fuskar ki ,
Hajiya tace '' kyale ta Jawad neman hanyar labewa take karta jawo maka asara ita ba abin da ya dame ta ..,
to yace addu'a tayi musu yace amin har gurin mota ta rako su shiga najlah tayi tana sauke ajiyar zuciya shima shiga yayi direba ya ja su .
suna zuwa airport checking akai musu lokaci yanayi suka hau najlah da take farko shi kuma yaka ciki tun da suka shigo wani matashi yake kallon ta lura da haka Jawad yayi ya kalle ta yace '' tashi dawo nan..,
batai musu ba , ta dawo jawad ya zauna yana aika mai da kallon banza dauke kai yayi, zaman jirgin ne ya addabi jawad domin lokaci bayan lokaci yana kallon matashin nan still idon sa nakan najlah.
ji yayi kamar ya shaƙe shi ya huta ya saba biyan first class amma a wannan dawowar da za suyi kawai sai ya biya normal set ashe rabon ran'sa ya ɓaci ne..
suna sauka ya kamo hannun najlah suka fito suna ƙoƙarin barin reception din ya gamu da wani abokin sa tsayawa da suka yi suna magana matashin nan ya tawo gub najlah da take zaune tana danna wayar'ta sallama yayi mata ɗagowa tayi tana amsawa domin ta zata irin me tambayar nan ne..
wayar sa ya miƙo mata yace '' dan Allah ki samin number ki.. wallahi tun da kuka shigo nake kallon ki dan ma yayan ki kamar baya so nayi miki magana..,
juya kan'ta da za tayi suka hada ido da jawad da sauri ta , tashu tsaye tare da barin gurin tunowa tayi da lokacin da jawad ya kusan ballanta akan wani yayi mata magana yaushe zata ƙara yadda ayi na biyu..
jawad sallama suka yi da abokin nasa lokacin najlah ta zo kama hannun ta yayi suka soma tafiya ganin be mata magana ba hankalin ta ya kwanta.
har suka shiga mota bece mata komai ba.
sai ma mai da hankalin sa yayi kan waya da alama abu me mahimmanci yake yi horn suka yi masu gadi suka wanga le gate din gidan.
turo hancin motar su direve yayi Najlah tabi motar yan sanda da tagani a cikin gidan da kallo tana mamakin me ya kawo yan sanda ko ya canza ma'aikatan gidan daga sojoji ya kawo yan sanda ne.
bata da me bata amsa haka ta buɗe murfin mota, ta fito shima fitowa yayi be bari an bude mai ba ma'aikatan gidan da sukai jigum jigum suka karaso gurin ubangidan nasu, suna gaisheni sa Alhaji Barka da zuwa ka dawo lafiya..
Barka dai ma same ku lafiya..?
ya faɗa yana yiwa najlah alamun ta shiga cikin gidan..
wucewa ciki tayi me gadi yace '' Alhaji wa'yannan yan sanda zuwa sukai su tafi da Hajiya shi ne muka hana su shiga ciki su kuma suka ki barin gidan sai ya fito..,
da sauri jawad ya kalle su yace '' okay ba damuwa bara naje naji me ke tafe dasu karku damu kowa ya koma bakin aikin sa kai isa shigar da kayan dake cikin boot ciki..a parlour zaka ajiye idan na zo na shigar mata dasu daki..
an gama oga suka ce suna barin gurin.
ƙarasowa gurin su yayi ya miƙa musu hannu suka gaisa ɗaya daga cikin sune ya ciro I'D card yace '' suna na jibrin abba gumel daga hukumar yan sanda an aiko mu ne daukan Hajiya domin tayi faɗa da wata har ta fasa mata kai..,
duban I'D card din sa yayi tabbas haka ne amma me ya haɗa ta da Jawaher yace '' okay ba damuwa ku koma za mu zo Insha'Allahu yanzu na dawo zuwa anjima zan zo.,
basu yi mai gardama ba kasancewar babban mutum ne idan yace a kore su daga aiki ta zauna korarsu za ayi suka ce to godiya yayi musu ya shiga cikin gidan jawaher ya tarar a zaune ta ci ka gaban ta da kayan motsa baki tana ci ta ɗora kafa ɗaya kan ɗaya sallamar da yayi ne ta janyo hankalin ta , ta juyo da sauri tare da rungume shi tana farij ciki kiss tayi mai a kuma tu tare da haɗe bakin su.
dai-dai lokacin najlah ta , fito shan ruwa domin ta duba babu a cikin fridge din dakin ta.
ƙasa ɗaga kafar ta , tayi saboda kunyar da taji ta kamata wai su wa'yannan basu da hankali ne kome ku tsabar rashin kunya ne juyawa tayi ta , koma Jawaher da ta lura da ita , saki wani malalacin murmushi kadan ta gani sai sakewa ta gagare ta a cikin gidan nan shima Jawad sarai ya ganta.
sakin juna suka yi suna aikawa da juna wani irin kallo tamkar zasu cinye junan su ji suke kamar sun yi shekara dari basu haɗu ba Jawad da ya gara jin wani irin son Jawaher yana shigar mai zuciya ji yake ba macen da takai ta komai wani irin kallo yake binta dashi kamo hannunta yayi yana cewa sweet heart kin kara kyau.. komai naki na musamman ne....
wata dariya tayi tana jifan sa da kallo ƙasa tace '' uhmm dauke ni mu shiga daki kaga irin tanadin da nayi maka..,
wani irin dad'i ne ya ziharce shi yace '' a you sure..?,
kai ta gyaɗa mai cikin wani irin salo tace '' amma a dakin kusan da najlah zan nuna maka mu shiga ciki..
be mata gardama ba domin ji yake ko me tace mai yi zai yi domin ya faranta mata shaf ya manta da maganar yan sanda balle yayi mata ita..
ajiye briefcase din sa yayi ya ɗauke ta , tamkar wata yar baby ya buɗe dakin wow komai ta gyara shi ga wani irin kamshi da yake fiddawa..
sauke ta yayi akan gado da sauri ta , tashi ta janyo