An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
*WANNAN PAGE ƊIN NA SADAUKAR DASHI GARE KA, UNCLE YUSEEPAH NADABO,THANKS FOR HALACCIN KA AGARE NI ALLAH YA BAR ZUMUCHIN MU FATAN ALKHAIRI A GAREKA ALLAH YA ƘARA MAKA BUƊI DA ƊAUKA KA, FATAN ALKHAIRI NAKE MAKA A DUKKAN RAYUWAR KA,UBANGIJI ALLAH YA KAREKA DAGA SHARRIN MAKIYA DA MASU YI MAKA HASSADA, ALLAH YA ƘARA MAKA BASIRA DA ƊAUKA KA INA MATUƘAR GODIYA*
*FAREEDAH NABEEL DEDICATED TO :- ƘAWATA WATO XAYYNEB💤💤(XEXEN FASAHA)*
*SAKON FATAN ALKHAIRI ZUWA GARE KI ƘAWATA WATO XAYYNEB 💤💤 (XEXEN FASAHA) ,THANKS FOR KULAWARKI AGARE NI ALLAH YABAR KAUNERH ,FATAN ALKHAIRI NAKE MAKI A DUKKAN RAYUWAR KI,UBANGIJI YA KAREKI DAGA SHARRIN MAKIYA DA MASU YI MAKI HASSADA, WALLAHI ALLAH INA KAUNAR KI HAR CIKIN RAINA, ALLAH YA ƘARA MAKI BASIRA DA ƊAUKA KA KANA ALLAH YA ƘARA MA MAMAMU LAFIYA TARE DA NISAN KWANA*
*Sdeendtm*
I'm sell data to all Nigeria network
Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*
*I'm
selling MTN data with this cheap price*
*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*
*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951
Bismillahirrahmanirrahim
Da sunan Allah mai rahma mai jin kai
dukkan yabo da godiya su tabbata ga Allah mai kowa mai komi sarkin daya halicci sammai da kassai batare daya kwaikwaya awajen kowaba madaukakin sarki me kowa mai komai
Wannan littafin ƙirƙirar ren labarine. banyi shi dan cin mutuncin wani ko wataba.
so idan yayi shige da halin mutum yayi hakuri nayi ne domin fadakarwa da kuma nishadantarwa, badan cin mutunci ko izgili ba
yadda na fara wannan sabon littafin da Bismillah inna rokon ALLAH yasa in gama da ALHAMDULILLAHY
*🌺chapter 1-2🌺*
*MINNAH*
Wani katafaren gida ne da yake dashe a unguwar shiroro road
na hango!
tsarinsa da kyawunsa ma Abin kallo ne.wanda idan har bakasan a inda kake ba .baza ka iya tantance wace ƙasa kake ba
kai Daga gani kasan Allah yayi baiwa ga dukkan wanda Ya mallaki wannan gidan,
kyakkyawar mace ce Ta bugawa a jarida na hango,doguwa mara jiki shape d'in bakin ta gwanin ban sha'awa gashin girarta ta cika sosai .gashinta na ido zara-zara ,hancinta dogo ne de-de masali dan bai yi tsayi dayawa ba, Kuma bai Yi gajarta ba,
fuskarta it'a ba Mai fad'i ba ,kuma ba mai tsayi ba ,idanuwanta de-de Misali dan suma basu yiyawa ba Kuma basu yi ƙanana ba ,duk da cewa ba fara bace chocolate colour ce hakan ba zai sa ace ita ba kyakkyawa bace ba dan ta haɗA dukkanin abubuwan da ake bukatar agani wajen y'a mace
bata da jiki Kuma ba siririya bace Dan babu wani mahaluk'in ɗa namiji da zai ganta bai ji ya yaba da irin tsarin halittarta ba,
*FAREEDAH KENAN*
shekarunta basu haura shekaru ashirin da bakwai ba ,ko murmushi tayi sai ya ratsa ko inna na jikin ɗa namiji bare kuma kallonta
mai cike da birgewa...
Zaune take a saman one seat a gaban dressing mirror ,tana shafa turaren jiki wato humra , kasancewar ta Mace ce mai son k'amshi , tana shafawa ne a duk bayan lokacin da ta kammala yin kwalliya, domin kuwa a yanzu ma kwalliyar ta kammala dan har ta saka kayanta ,
fuskarta babu wani makeup sosai daga powder sai jagira da tayi da kuma ɗan lipstick da ta shafa a labb'anta , tayi kyau matuka musamman Irin tsarin shigar da tayi na riga dogo ,haka kalar kayan blue da yellow abin gwanin birgewa,
tana gama kammala shirin ta ,sannan kuma ta ƙara kallon madubi sannan ta juya ta nufi hanyar fita daga cikin ɗakin cikin salon takun tafiyar ta mai
matukar ɗaukan hankali,....
Ahankali take tako steps din benen tare da saukowa daga saman upstairs, kana jin karar takun takalmanta kas kas kas cikin natsuwa
tana gama k'arasowa cikin tsakiyar parlourn ,daidai lokacin ne kuma wata matashiyar yarinya ta fito daga cikin kitchen,
K'arasowar ta Cikin tsakiyar parlourn yayi de-de da fitowar Azmerh daga cikin kitchen , ɗauke da faranti Ahannuntah ,wanda ta ɗaura masu food flask flask d'in abinci asama Tare Da plate and spoons and forks,
daga ganin alamun abincin dinner su na dare ne, haka zalika yayi de-de da kai dubanta zuwa ga kofar fitowa kitchen a de-de Lokacin ne kuma idanuwanta suka sauka a kan Azmerh,
Tsayawa FAREEDAH tayi turus atsakiyar parlourn tana kallon Azmerh,cikin ranta tace son maso wani koshin wahala , Allah dai ya kyauta wa wasu masu matattun zuciya ,musamman marasa zuciya Irin su Azmerh ,tana gama k'arasa maganar zucinta ,direct inda Azmerh take tsaye atsakiyar parlourn tana jera abinci asaman center table ɗin dake tsakiyar parlourn FAREEDAH ta k'araso gunta cikin fara'a FAREEDAH ta kalli mumunar fuskar Azmerh Kafin cikin murmushi FAREEDAH ta buɗe bakin ta tace"
Azmerh kenan ,..
Agaskiya kina matuƙar ji da yayan nan naki,yau tun daga safiya zuwa dare hidimarsa kike!...
"D'agowa. Azmerh tayi tare da mik'ewa tsaye ,kallon banza ta aikawa FAREEDAH Dashi Haɗi da gallamata Harara kafin ta haɗe rai, Cikin daka mata tsawa Azmerh ta buɗe bakinta tace "kinsan shi doki girmansa da haniniyarsa sune suke nuna kasaitar shi..
"Dariyan dole FAREEDAH ta kyalkyale dashi cikin dariya FAREEDAH tace" gaskiya ne kam ,wannan haka yake, kin yi gaskiya yan mata
Duban Azmerh FAREEDAH tasake yi dakyau tukun Kafin daga bisani cikin tsananin farin ciki FAREEDAH ta buɗe bakinta ta ɗora da cewar"Ni dai fatana Allah yasa ki samu abunda kike nema....cikin fusata! Azmerh ta katseta ta hanyar fad'in "....
"Bangane abunda kike nufi ba?
"Tsayuwa FAREEDAH ta gyara tukkun Kafin Cikin smiling FAREEDAH tace"ina nufi Allah yasa wanda kika yi domin sa yayi masa maganin yinwa da zai kwaso
"Cabd'ijam inji cewar Azmerh tana fesar da wani irin huci!
Sannan cikin tsananin masifa haɗi da bala'in da suke cinta ta cigaba da cewar" ai ko ya zama dole gyaɗa tayi mai ,idan taki tasha matsa,
tun daga safiya zuwa dare in bata lokaci na ina abu guda ɗaya,tabbas yau makwabta suma sai sunji k'amshinda basu taba jiba
"Haha haha haha FAREEDAH tasake fashewa da dariya har da zubar da hawayen dole sabida tsabar shan dariya
Cikin dariya FAREEDAH tace"hmmmm nidai bari inje in k'arasa yin aiki na kar cikina ya fashe,. .
"Kutmar bura uban aiki ɗin da zakije k'arasa ta ɗura ashar, ba aiki ba ubanki dai, shegiya yar gidan bokaye, Yar matsiyata kawai. ke har wani aiki kika iya! .in banda shirme da jagwalgwalo ,shashsha kawai yar matsiyata ,,,,,kuma bari kiji , idan ma baki sani ba to yau kisani insha Allahu yau idan yayana yadawo daga gun aiki yau dolenshi ya amince da maganar auren mu,kuma duk maitarki da bin malamanki akan kar maganar aure na da yayana kada ya yiwu, insha Allahu wataran Kamar anyi an gamane, dan ni nasan ta hanyan da zanbi in shawo kan abuna,so daga yau ina son kirubuta ki ajiye muddin ni Azmerh na shigo cikin gidan yaya NABEEL a matsayin matarsa tofa shakka babu sai nasa shi ya sake ki , kai wataran sai nasa kin bar gidan nan,dan nina san me na shirya, dan wallahy Allah natsaneki matuƙa, ji nike kamar in shake maki wuya har sai kin mutu kafin nasake, sbd yanda nake bala'in jin haushin ki acikin rai na,
Matsowa Azmerh tayi daf da FAREEDAH kamar zata shige cikin jikin ta ina nufin face to face sannan tasaki wani murmushi irin na mugunta Azmerh ta ɗora da cewar
"baki san ni bane har yanzu dan inda ace
Ƙin san ni, Wallahy zakiyi MATUƘAR jin tsoro na! sai nasa kin bar gidan nan
Taka rasa zancenta
tare da k'wafa
"HAHA haha haha FAREEDAH tasake fashewa da dariya sannan tace"Allah ko yan matah ,.....
OKAY....
Allah yanuna mana lokacin Kawai FAREEDAH ta faɗa tana mai ɗaga kafaɗar ta alamun ko ajikin ta kenan, kana cikin nutsuwa ta juya direct ta nufi hanyar kitchen Tare Da shigewa
kitchen abinta.
_____________________
Bacin rai mai tsanani ya sake rufe Azmerh cikin ranta tace wai yau ni wannan yar matsiyantan take wa dariya, "ita dai FAREEDAH haka Tabar Azmerh da zage-zage
haɗe da tsinewa FAREEDAH d'in Albarka " 'kwafa Azmerh tayi tare da bin bayan ta
Da misalin ƙarfe takwas da rabi na dare....
___________8:30 pm, wani kyakkyawan matashin handsome guy ne ,ya turo kofar parlourn ,sanye yake cikin wasu kananan kaya da suka yi mutukar ansar jikinsa ,kana kuma yakara bayyanar da kyawunsa da kwarijininsa NABEEL ya hadu iya haduwa,kyakkyawane NABEEL asalin kyakkayawa kuwa domin duk inda ake batun kyau to wannan magidancin zai answer first number ,Cikin parlourn
ya shigo tare da furta sallam
"Assalamu alaikum!"
AMIN walkslm inji cewar Azmerh ,"cikin natsuwa NABEEL ya k'arasa shigowa cikin tsakiyar parlourn, samun guri yayi ya zauna a saman two-seater yana mai sauke nannauyar ajiyar zuciya',',,, kallon kyakkyawar fuskarsa Azmerh tayi kafin cikin kulawa ta buɗe bakinta tace"..
"Sannu da zuwa !..
yaya ina wuni!!,.
ya aiki ya jama'a!!! ?..
"Cikin sauri ya jiyo ya kalle ta dan shi baima san akusa da Mutum ya zauna ba,
sabida tsabar gajiyar daya kwaso, shima ɗin duban Azmerh yayi dakyau tukun Kafin cikin kulawa ya buɗi bakinsa yace"aaa yau kece a gidan?'...
"E Wallahy yaya..
Sannu da zuwa
Ya aiki?
"Alhamdulillahy...
"To madallah
Gyara zama Azmerh tayi Haɗi da Washe baki sabida yau taga yadan sake mata fuska, Cikin fara'a Azmerh ta cigaba da cewar"yaya nerh yau girki nayi maka na musamman!"
firgigi NABEEL yayi kamar wanda aka tsikara yasake dubanta kafin cikin ɗaure fuska NABEEL ya buɗi bakinsa yace"kikai wa gida dai,ai bani kaɗai ne a gidan ba
"To ni dai yaya kai kaɗai na girka mawa, Janyo masa table ɗin tayi gabansa kana ta shiga serving ɗinsa
Ahankali Cikin nutsuwa ya kai hannunsa kana ya debi abinci acikin cokali , yakai bakinsa ai nan da nan fuskarsa tasauya kamar wanda yagumtsi guba
tun kafin ya fara taunawa yaji Abincin tabal ba daɗi sai wani uban gishiri, Sannan kuma yaji d'andano ba irin wanda yasaba jiba
,yana tauna abinci yana tabe bakinsa tareda yamutsa fuska,haka ya tauna abinci yana tah yamutsa fuskarsa ."yayin da ita kuma Azmerh ta kafe shi da ido tana mai famar washe baki
, shi kuwa Nabeel sai famar yamutsa fuskarsa yake
Kai Ka rantse kashi yake taunawa, dan dakyar ya iya haɗiye abinchin dake baƙin sa cokalin hanunsa ya ajiye.. ɗaure fuska yayi cikin ɗaure fuska ha'di da bata fuska ya shiga 'kwalawa FAREEDAH kira
"FAREEDAH!
inji cewar NABEEL cikin tsansar
ɓacin rai
FAREEDAH NABEEL!!
NABEEL yasake kwalawa FAREEDAH kira akaro na biyu
"NA'AM .....
Injicewar FAREEDAH tana mai amsa masa kiranta dayayi mata, kana Cikin sauri ta fito daga cikin kitchen
"Mtsww! Wata uwar tsaki Azmerh taja sbd duk duniya ta tsani taji ankira FAREEDAH da FAREEDAH NABEEL
"Ita kuwa FAREEDAH kai tsaye ta nufi inda suke zaune ta k'araso gurinsu, kallon kyakkyawar fuskarsa tayi kafin cikin fara'a Haɗi da kulawa had'i da sanyayen murya
FAREEDAH tace"..
Sannu da zuwa!my Prince
Ka dawo!!
Ya aiki ya jama'a?!?..
Ɗago kai NABEEL yayi tare da kallonta kafin cikin sanyin murya NABEEL ya buɗe bakinshi yace "
yawwa sannu
alamu yana cikin ɓacin rai
"Cikin murmushi FAREEDAH tace'kalbinerh yau ka ji ɗanɗanon ba irin wanda ka saba ji ba ko?
"Kallon kyakkyawar fuskar matansa NABEEL yayi kafin cikin sanyi muryarsa Haɗi da tsananin kaunar matarsa ya buɗi bakinsa yace"babu wani nau'in abincin da zan ci ko in saka shi abakina har ɗanɗanonsa ya ratsa harshena, matukar ba hannuwanki suka sarrafa abincinba ,ina nufin matukar ba hannuwanki ne suka haɗa mana abincin gida nan ba
"NATSUWA FAREEDAH ta karayi sannan takura
masa idanu
kafin FAREEDAH tace".....
Ban fahimce ka ba?
"FAREEDAH wannan abinci daga ji bake kika yi shi ba, in kuma ke ɗin ce To akwai sa hannu wani a ciki,dan haka yi kokari ki kawo min.ko da taliya ce kid'an bararraka min.
"Kan bura uba!!! Azmerh tazabga ashar saida NABEEL da FAREEDAH duk suka waigo afirgice suka dubi inda Azmerh take tareda zaro idanunsu sabida tsananin mamaki.....
Yayinda Ita kuma Azmerh ta mike tsaye tana mai cigaba da cewar"..
Amma NABEEL lallai kai ɗan rainin hankali ne ,...
Inji cewar Azmerh cikin tsantsar zafin rai.
Sannan cikin faɗa da masifa Haɗi da tsananin bala'in da suke cinta Azmerh ta cigaba da cewar...
"In bata lokaci na!
In bata ajina!!
Tun daga safiya zuwa dare, ina Abu guda ɗaya, amma daga karshe kayi Allah wadai da bajinta?
kallon Azmerh NABEEL yayi kafin cikin ɗaure fuska NABEEL ya buɗe bakinsa yace"Azmerh babu wata mace me aji indai har FAREEDAH NABEEL tana nan, sannan kuma kin daɗe da sanin sirrina na zama na da FAREEDAH.tun Farkonsa har da karshensa dan haka babu wata mace in ba FAREEDAH ba,..
"Tsawa Azmerh ta bugawa NABEEL cikin k'araji kamar zata dake shi ta furta"
in hakane kuwa wallahi ka zalince ni, kuma zan iya cewa
Allah ya saka min,...
Mik'ewa tsaye NABEEL yayi cikin tsananin ɓacin rai NABEEL bai tsaya wata wata ba ya sauke mata mari" jikake tasssssss amatukar firgice Azmerh ta dafe gefen fuskarta inda taji saukar mari Sannan cikin zubar da hawayen Azmerh tace"...
Yaya NABEEL ni ka mara,?
"Cikin ɓacin rai NABEEL ya daka mata tsawa yace"an mare ki ɗin ko zaki rama ne?
Cikin sauri FAREEDAH ta furta"haba NABEEL bansan ka da saurin hannu haka ba
"Cikin ihu Azmerh tace "Dan Allah gafara can ,munafuka, ke har kina da kalmar da zaki faɗa tai tasiri ,ban cin duk maganganun da kika faɗa masa akunnensa
"cikin sanyi murya FAREEDAH tace"
"Allah ya baki hakuri Azmerh,ni dai asanin da nayiwa mijina ,baya cin abincin ko wace mace in ba na matarsa ba ,shiyasa na Tanadar masada abincin shi .ba tare da na gaya maki ba .amma saboda alakan dake tsakanin ki dashi ,shiyasa na Kyale .
"Cikin sauri NABEEL yace"me kike wani bata hakuri , hakurin me kike bata,Dan Allah rabu da ita ,kawo min abincina Dan Allah ni yunwa nikeji
"Cikin fushi Azmerh ta ɗauki Jakarta da mayafinta ,tare da janmasu dogon tsoki mtswww Kafin ta furta
"Allah ya isa na!
Allah ya isa na!!
Allah ya isa na!!! Har sau uku
sannan ta nufi hanyar fita daga cikin parlourn Tare da ficewar, daga gidan gaba daya
"Cikin daga murya FAREEDAH tace"Azmerh dan Allah kiyi hakuri ki dawo ,"NABEEL yace
"FAREEDAH dan Allah ki kawo min abinci ,ki rabu da 'yar iska, yar rainin hankali kawai
"Cikin sauri