takara Shiga Ruwan zafi domin Anty madina tafadamata Shizai Taimaketa duk Ranar da Yaya captain yayi Disvargin dinta.
_________________
_Masauratar garin Agadez_
"""Da gudu Wata mota 607 kirar Piagion,baka ta shigo cikin babban kofar masarautar inda ainihin sashen matan maimartaba suke Dogaran dake waje suka Rumtuma da gudu zuwa ga motar suka mata dafifi daya daga cikinsu ne,ya bude murfin motan yana fadin"Barka da dawowa Yarima dan sarki jikan Sarki yarima mai jiran gado. "gabadayansu suka amsa sai da yabata lokaci kafin ya saka kafafunsa zuwa waje,kafar nasa sanye da wani katon takalmi booth ne baki masu igoyoyi duk ya daure su,Kafar Nasa farace sosai,takamarsa ne yasa bai Fito kai tsaye ba sai daya bata lokaci sai gashi ya fito masha Allahu daga sama har kasa na karemai kallo sanye yake da riga da wando masu Ruwan kasa baground dinsu sai ratsin green,kansa sanye da hula Shima irin kayan jikinsa kugunsa tamke da wani katon bell baki,daga gefen kafadansa Sai ga wani dan Anini daya nuna sunanshi Baro baro kamar haka.
*LIEUTENANT UMAR ABDULNASEER TAMBARI BUZU..* Kenan wanda ya kasance sojan kasa ne dayake aiki akarkashin Sojojin kasar Niger a yankin Niamey,dogon Namiji ne mai dauke da kyau da zati,Baya naja da Sauri saboda yadda naga yana kama da Aliyu gadanga sai kace wasu yan biyu saboda yadda komai nasu yazama iri daya ban tsorata ba sai daya fara taku da yanayin isarsa da takamansa komai irin na Captain Aliyu ne,dogarawan dake durkushe kasa suna zubamai kirari yadagama hannu kafin ya Shiga babbar kofar da zata sadashi da sashin Mahaifiyarsa wato GIMBIYA FASILATU.
Tunkafin ya karisa sakon isowar tilon Yaron sarkin ya cika Masarautar Duk da baifara isa Fada ba,ammh har jakadiya takaima sarki rahoton dawowar baban dan Nasa kuma magajinsa wato yarima Umar,ita kanta Gimbiya Fasilatun Tuni wata amintattaciyar baiwarta ta Shigo ta labarta mata bata ma kai ga Ficewa ba sai ga Yarima Umar din ya Shigo cikin Babban Falon na mahaifiyarsa wanda yaji kayan alatun more rayuwa,tana zaune bisa wani Tuntu na gidan Saurata gefenta wasu kunyangu ne,sunata faman mata Fifita da wani katon Faifai mai wani gashi gashi ajikinsa,yana Shigowa suka mike da hanzari kafin su sake zubewa suna fadin"Brka da zuwa yarima dan Sarki jikan sarki kuma sarki agobenmu in Allah ya yarda..!Suka hada baki Suna fada.
Fuskars babu Fara"a ko kadan ya daga musu hannu,jikinsu na rawa suka mike suka fice,dakin ya rage daga Shi sai mahaifiyarsa cikin wani taku ya isa kusa da ita yazauna kasa kusa da kafafunta yana fadin"Barka da hutawa Ranki shi dade.."ta dago tana kallonsa kafin ta sanya hannu ta dauko Tuffa cikin wani Faranti ta saka abaki ta gutsira kafin ta sanyamai baki Shima ya gutsira maidawa tayi ta ijiye tana fadin"Brka da zuwa yarima Umarun Faruq yarima mai jiran gado.."Tafada tana mai mirmishi tabe baki yayi yana Tauna Tuffan bai yi mgana ba sai da yagama hadiyewa Tukunnah yace"Nifa Ranka shidade bani son kina sanyawa ana min kirari da yarima mai jiran gado,sam ni mulki baya gabana Nafi kaunar aikina fiye da komai.."Yafada yana bata Rai.
Mirmish tamai mai kayatarwa kafin tace"Naka wasa Umar,ka manta duk sanda kayimin wannan mganar nasha fadamaka tun Wuri ma ka sanya son mulki aranka domin watan watarana kaine zaka mulkemu a wannan Masautarta ta *TAMBARI BUZU.* Saboda Maimartaba bai da wani da Namiji sai kai,sauran kannenka duka mata ne Umar,kuma ko ba mutuwa ba akwai Tsufa kuma dole masauratar nan na bukatar Adalin Sarki kamar mahaifinka kuma bakowa bane face kai.." ido ya tsuramata harta gama mganarta ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Uhm...,Mommy kenan ni duk ba wannan ba wata tafiya ce ke gabanmu next month in Allah yakaimu duk da bansa rai dani aciki ba sai gashi Sunana ya fito.
Kai tsaye ta takalleshi kafin tace"Wata Tafiya kenan? gyara zama yayi yana fadin"Gwanntin kasar Nageria ita ta kawo ziyara zuwa ga gwannatin kasarmu kuma azuwan datayi ne ta nemi hadin gwiwa da gwannatinmu domin Subata wasu daga cikin dakarun Sojojinta guda dari zuwa Nageria domin hadin gwiwar yakar yan boko haram da masu garkuwa da mutane,hadin gwiwan ta hada da cameeron da chadi,da Niger da kuma Nigeria,shine acikin wadanda za"a Tura harda bacth dinmu aciki kuma nine Shugaban tawagarmu.."Washe baki Gimbiya Fasilatu tayi tana fadin"Masha Allah wannan ai Abun alfahari ne,Allah yabada sa"a Allah yasa acimma buri,yanzu kaje kayi wanka kaci abinci ka huta nasan zuwa lokacin maimartaba ya bar fada yana Shashensa zan aika jakadiya tamaka iso sai kaje ku tattauna saboda yau bani keda Turaka ba gimbiya Razeenah ce"Gyada mata kai kawai yayi kafin ya mike ya fice yana mamakin yadda Mommysa tayi Farincikin da wannan Tafiyar wanda Shiko ko alama tafiyar bata kwantamai ba.
*Intelligent writer's Asso.*
*Janafty Aka Shakira*💇
*2019..*
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_
*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_
*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent Writers Association*✏
_Sadaukarwa ga FIKIRAR MARUBUTA..,kamar irinsu,HassanAtk,and Hussain80k mai warin baki😹😛,Sai ke my abokiyar Hassada Mrs Sardauna,Ina kike kawata Hassana Dan labarabawa,Walidition,Diyata Ladingo,Sisinah Aisha Alto,my mryam obam Rabi"atu Sbs,Sahibata Hafsart Hafnan,...Da duk jama"ar dake gidan Fikirar marubuta kusani ku kara sani Janafty na muku Son kauna mara iyaka,Ina kuke yan Group din KHADIJA CANDY NOVELS..Ina gaisuwa Salwess,Da duka sauran masu Sharhi dake cikin group din,sai ALIYU GADANGA FANS1..ina kike My Esha,dake mman Muneebata,Aisha Adris,Fatima garba,Mman Ummu(Nemecyna),Kuma yan ALIYU GADANGA FANS2,Ina kai gaisuwa Allah yabar zumunci da duka Sauran group din dasuke Sharhi kan wannan buk din,Ina godiya Sosai Allah yabar Zumunci BOHOT BOHOT LOVE_
*NOT EDITED*💥
*Chapter 21*
""Bai isa Shashen mai martaba ba sai zuwa dare bayan an idar da sallar Issha"i lokacin angama hidimar Fada Sarki ya Shiga cikin gida wajen iyalansa,Lokacin da Umar ya tarar dashi yana kishingide cikin kayatattacen Falonsa wanda yaji kayan alatun more rayuwa,Tuffa ne ahannunsa yana Ci,gefe daya kuma yana duba wani littafin Iziya,jikinsa Sanye da riga da wando,irin na gidan Sarautu,Yana ganin Umar yatashi daga kishingiden yana mikamai hannu Karisawa yayi yana mai mikamai hannun yana fadin"Barka da hutawa Ranka yadade...".
Kusa dashi ya zaunar dashi yana dafa kafadansa yace"Yauwa Umar Sanda,ya aiyukan,nasamu lbrin dawowarka Tundazu toh lokaci muna fada kasan Sha"anin mulki sai da taka Tsantsan,nima dabakazo ba,yanzu nake Shirin zuwa shashen naka.."mirmishi Umar ya saki yana kallon Fuskar mahaifinsa mafi soyuwa gareshi,kafin yace"Eh Abbah Tun dazu na Shigo nima Ban leka Fada ba,saboda gajiya ammh kasan kowani hali nake ciki Dole nazo har shashenka na isheka.."girgiza kafadansa yayi yana fadin"Hakan na dakyau,ya wajen aikin naka Fata dai komai lafiya.
Ajiyar Zuciya Umar ya sauke kafin yace"Lafiya ba lafiya ba Abbah..."kallonsa yayi idanunsa sanye da Wani Farin medicated glass mai karama Mutum karfin gani,kafin yace"Lafiya meyafaru Umar zaki.."?Kada kai yayi yana Fadin"Wlh Abbah mganar hadin gwiwar nan ne Kasar Nageria ta nemi gwannatin kasarmu data hada hannu Suyi tare,Toh acikin Sojojin, daza"a Tura Nigeria Abbah harda tawagarmu kuma nine shugaban Tawagar.."Kallonsa yake har ya dire dan mirmishi yayi mai kafin ya maida kansa gefe yana kallon wani waje Mamaki yakama Umar a ladabce,yace"lafiya Abbah ko acikin mganata akwai Abunda yabata maka rai ne?.."girgiza kai kawai maimartaba yayi kafin ya saka hannu ya zare gilashin dake idonsa kafin yace.
"Ko daya Bata batamin rai ba,saima Tuno min da wani gibi dana kasa cikewa,karka damu Umar Allah natare dakai kuma addu"ar iyaye na bibiyanka,insha Allahu zakuje lafiya ku dawo cikin Nasara.."kai tsaye Umar yace"Ammh Abbah ka taba zuwa Nageria ne,wai ina Nufin koda yawan Ran gadin gidan Sarauta ne?" Kallonsa yake kur kafin ya kauda kai yayi Shuru sai zuwa chan yace"Na taba Rayuwa A Nageria bama zuwa ba Umar.."Da mamaki Umar ke kallon mai martaba kafin ya washe baki yace"Toh Abbah wani yanki ka zauna..? Yanayin Fuskarsa sai ta chanza Jikinsa yayi sanyi yayi Shuru baiyi mgana ba,ganin haka yasa Umar Saurin cewa"Afuwan Ranka ya dade bansan Tambayata zata bata maka rai ba Allah huci Zuciyarka.."bai yi mgana ba sai ma mikewa dayayi yazura takalminsa irin na gidan Sarauta hanyar wani kofa ya nufa sai da yakai kofar dakin kafin ya harde duka hannuwansa ta baya ya waigo yana fadin"Baka Batamin ba Umar,tambayarkace ban da amsarta domin nikaina Bansan awani yanki na rayu ba balle har na dora da wani Abun,Abu daya na sani inaji ajikina cewa ada achan baya nayi Rayuwa da wasu mutane,wanda Ahalin yanzu suke bukata,ammh kuma Allah ya boyemin Abun,addu"a zaka taya mahaifinka Allah ya bayyanar da Duhu yazama haske.."Yana gama fadar haka ya Shige kofar da hanzari.
Duk da Umar bai gane ina mahaifinsa ya dosa ba,ammh yasani koma miye shi Toh Tabbas,yana da matukar amfani sai yasamu kanshi da addu"ar Allah ya bayyana koma miyeshi,bai wani jima ba ya tashi dauke da Tuffa guda daya ahannunshi,yana Shirin Ficewa sai ga gimbiya Razeenah cikin alkyabbanta zata Shigo sukaci karo,baya yaja yadan rankwafa yana fadin"Barka da Fitowa Ummah.."Mirmishi ta saki tana fadin"Yauwa Umarur Faruqu saukan yaushe ba lbri,dazu kannenka keta zencenka.."kai ya sosa yana fadin!Dazu ne Ummah,agajiye nadawo Shiyasa ban Shigo ba,Zan Shiga da Safe mu gaisa da kiddo's dina.."Gaba tayi tana fadin!Ayyah..Yakamata.."Ficewa yayi yana fadin"Afito lafiya Ummah.."Ta amsa Da Allah ya sa Umar.
____________________
_Gombe_
Su goggo sun sauka gida lafiya,goggo akafara Saukewa kafin awuce da Baba Ade gidanta cike da kayan arzikinta ta sanadin Azeema domin kawu sai da yabata 20k dakyar ma ta amsa,sai kayan Abinci wanda yabasu ita da goggo harda na mallam lawal,wanda dama akidane Duk wata in zaiyima goggo sako,toh harda nashi aciki yamaida Abun Nauyi ne wanda ya rataya awuyanshi don ko komai Mallam Lawal nada matukar Tasiri ga rayuwar kanwarshi Suwaiba da Aliyu,balle yanzu da Aliyu ke Auren diyarsa.
Sai washegari goggo ta Shiga gidansu Azeema ta kaima mallam lawal sakon kudinshi da kayan Abincin Da kawu yabada abashi,haka yaketa zubamata godiya kamar yayimata kuka,domin kudin sunzo akan gabane,kasuwa taja baya gashi babu kudi ahannunsa,toh ga budi daga Allah,Nan yake tambayar Azeema aiko goggo ta tankwashe kafa tana bashi lbrin Azeema na kaduna in ma yaganta bazai ganeta ba,Yaji dadi Sosai yayita musu addu"an zaman lafiya,inna Ramatu kuwa dakyar ta iya bude baki ta amsa gaisuwan Goggo itako ko ajikinta bata damu ba,Tadade suna hira da mallam lawal kafin tayimai sallama zata tafi dago kan dazatayi taci karo da Azeeza Inna Ramatu ta rikota zasu bayi,Goggo ta tsorata da ganin yadda Azeeza ta dawo,saboda yadda ta rame duk kibar nan dakuka sani bata,tayi baki tarame fuskarta tayi wani iri,Bakinta duk ya bushe,dakyar take Tafiya,har suka Shiga bayin,Goggo na binsu da kallo sai da suka Shigene kana goggo ta maida kallonta kan Mallam lawal tana Fadin
"Mallam lawal,nace meya samu Azeeza ne,naga duk ta kare..? kada kai yayi kafin yace!Wlh bansani ba Suwaiba tun Ranar da kuka tafi ta kwanta ciwo,daga zazzabi shikenan jiki yaki dadi,toh Rashin kudi ne yasa Ita uwar tata bata kaita asibiti ba,ammh Tunda yanzu sun samu gobe sai Su Shirya su Tafi.."Gyada kai goggo tayi kafin tace"ikon Allah,anya ko Tana cin Abinci.."?Girgiza kai Mallam lawal yayi kafin yace!gaskiya bata wani ci,koni sai na mata jan ido take iya ci kadan,bata da aiki sai kuka nayi Tambayan Duniyarnan tafadamun meke damunta taki mgana,ta tambayi mahaifiyarta itama tacemin bata sani ba.."kada kai kawai Goggo tayi tana fadin!Allah Shi kyauta..Allah kuma yayayemata Abunda ke damunta.."Da Amin ya amsa,kafin Shima yamike har waje ya rakata yanata mata godiya.
Koda Su Azeeza suka Fito daga bayi basu samu goggo ba,waje Inna Ramatu ta zaunar da Azeeza inda Mallam lawal ya tashi,Kasa zama tayi saboda bata da karfin jiki,komawa tayi takwanta tana tari,inna na mata sannu,dagowa tayi tana fadin"Inna Da Azeemar aka dawo..?"tafada cikin alamun ciwo,Tsaki Inna taja kafin tace"Mtsewww..Bansani mara zuciya koda ita akadawo ubanki zatayi miki,duk uban wulakancin dasukayi miki,aiko yacu ki kama kanki,shiko shegen yaron nan mara asali,wlh ko bayan Ran Azeema ban amince ki aure shi ba.."tafada cikin kakkausan murya kafin ta wucewarta madafi tana ta fada tana zagin Azeezar hade da Azeemar lokaci daya tana kuma tsinema goggo don tace ita tazo anguwansu ta haifan musu dan Shege yazamantomata bala"i.
Azeeza na kwance tana fitar da hawayen bakin ciki,Tunda yaya captain ya tafi da Azeema kaduna ta kwanta wannan ciwon saboda bakinciki da zafin zuciya,akullum kwanan Duniya in dare yayi bata iya barci saboda Shedan na haskomata Azeema da yaya captain kwance agado daya suna gudanar da wata rayuwa mai tsayawa arai,Zafin kishi baya barinta tayi barci ta dinga kuka kenan tana Tsinema Azeema aranta,kuma wata tsanarta na kara girma aranta,domin itace ta Shiga tsakaninta da masoyinta,wanda duk kwanan duniya dashi take kwana take tashi,sonshi bai ragu aranta ba,saima karuwa dayake.
Cije baki tayi kafin tace" _Yazama dole nayi yaki domin samun kusanci da Abun sona,Azeema kiyi hakuri zan zo gareki kuma,kuma ina Fatan wannan karan zaki afka ramina.._ take Fada tana zubar kwallah,lokaci daya tari ya sarketa daga kwance take fadin"inna Ruwa..."Inna Ramatu ta fito daga kichen ta Shiga daki sai ga ta da ruwa awani karamin kofi ta dankwafarmata dashi nan tana fadin"ai sai ki tashi kisha,ni tuni nadaina wahalar dakaina akanki,Tunda bazaki daina sakama ranki abunda ba zai yuyu ba,banda Rashin hankali kowa na gudun Shege,ammh ke kina neman kashe kanki saboda wanda ba"asan asalinshi ba.."
Tafada tana komawa madafin,daKyar Azeeza ta iya tashi ta dauki ruwan tasha kadan,Inna tabi da kallo tana dan mirmishi Aranta tanajin Haushin inna mussaman ma in ta zagi Yaya captain ji take kamar ta rama mai,itafa yadda takejin nan zata iya rabuwa dakowa aduniyar nan indai akan yaya captain,ciki ko harda inna don ta lura basuyi Tarayyah akan Abunda take so ba.
""Fadar irin Soyayyah da kulawa dake Shiga tsakanin Azeema da Aliyu kauyanci ne,domin acikin Satin nan gabadaya Azeema tagama rikita Aliyu da salon da Anty madina ta koyamata,kyautan First dinsu na Farko wayace Aliyu ya siyamata galleliya mai kyau da yarari pack4 wayar ta hadu ta karshe,yabata ne saboda Kyautatawarta gareshi,Azeema ta saki jikinta Sosai tana bin Aliyu sau da kafa,dayake ta karance shi sosai Shiyasa batasha wuyanshi ba,tana bashi girmansa daidai gwargwado.
Aliyu A adaddafe yabari Azeema ta sake kwana uku bai kara tabata ba,saboda tagama warkewa Sosai,Rana na hudu kuwa Sai da Aliyu ya maimata Abun da yayi Ranar Farko,kuka ya dingamata Share share,Bude muryansa yayi ya dinga kwararamata ihu😛😂😹Domin Azeema nakaishi wata Duniya da baitaba kawowa akwaita ba,sai gashi Ta Sanadin Azeema yaje,Itako Duk ta fahimci yana da yawan bukata bata nuna ta gaji koda ta gajin,duk sanda yazo da bukatarshi zatayi hanzarin tallafanshi ta biyamai bukatunshi,Azeema bata yarda shawarwarin madina ba kodaya don Aliyu da kanshi ya budemata whatsapp,ya sakamata nombarsa,data Anty madina dana,Anty mardiya sai ta goggo data Ummah harda ta Babanta,aiko ranar Murna kamar mene wajen Azeema,Wuni tayi kiran mutane Suna gaisawa,data kira mallam lawal sai da yayi kwallar Farinciki,goggo kuwa sai da suka kusa shafe awa suna waya,sai da Aliyu ya karbe wayan ya kashe,kana ta Saurara,Anty madina da hanzari ta sanya ta cikin groups din su na karuwa ta whatpps,dana girke girke don ta dinga karuwa.
Sau biyu Aliyu na gayyato Jabir,suna zuwa suna lonching Agidanshi,saboda yadda Azeema ke kasheshi da wasu salon girke girken,wanda ko Abu take bata gane ba,yanzu zata kira Anty madina takaramata bayani,bata da son jiki ko kadan balle kusan tasaba da aiki da gari ya waye ko kafin yaya Aliyu ya tashi ta gyara ko"ina ta tsabatace,tayimai breakfast harta cakare cikin Shigata alfarma,Aliyu bazai iya dora komai kan zamanshi da Azeema ba,Domin yadda suke zaune babu wanda zaice ba Auren soyayyah sukayi,ba,yadda take girmamasa da yadda takesakin jiki dashi yafi komai yimai dadi,in yayi Rantsuwa bazai yi kaffara ko ada baitaba kin Azeema ba,Abu dayane ke bashi Haushi da ita sakarcinta toh yanzu bayi da haufi Azeema ko cikin mata dubu zata Fidda kanta Ada yana ganin Ni"ima amtsayin wayayyiyar mace,ammh yanzu sai yake ganin Azeema dabata ko gama Secondry sch ba,zatayI Abunda Ni"ima bata taba Saninshi ba,Shiyasa batare da Sanin Azeema ba ya aikama Madina kudi ta account dinta 2 hundered Thousand,Tayita godiya bakinta har kunne,ita ke fadama Ma Azeemar,nan kuma takara zage damtse tana koyama Azeema wasu salo,na yadda zatakama yaya captain ahannunsa,Tunda tazo bata taba Fita ko kofar daki ba,tun bayan Tafiyansu goggo,kullum tana cikin gida in tagama aiyukanta sai takoma tazauna daga kallo,sai ko danne danne awaya,Sai Yaya captain ya dawo bayan ya ci abinci ta tada rigimar sai ya goyata,Toh daga goyon ne,sai Atafi goyon gasken,cikin satin dayan nan Sai ga Azeema tayi kiba tayi haske kamar ba ita,Toh tana cin mai kyau tasha mai kyau,ta kwanta waje mai kyau,Akula da ita toh meta rasa ai sai ta baje waje ta hau kiba tana murjewa.Mganar wajen kula da kanta kuwa bata wasa,saboda ita Fruit basu yankewa agidan,Shikanshi yaya captain bai kiyuwar Soyowa da zarar Sun kare,tunda Tsakani harga Allah yana fa amfana,Shiyasa yanzu Jabir yake tsoron mai mgana dayayi mgana sai yace Shi yaro ne haryanzu buh ya bari ya girma,Abun na damun Jabir Shiyasa yakira maminsa awaya yace tama baffansa mgana Shima ya matsu atura gidansu Mufeeda ko Aliyu zai daina masa kallon Tara Saura kwata😂😹
*************
Yau Takama Sunday ne,Gabadaya yau da Sanitation Azeema tatashi Aliyu na tayata suka zage suka gyara ko"ina na gidan Suka goge,kafin su Fada kichen Su yi breakfast duk da Aliyu da hira kawai ya tayata,Tana gamawa taja Gadanga taje ta hadamai Ruwan wanka tazo zata Fito yazo ya ritsata abayin,cikin bath din ya tura ta da kayan jikinta yana mata dariya Bata Fuska tayi zata fashe da kuka yayi Saurin cewa..
"Oh Pretty,kuka karki yi bari nazo na Fito dake."ya fada yan Fadawa cikin bath,bakinta ya matse yana fadin"kin cika shagwaba.."kwabe Fuska ta sakeyi zatayi mgana sai taji ya hade bakinsu waje daya,lokaci daya yana sabule mata rigar jikinta,hannunta ta sanya duka ta tallafi kanshi bayan tataso ta haye kan cinyoyinsu ta zuro da kafafunta ta baya Dama da hagu,Shiko yasaka duka hanuwansa abayanta yana yin kasa da guntun wandon jikinta.
Basu Fito daga Tiolet din ba,sai da Suka mori juna son rai,saura kiris yarage ayi Azeema taki yarda ta kalleshi Ashagwabe tana fadin"Nidai A"a..."Idonsa na Rufe yace"Meyasa kuma? Ruwa ta dibo ta