hibba sun dawo daga sch nan fa suna cin karo da Azeema sukayita ihun murna kamar su maidata ciki sun hanata sakat,itako tana biye musu Ranar ko Maminsu basu bi ta kanta ba,hatta cire musu uniform da saka musu kaya na Azeema sukace suna so tayi musu,wanu homework ne,harda yar goye goye duk ita kadai,dayake kuma ta saba da yaran,kuma kunsan Aduniya babu aikin da zai gagari Azeema sai dai in ba"a kirkiroshi ba,Karshenta dai Ranar dakinta suka tattara sukace wlh chan zasu kwana har jan madina tayi musu suka makale su Tare Anty Azeema zasu kwana,Azeemar ta roki,Anty madinar kafin ta kyalesu su kwana,aiko sun kai wajen 11 suna hira,kafin su kwanta,ta Shege tsakiyarsu kaunarsu na Ratsata tana fatan kada Allah ya Dau Ranta sai ta haifi mace ta sakamata Suna FATEEMA..,Niko nace karki damu Azeema very soon Aliyu zai baki kwan haihuwa🙈🙈
Sai washegari suka samu Tafiya,bayan yaran Sun tafi mkranta,kasuwa suka Shiga Madina ta darzomata Atamfofi Masu Rai da lafiya super,holland,swices less,codde less,material dogayen Rigana,masu sikat da masu wando,Mini sikat da mini wandunan,bras,pants,kayan kwalliya komai da komai da kayan mata sai da ta siyamata harda takalma masu Tsini da Flat,sai kananun jaka,dan kunne,masu sarka da Fashion Bands,da sauransu kafin su wuce shagon dinkinta,tabada dinkunan kayan,wata in yamurace bosse,ta gwada Azeemar tace jibi ta aiko direba ya karbi dinkunar,bayan madinar ta ijiyemata kudinta cash,suna Fitowa dagana shagon salon takaita aka wankemata kai harda gyaran kafa sukayimata,wajen harda gyaran jiki sunayi,ammh sanin itama madinar sana"arta kenan basu mata tayi ba,domin sun santa tun Tuna budurwa suke gyaramata kai,ta yarda da shagon sun san aikinsu sosai,basu dau lokaci ba,suka kammallamata sai ga gashin Azeema ya mike sosai yayi kyau kamar ba ita,ba kudinsu tayi musu Transfer ta banki suka Fito suka wuce,daganan anguwan Rimi suka biya gidan wata kawarta SALAMATU FODIO SG GUMBI..Ta amshi wasu tsimi ahannunta tare da Wasu garin magani cikin wasu robobi,dayake sana"arta kenan itama,basu wani jima ba,daganan suka koma gida,suna komawa gida,madina ta shiga tiolet ta hadamata Ruwan Turaruka masu tsada hadin yan maiduguri ne,ta umarceta data Shiga tayi wanka,ita kuma ta sanya wani kasko ta kunna Hurashi ta watsa Turare,tana Fitowa da digon Ruwan ta Umarceta data tsugguna hayakin Turaren ya dinga shiganta,ba gaddama Azeema tayi yarda Madina tace,sai da ya sike kana tace tatashi,wani hadin mai shima cike yake da wasu hadin Turaruka tabata tace daga yau yazama man shafawanta,karba tayi ta shafa,kayan da suka siyo ta zazzage pants dinta ciro mata kafin ta miko mata wata kwalba tana fadin"Rike wannan almiski ne,zaki dinga digama wandunan ki kafin ki sanya kinji ko? amsa Azeema tayi tana fadin"Naji Anty.."wani riga da Sikat Madina ta mikamata tana fadin"Karbi ki sanyasu,wadandan Dressing din,duk bayan kin daidaici lokacin dawowar yaya captain ya kusa zakiyisu,ammh bayan kin tabbatar da Dinner dinshi is ready kinji ko.."kai Azeema ta gyada tana Fadin"Naji Anty.."kada kai tayi tana fadin"Shirya bari baje na hada miki Sauran magungunar ga Turaran wankan chan a tiolet sau biyar akowanni Rana,Kowani wanka Murfin jarka Uku zaki sanya,na sati daya ne,bari na kawo miki Sauran na garin akwai na karin Ni"ima kana kuma akwai na mganin infection ma"ana Sanyi..."Gyada mata kai Azeema tayi alamun ta Gane ficewa tayi tana fadin"In mun gama da wadanan kingane sai mu dora da lacran mu,munayi lokaci daya kuma muna Shiga kichen tare,domin kinsan Duk wadananan Abubuwan basu tasiri,sai Mace ta kasance ta iya sarrafa mai gida ta hanyar iya girki,balle nasan Sojiji da son cin Abinci mai dadi.."Tana fada tana yar dariya kan Ta fice daga daki.
Yar Dariya Azeema tayi tana bin Tulin kayan da suka siyo wadanda ke zube bisa gado,kayan da Anty tace ta saka take bi da kallo,Tana mamakin yadda zata sakasu,sai da bazata iya bama Anty madina kunya ba,da hanzari ta sakasu,kayan roba ne sai suka lafe bisa jikinta gashi sun kamamata,hips dinta ya fito tana tafiya suna rawa,duk da ta saka pant,sai kirjinta wadanda suka cika fam,suna bin bayyana,gashinta ta daure da band,kayan baida dan kwalli,Sai ta samu wata hula ta saka ta isa gaban mirrior tana kallonta sai da tayi mamakin ganin yadda kwana daya tadawo gawani Fitinannen kamshi na binta da ko"ina,duk inda ta Shinshina ajikinta sai taji kamshi,ita ta kanta take lumshe ido in ta Shaki kamshin jikinta,shafa fuskarta tayi taji wani Santsi Mirmishi ya subuce mata lokaci daya hawaye sun ciko idanunta ta furta ahankali
_Thank you,Yaya captain,Thank you goggo,Thank you Ummah and Thank you too Anty madina.._ take fada tana goge kwallar data zuraromata bisa kumcinta
Madina dake bayanta ta bugamata tafi tana fadin"Weldon matar Yaya da alamun zaki Saurin dauke komai kafin sati dayanmu ta cika,.."Tafada bayanta yar aikinta ne,ke ta Shigo dawasu jarkunan magunguna dawasu arobobi sai madara Sajet sajet,sai Zuma awata katuwar gora sai gumba mai yawa,gabanta tasaka aka zube haka ta zauna ta tankwashe kafa itama Azeemar ta sauko daya bayan daya take maata jawabi,da wanda zata sha da madara,dana sha da zuma,komai dai tayi mata jawabi,harta Fahimta,nan kuma ta ake ta shiga hadamata ta mikamata tana Sha,duk da wasu suna da bauri,ammh hakanan take Daurewa Tunda ba laifi takan danci karo da mai dadi har dawani hadin Dabinon makka mai dan karen dadi,Azeema taji dadinsa sosai,shida wani garin Aya shima da madara ake sha Duk sun mata dadi sosai,Tana gama sha madina ta kwashe ta sanyasu gefen gado tana fadamata Sau daya zata dinga sha Arana,ammh Turaren Tsugguno sau biyu arana safe da yammah Ficewa tayi ta barta tana fadamata cewa gobe zasu Fara lacra su,da safe Allah barshi da yammah sai sudinga Shiga kichen domin koyar da ita girke girken zamani wato Akushi da Rufi😂Tuni Azeema ta amsa da toh domin Ta fahimci Rayuwarta ta yanzu tafikomai dadi,koba komai itama tanaso ta waye tazama irin Anty madina da kawayenta,zaka gansu so classisc mallam babu Raini ko kadan.
*Intellenget writers asso..*
*Janafty..Aka Shakira*💇
*ALIYU GADANGA..!*
_(The Story of Young Soldier man)_
*Wattpad:Janafnancy12*
_Mallakar:Janafty💖_
*DEDICATED TO MY MOMMAH...HAUWA S ZARIA(MMN USWAN)*
_Special gift to my Real Dota RAHMA😘Ladingo yar mutan Niger_
*Intelligent Writers Association*✏
_*Kyakyawan Shafi lokaci Daya da kyakyawan sadaukarwa,eh mana domin Duka Shafin yau na ALIYU GADANGA.,Kacokan Dinsa sadaukarwane ga Daukacin malamai da Shugabannin dake mkrantar primary U.B.E. KOFAR KIBO ZARIA..,Gaisuwan Fatan alherin zuwa gareki ne mai gayyah mai aiki,headmistrees HAJIYA BINTA UMAR ABUBAKAR(Momy)Allah yaja kwana👍😂,Tare da uwar gayyah Assitances,HALIMA IDRIS(Goggo balaraba)😹 Allah dai ya biya,bazan yi toya na manta da albasa ba,jinjinar ban girma zuwa gareka lantarkin zuciyata,kuma malami na,kuma uba yake awajena,lalle na kasance mai sa"a Tunda Allah yahadani da gwarzo kamar ka,UMAR BELLO SADIQ(Uncle me)😘,Soyayyarka gareni sai dai nace A kinda masha Allah,Kulawarka akaina sai da na kirashi da Alhamdulillah Allah nake roko daya iya maka Abunda kagaza,Kafin na wuce zuwa wani ajin yakamata nafara Farawa da gida ne,gaisuwa tare da Fatan alheri gareku MALAMA RUKAYYAH(Maman Suhailat)sai MALAMA AISHA(mmn Fuad)sai MALLAM ABUBAKAR(mallam Ammar),Bazan manta daku ba dole ne nayi jinjinar ban girma gareku iyayan dakina,ANTY HADIZA,tare dake MALAMA AISHA,Bazan manta dake ba kawata abokiyar Cin mushe,😂😛,kuma malamata ba wato ANTY JUWAIRRIYAH,Son so Fisabillillah,kai zan yi Abun kunya ban ambaci uwata ba takaina ba MALAMA ZAINAB(Anty Ummi)tare dake Malama Hafsart,malama jamila,(Namecy),sai malama Harira,Anty hauwa,Malama Asiya dake da malama Hafsart,ban manta dakai ba Mallam Aminu tare da wadanda ban ambataba,gaisuwan Ban girma gareku Allah yabar zaman Tare Ameen..Ku sani ku kara sani JANAFTY AKA SHAKIRA,na Sonku Fisabilillah*_😘😍❤💕💖💞💘🔐
*Chapter 18*
"""Koda garin Allah ya waye,Kafin Anty madina tagama Shirya yara zuwa mkranta Tuni Azeema hartayi wanka,takumayi Turaren Tsugunnonta,takuma sha mganungunanta wanda Anty madina ta nunnuna mata,koda Anty madina ta Shigo Azeema ta cakare,cikin Wata Atamfa mai blue da ja,cikin wanda goggo ta dinkamatane,simple make up ne Afuskarta,ta taje gashinta tayi baya dashi ta saka band ta daure,tsaye take gaban madubi tana cikiniyar Daura dan kwallin Anty madina ta Shigo kallonta tayi tana rike baki kafin tace
"Matar yaya,Allah kinyi kyau kinganki kuwa chanchadi.."Tafada tana dariya Rufe Fuska Azeema tayi kafin tace"Ina kwana Anty madina.."Ta amsa da lafiya kalau matar yaya,yakika tashi..? tafada tana karisawa kusa da ita ta karbi dankwalin tana fadin"Laccan Mu ta farko zata Fara daga Dauran dankwaline,Tunda Shi na tarar kinayi.."Gyada kai Azeema tayi tana kallon yadda ta dankwasa dankwalinta,Kafin ta Dauramata bisa kai,Daurin Maryam babangida tana yi tana mata bayanin yadda zatayi bayan tagama sai tace ta kwance ta daura da kanta,nan da nan kuwa ta aza abinta yayi kyau sosai Tafi Anty madina tayi mata tana fadin!Good matar yaya da alamun, dai zaki Saurin dauke komai,yanzu taho muje mufara dora karatunmu lokaci na kurewa.."Tafada tana jan hannunta zuwa kan gadon,tsakiyar gadon madina ta hau tana fadin"Hayo nan matar yaya..!Hayowa Azeema tayi suka zauna Suna Fuskantar juna bayan Dukkansu sun tankwashe kafafunsu Riko hannunta Madina tayi kafin tafara da cewa.
""Abu na farko kafin mufara dora karatunmu yakamata kifara sanin menene Aure,Aure dai wani Nau"i ne na bauta,gabadayanshi bauta ne na ubangiji,kuma duk Abunda akace Bautane na ubangiji toh sai fa mutum ya dage kuma ya zage damtse,Abubuwa guda biyu da suka kasance ginshikin bauta ma Aure sune LADABI DA BIYAYYAH..Matukar kinaso,kiyi bautar Aure,sai kin kasance,kina da ladabi da biyayyag,kibi mijinki Sau da kafa,yi nayi bari na bari,kiyi amfani da Umarninsa kiyi hani da Abunda yahanki,karki tsallake Umarninsa ko alama,ki kuma bisa don yana gaba dake,tsakaninki dashi tamkar tazaran kasa da Sama ne,Aljannarki,tana karkashin digadigin sane,sai yalamuncemiki zaki Shiga Aljannah,Abubuwa masu muhimmancin dayakamata kisani bayan Ladabi da biyayyah wanda suka kasance ginshikin,ki kasance mai HAKURI.. Hakuri wani babban Tsani ne,Azeema matukar babu hakuri Da juna Da Auren mutane dadama ya mutu acikin Duniyan nan,domin ko harshe da hakori,suna sabawa balle zaman mutum da mutum,Namiji yana son agirmamasa sosai balle ke mijinki yana da son abashi girma bayason Raini ko kadan,kuma yana da isa da takama,toh dole sai kin zama mai hakuri domin zaki dinga ganin yana yi miki komai cikin isa,duk da ya isan ne,domin Shi Shugabane gareki,ki ka sance mai kauda kai,banda yawan korafi kigani kikigani kiji kuma kikiji,Toh in kikayi haka Aurenki zai zauna lafiya kuma zaku Fahimci juna Sosai,abu nagaba danikeson fadamiki,Shine Kisance mace Tagari wacce take maida damuwar mijinta nata,Farincikinshi shima naki ne,ki kasance kina kokarin rike Sirrrinki dana mijinki,domin bayyanar da Sirrinki ga kowa,koda ga goggo ne,ko kakarki ke ko ni kaina,in bawani abu bane wanda yazama dole sai iyaye sun Shiga ba,Shima din ki bari sai dai in Shi yafara furtawa,yin hakan ba karamin karama mace daraja yakeyi ba,kinga duk sanda Namijin yasan baki da Sirri shikenan ya ranmiki Daga ranar zai Fara kokarin Rike Sirrinshi bazai taba bari ki sani ba,Ki sance mai yawan Fara"a ga mijinki Azeema,karki bari ko alama ya zauna cikin Damuwa kiyi amfani da baiwarki ta diya mace ki hillaceshi har ya manta damuwarshi,ki sance mai ba mijinki shawara,ta wajen aiki ne,na game da yan"uwanshi ne,ke nakomai ma,ki zama mace jaruma wacce zata dinga karafafama mijinta gwiwa aharkan komai,kinga in kika cika wadan nan sharudan kin gama cika Sharudan zama MACE TAGARI.."Fatan kina Saurarena da kunnen basira.
Jikin Azeema daya gama yin sanyi tagyada kai tana fadin"Eh ina Sauraranki Anty madina.."gyara zama madina tayi kafin tace"good to kinga duk wannan karatun danayi miki toh matukar baki cika Wadandan Fa"idojin da zan gayamiki ba,toh duk abanza ne,domin kamar kayi wanka ne kayi kwalliyah ka koma kayi ma kanka wanka da Kasa ne,"Kallonta Azeema tayi tana Sauraren mai zata cemata Madina ta cigaba da Fadin"Fa"idojin Sune, *KWALLIYAH,GIRKI,IYA SALON MGANA,SALON KWANCIYA.*Kinga duk wanda kika saki acikin hudun nan Toh ina mai tabbatar miki kin samu nakasu"Zaro ido Azeema tayi madina tace"Yes..Matukar baki iya girki toh yakamata ki daina amsa sunanki na mace,ko baki iya kwalliyah ba,da yadda zaki dau dressing din da zaki dau hankalin megida ba,kema Sunanki Sauna,kana matukar baki iya Salon mgana ba,da yadda zaki Rikita mai gida da salon mgana na jan hankali ba,kema Sunanki sakara,uwa uba baki iya salon kwanciya balle sanin yadda zaki sarrafa maigida ta hanyar rikitashi da salolin kwanciya toh wannan Sunanki Dussa,duk matakan baya,kin gama zubar dasu,don sai wadannan sunyi kyau hasken wadanchan ke bayyana"
gyada kai Azeema tayi kafin tace"Toh Anty kimin bayaninsu daya bayan zan Fi ganewa.."Anty madina tace "Yanzu kuwa matar yaya.bari mufara da kwalliyah, girki wannan sai anjuma zamu Shiga kichen Shi pratical zamuyu kingane.."gyada kai Azeema tayi kafin Anty madina ta Furta..
*KWALLIYAH..* ita kalmar kwalliya ko ahausance sai da aka kawatata kafin Afurta,Ita mace kuma dama asanta yar kawa da kwalliyace,kwalliya kala kalace,akwai wacce akeyin wanka kawai asaka kaya Shikenan,anyi kwalliya toh ni ba ita nake Nufi ba Azeema Firstly Ki lakanci kayan da in kika saka Suna amsanki,riga da Sikat ne,ko kuwa Riga da zani ne? Doguwar rigane? ko kuwa kayan Rumgumar darling ne,ma"ana kananan kaya na zaman Falo,da inda kika karanci Kayan da sukafi fitar miki da Sirrin kyau sai ki lazimci dinka ira irensu,bayan nan kada ki dauka ance kwalliya ki zata wannan kwalliyan ta zamani ne data Fito ta hauka,ki saka Foundation ki zamo aljannah garin gyaran ido ki Rasa gira,No ba ita ba Simple make up,wacce da an kalli mace asan ta san Abunda take,kuma kallon Fuskarta zai sa agane kedin classic ce,ki shafa hodarki sai jambakinki wanda yayi daidai da kalan kayanki Shima kada ki cika,ki laziminci sanya kwalli domin Farin idon mace bai da kyan gani,ki koyi kashe dauri kala kala domin burge mijinki koyi salon Tafiya mai daukan hankali duk zan koya miki wannan,Ki sanya dan kunne da sarka ki sanya awarwaro,da Sauran kawan mata kada kibari mijinki yadinga shakan wari ajinki basai kin zama kwado wajen wanka ba,kiyi koda sau biyu Arana da wankan gaisuwan Safe da waankan barka da dawowa megida,wankan safe ta Kayanmu na hausawane Atamfa ko leshi,ko wht ever dai,da yammah kuwa english wear ne,mai wando ne mai sikat ne,sai dai wanda kika zaba duk dayane ya kasance dai koya kika gilma kamshi ke binki shiyasa duk Rinti duk wuya kada ki Rasa humra ko kiyima Turare yaji sam kada ki Fara Azeema domin kamshin na jan Hankalin Namiji zuwa gareki tare da Kara dankon kauna,sai Abu na gaba
*IYA SALON MAGANA.* Kefasan akwai dayawa matan da basu iya mgana da miji ba,wata in tana mgana da mijinta kamar tana mgana da wani kaninta ko tsaranta ba karya harshe ba Tautausawa ba girmamawa bawani karkwasa balle wani Shagwaba a"a sai dai kawai damkam dinkin kamar wata Sauna ko sakarya yakamata mata su gane harshenki yazamanto kala kala ne,ma"ana harshen da zakiyi mgana da mijinki dabam,wanda zaki amfani dashi wajen mgana da kawarki dabam,wanda zakiyi da makotanki dabam,kai kowa kinsan yadda zaki karya harshe ki iya salon mgana dashi Sai kiga kin zama mace mai aji da kima a idon Jama"a,mganar yadda zaki karya harshe wajen Miji Shine First look at me Azeema kamar ace kene Abban Hidaya muna zaune haka kamar zanyi mai wata mgana mai muhimmanci abu na Farko sai na Fara jan Hankalinsa zuwa gareni,bayan na kuramai ido na langwabe wuya gefe daya na marairaice To indai yaga kinsamai ido haka zai bar dukkan Abunda yake ya tambayeki"Noor meya faru ne?Zaki Fara rigimarki ko? ke kuma dagajin haka sai ki shagwabe Fuskarki da muryanki kice"Abban hidaya ya mganarmu Ta Ranar naji haryanzu bakace komai ba.."Ki karishe kinamai Fari da ido,toh lokaci daya zaki ga ya Rude yana tambayanki wata mgana,ke kuma sai ki kalailayeshi bisa jikinsa,domin yin nesa da Jikin miji na rage Shakuwa Shawarata gareki Jikin yaya captain yazama wajen zamanki matukar yana gida ta hakane body contact dinku zai Shaku da juna,kuma shi Namiji yanason adinga mannemai ana lafemai bisa jiki,kin Fahimta..? ajiyar Zuciya Azeema ta Sauke kafin tace"Na gane Anty madina.."ta gyda kai tana fadin"Naji dadin jin hakan yanzu bari muje gaba lokaci na Tafiya,Abu na karshe kuma wanda yafi muhimmanci Shine
*SALON KWANCIYA..* Zaro ido Azeema tayi Da Sauri tana Rufe baki da hannu hararan wasa Madina ta mata Tana Fadin"Stop joking Azeema Abu ne mai muhimmaci infact ma Shine ginshikin Aure,so u better listening very carefully don zai miki amfani ki cire kunya domin dama rayuwar aure sai ka cire dukkan wata kunya kake iya mace mai aji da Kima a idon mijinta.."Saurin gyada kai Azeema tayi,kafin Anty madina ta dora da cewa
"In Akace Salon kwanciya ba Ana nufin komai bane illah yadda zaki iya Salo salo tare da hikimar Sarrafa mai gida A Shimfida,Na farko bawai ki zama wata dussa ba,kina kwnce duk inda miji ya juyaki ki juya kamar wata bichan No ki zama kece kike jan Ragamar Abu kezaki dinga sarrafashi Ta salo kala,kala wanda zai gane yes yana tare da cikakkiyar mace wacce ta san Kanta,ki sance wacce zaki jiyar da mijinki dadi takowani Fanni,ki sanyashi yayi miki kuka harda koke koke,ki sakarmai jiki,shima ya sakar miki kada kiji kunya ki saki jikinki ki Tsotse mijinki daga sama har kasa,shima haka kuskuren da mata yakeyi Shine sai ga mace wai sunyi Fada da miji sai kiga ya nemeta Shimfida,wai Saboda yabata miki rai sai kiga mace tayima namiji sharaf yayi yadda yagama dama dake,bawani Taimako,toh hakan kuskure ne,wlh yana kawo tsana koda bata miki rai yayi,in kika tsage kika farantamai wlh tallahi da kanshi zai gane yayi Kuskure har yabaki hakuri,Azeema sai kin dage sai kuma kin zage damtse,domin Duk cikarki mace matukar baki gyara chan headquater ba duk abanza,kinga magungunar dana baki kina amfan dashi,duk dakaina na hada kayan Ni"imar mata ne,Kayan Gona ne,sai su aya dasu dabino,sai su kanunfari da Sauran itatacenmu,kada ki bari Fruit yadinga Wuceki duk Rana,ki lazimci Shansu akoda yaushe,domin Babu Abunda yakaisu kawoma mace Ni"ima kamar Shi,ga madara ga zuma koda baki dashi siya madararki ta sajet kullum na Hamsin ki dinga kalata da zuma duk safiya ki dinga sha kigani wlh sai kin bani labari,ammh yanzu mata sun Haukace da mganin mata kamar ibada,Abun haushi ma sai wani lalacewa Daya Fito yanzu sai kaji ance wai kashin tantabarama mganin mata ne kasiddan,ke kuma don kina wawiya Tantabara ta Fitar da cuta ke kuma ki siya,ki dinga Turawa kamar wata zararriya wlh mata mu Farka da wannan Siya siya dakikeyi da sana"a kikama da kudin daya fiye miki wlh domin yanzu kishinki Abun hannunki dakuma yadda kika dauki Aurenki,matukar Baki da sauran Abubuwan nan,koda mganin dubu dari