x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 12 - MAJNOON

  • 33001 words
  • 36000 words
  • Out of 47364 words

Category: Romance Story +18

Views 125

02 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
103 and 104
Via *OHW*
_A love story_πŸ’

Suna karasawa airport sukayi sa'a kuwa jirgir safe bai tashiba, nan suka shiga.... suka lula zuwa abuja..
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Rumaisa tana zaune a daki, tare dawasu kawayenta su biyu, leemart da kuma maryam, suna fira, amma ita sam zuciyarta bata gurin, tunani takeyi ashe daman burinta zai cika akan MAJNOON, yau za'a daura mata aure tare da kabir (Majnoon) tazamo mallakinsa shima yazamo nata, daman hausawa sunce komai yayi farko zaiyi karshe

Maryam ta dafata, ta baya, saida ta zabura "waike tunanin me kike ne, tun dazu muke miki magana amma kinyi shiru"

Rumaisa ta sosa kanta, cike da jin kunya tace "amm bakomai, me kikace ?"

Maryam tace " cewa mukayi kitashi kije kiyi wanka kingafa lokaci yana tafiya"

Murmushi rumaisa tayi sannan tace "Tohm shikenan kujirani yanzu zanfito" tana gama fada tamike tafada toilet,
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Abba kuwa tuni yayi wankansa cikin farara shadda, sai fara,a yake, anata shirye-shirye fara daura aure,

umma ma tasha ado, ita da haj luba sunyi kyau abinsu, yau farin ciki ya yawaita a gidan abba,
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Kabir kuwa tunda yatashi a safiyar yau yakejin gabansa nafaduwa,

Duk yakasa sakin jikinsa, musan mamma dayaji labarin cewa yaune aurensa,

Tun jiya abba yakai masa nasa kayan dazai saka, yayi wanka yafito yazo yayi tsaye a tsakiyar daki, shifa yanzu komai yadaure masa kai, a duk lokacin dayaji anyi maganar auren nan sai gabansa yafadi, yarasa dalilin yin hakan,

Yayi tsaye a bakin mirror yana kallon kasan, bansan meya tunaba sai kuma naga yayi murmushi, sannan yafara shafa mai, bayana yagama,

Sannan ya shirya shima cikin farar shadda tasha aiki, tana kalli, yasaka hula baka, takalmi bakake, abinka da farin mutum saifa yafito tas dashi, yayi kyau sosai...
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
9:30
Motoci sai parking sukeyi a kofar gidan abba, yafito waje yana tabar baki cike da fara'a, duk da auren na boyene amma saida mutane suka taru sosai, domin abba mutumen mutanene, harabar gidan abba tacika sosai, saura mintuna kadan a fara daura aure, koshi dan daddy baya nan ne yatafi airport dauko faisal ...
β–‘β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
*Airport*

Jirgi yadira a airport dake abuja, cikin gaggawa su faisal suka fito, daman daddy yakaraso shima su yake jira duk ya kagu suzo, domin yaga lokaci yana tafiya,

Tundaga nesa faisal ya hangi daddy, da sauri suka karaso gurinsa, faisal yayi hug dinsa cike da fara, "you're wll com my son" faisal yayi murmushi yace " thanks daddy, faisal ya nuna adnan dake tsaye a bayansa yace "daddy wannan aboki nane sunansa adnan"

Cikin gaggawa daddy yace " oya let's go, daga baya idan an gama dauren auren mayi magana a gida, kushiga muje lokaci na tafiya"

Nan suka shiga mota, daddy yajasu suka nufi gidan abba..
β–‘β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Mutane sai kara taruwa suke, Abba yashiga cikin gida yafito da kabir ango, domin lokacin daure aure yakusa, Su daddy kawai ake jira,

Rumaisa kuwa bayan fitowarta daga wanka, kawayenta suka fara shiryata, suka tsara mata kwalliya mai kyaun gaske,

Sannan akaje ga sutura ananfa akasha rigima domin ko wacce aka dauko sai rumaisa tace ita bata yimata ba, itadai tafison a yau dinnan tafi kyau fiye da kowace rana,

Da kyar dai aka samu tazabo kala daya, sannan tasaka, tabbas tayi kyau sosai kamar ba itaba, leemart tayi dariya tace " amarya ansha kamshi, kinyi kyau abinki" murmushi kawai rumaisa tayi, suka kwashe dadari, maryam tace " nimadai baza'a barni a bayaba, saina tsokano magana, amarya bakya laifi kokin kashe dan masu gida" su duka suka kwashi dariya harda rumaisa, haka dai sukaci gaba da zolayarta ita kuwa sai faman murmushi take musu.. (amaryar Majnoon😜 )
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Motar daddy ta ja parking a bakin kofar gidan abba, tun a lokacin adnan yakejin gabansa na faduwa,

Daddy da faisal suka fito suka barshi a cikin motar yana tunani, harsun fara tafiya faisal yaduba yaga babu adnan da sauri yadawo bakin motar ya leka, yaganshi zaune yayi jugum, faisal yace "fito muje mana"

Saida adnan ya dan zabura yace "to...to" sannan yafito suka nufi kofar shiga gidan, a lokacin har daddy yashige ciki, gaban adnan sai faduwa yake,

Suka tura kofar gidan suka shigo, nan suka tarar da mutane zazzaune, sukayi tsaye suna kallonsu, faisal ya dube adnan yasauke murya yace "cab di jan, to yanzu taya za'ayi mufita da shi"

Adnan yayi ajiyar zuciya yace " hmm nima ina nasani, niko ganinsama banyiba"
Faisal yashiga leka taron yana fadin " bari na duboshi" nan ya d'aga yashiga neman Majnoon, yabar adnan tsaye a gurin, zuciyarsa sai saka masa take taya zai kashe majnoon batare da faisal yasaniba, haka dai yayita sake-sake.. yana neman mafita
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Kabir yana zaune akan kujera, kwata- Kwata yau bayajin nishadi, baisan komeye dalilin hakan ba, jin anfara adu'ar daurin aurensa, yasa yaji kansa yafara sarawa, nan take edonsa suka chanza launi zuwa ja, duk jikinsa yadau gumi, tashi yayi dasaurin yana kokarin komawa cikin gida,

A daidai lokacin faisal ya hangesa, da sauri ya kad'a hannu yace " yes!! Nagansa" sannu yafada, sannan yakarasa gurinsa,
Assslamu alaikum" ya tsayar da kabir tare da mika masa hannu sukayi masubaha, sannan kabir ya amsa masa,

Yana murmushi yace " sunana faisal, amm munzo ne nida abokina domin mutayaka murnan aurenka, mubakine daga kogi state"

Da karfi kabir ya zare edo, kwakwalwarsa tarika juyawa kamar zai iya tuna sunan, kamar yasan sunan, amma sai kuma yakasa tuna komai,

Faisal yariko hannunsa yace" muje koh,

Kabir yabishi da kallo, suka nufi kofar fita,

Adnan dake tsaye a bakin kofa, tun daga nesa yake hangosu,
Kallo daya yamasa yazare edo, duk jikinsa yadau rawa tabbas yaya Mubarak yana raye, mummunan tashin hankali ya ziyarci zuciyarsa, duk ya fita hayyacinsa, gumi yasoma karyo masa,

Tafiya suke suna Magana ammashi bayajin abinda suke fada, tun daga nesa Faisal ya nunawa kabir, gurin da adnan yake yace " ga abokinan ce sunansa adnan"
Da karfi kabir ya dago kansa ya dube gurin da faisal ke nuna masa ,

Tunda edon kabir suka fada kan adnan, yaji wani irin zirr kwakwalwarsa ta dauka; daga hannu yayi yadafe kansa saboda mummunan cewon dayake masa, yana kokarin nuna adnan, jiri yasoma dibarsa saboda zafin da kwakwalwarsa take masa, kad'an yayi ihu, a hanakali yake sulalewa kasa yafadi wanwar,

Daddy dake zaune acikin taro, yana kallon duk abinda suke, amma shi bai lura da adnan ba,sulalewar Kabir kawai yagani, da karfi yace " innalillahi wa inna ilaihin raju un" nanfa kaga kallon kowa yadawo kansa ana tambayarsa lafiya, dasauri yamike yanufi gurin su kabir, mutane suka bishi da kallo, kabir yana kwance a kasa a some, faisal ya durkusa kusa dashi, yana girgiza shi, duk ya tsorata, yarasa meke faruwa,
Daddy ya karasa kusa da faisal,
Ganin halin da ake ciki yasa mutane suka yo kansu, sai salati ake, hakalin kowa yatashi,

Cike da firgita adnan ya juya da gudu yafita yabar gidan, domin yasan dacewa yanzu kam komai yachabe, duk ya fita hayyacinsa, yana fita yayi daidai da wani mai napep yashigo layin da sauri yataresa , tare da umurtarsa daya kaisa airport, ba musu mai napep din ya tada napep suka wuce airport
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Koda faisal yajuyo gefe adnan yaga wayam, babu adnan babu labarin, abin yakara daure masa kai, waishin meke faruwane, kodai hakan yana nufin cewa wannan shine yayan adnan, kansa yake tambaya,

Daddy yasa aka kwashi Kabir akayi asibiti dashi, β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Rumaisa tana cikin daki ita dasu leemart, suna tsokanarta, umma tazo tasanar da ita mummunan labari, bakaramar firgita tayiba, taso taje asibitin amma umma ta hanata domin tasan idan taje bayan kuka babu abinda zata musu, haka ta hakura tazauna gida...
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Bayan ankarasa dashi asibiti likitoci suka karbesa suka bashi taimakon gaggawa,

Cikin kakkanen lokaci suka gano matsalarsa, sun gano cewa babu abinda ke damunsa, sock ne kawai yadibesa, nan bada jimawaba insha Allah zai farka...
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
Yana karasa airport cike da firgita ya sallami mai napep ko chanji bai tsaya karb'a ba, yakara shiga jirgi, yakoman kogi, tun suna cikin jirgin yake kuka duk ya tsorata,

Yau kam asirinsa ya tono, ya matsu bai karasa kogi ba yasanar da ummansa cewa tabbas Mubarak yana raye

bada jimawaba kuwa suka karasa kogi....

Waya ganemun edon umma taji lbrn Mubarak yana raye😜

https://free.facebook.com/Abdul-Mr-Smiles-Novels-220980808286357/?v=feed&_rdr
[10/20, 10:52 PM] β€ͺ+234 905 395 7618‬: _Title:-_ *MAJNOON*😴
_The mad man_

_Author_:- *MR, SMILES*πŸ˜ƒ

105 and 106
Via *OHW*
_A love story_πŸ’

Ana ajiyesa filin jirgi, Bai tsaya akazo daukar saba, taxi yashiga yakaraso gidan da shigowarsa cikin gidan yanufi sashen haj zainab cike da tashin hankali,

Tun bai karasaba yake kiran sunanta, dasauri tafito daga dakinta tana murna a tunaninta sunyi nasarane akan Mubarak,

Sunacin karo dashi taga yana kuka cike da firgita tace "adnan lafiya kuwa"

Adnan yakara fashewa da kuka, yana fadan "umma yau zamu mutu, wlh yaya Mubarak yana raye kuma yana ganina yaganeni"

Haj zainab ta toshe baki nta tana kokarin yin kuka tace "nashiga ukku" taja hannun adnan suka karasa cikin daki, tazaunar dashi kan gado, "kafadamun meke faruwane, garin yaya hakan tafaru" haj zainab tafada, takarasa maganar cikin hargowa

Adnan yana kuka yafara labarta mata komai akan abinda yafaruwa,

Cike da tashin hankali ta mike tsaye "karyane wlh bai isa ya hakana abinda kajima tana hasasheba, shidin banzaci uwarsama bazata iya daniba, matukar bokana yana raye, ai kamar yadda yabar gidan nan harna tsayon shekara biyu, haka zaibarka kayi mulkin wannan sa sarauta, ta juyo ta kalli adnan sannan tace " jirani naje yanzu nasanar da boka abnda ke faruwa, kazauna a daki karka fita saina dawo"
Tana gama fada sannan ta juya ta janyo mayafinta tayafa, tafita, tabar adnan nan zaune cike daki yana kuka,

Da sauri sauri take tafiya kamar ta had'a da gudu, daidai kofar falo fita sukaci karo da mai martaba saida gabanta yafadi damm, Sannan tadan daidai kanta tana ta gaidashi, ya amsa mata ya dube yace "ina zakije"

Nan take jikinta yadau rawa, cike da inda-inda tace "zanje, amm...amm...."

Mai martaba ya dakatar da ita dacewa "komadai inane, bazaki jeba domin yau inaji a jikina, kamar akwai wani abun da zai faru a gidan nan, don haka yau kowa bazai fitaba, tundaga kan 'yan aikin gidan nan harzuwa 'yan gidan nan, babu wanda zaije ko ina"

Dasauri haj zainab tace "amma ...."

Mai martaba yadaga mata hannu "banason gardama kikoma kawai bazaki jeba, yayi shiru yana kallon yadda jikin ke rawa, kamar zai tafi sai kuma yafasa yajuyo ya kalleta yace "ina adnan"

Cike da rashin gaskiya ta share gumin dake karyo mata sannan tace "yana cikin dakina" tana gama fada mai martaba yafice yabar gurin,

Tsaye tayi cike da tashin hankali, duk edonta sunfinfito, yaudai ko dubun suce tacika, take tambayar kanta,

Juyawa tayi takoma dakinta, adnan yana zaune yana kuka ya mike da saurin " harkin dawone"

Cikin sanyin jiki takai zaune kan gado " mai martaba ya hanani fita, yanzu bansan ya zanyiba, nashiga ukku" tadafe kanta tana kuka, adnan ya zauna kusa da ita shima kukan yakee...
β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘ β–‘β–‘β–‘β–‘
*Abuja*
_Bayan awa biyu_

Duk taron daurin aure kowa ya watse tsirarun mutane suka raka su daddy asibiti, suma basu jimaba suka wuce basu jira yafarkaba,

_Bayan wasu yan mintuna_

Abban rumaisa, daddy, dakuma Faisal, sune kadai a cikin dakin da Kabir yake kwance,

A hankali yasoma bude edonsa, yana nishi, hakan yasa su daddy suka karaso gurinsa, edonsa suka bude wanwar, dakarfi yazabura yana fadan "innalillahi wa'inna ilaihin raju'un" zai mike, daddy yamayar dashi zaune,

Cike dajin dadi abban rumaisa yace "bari naje nakira likita" yana gama fada yafita yabar dakin,

Kabir yadubesu duk bai sansuba, a hankali yake kallon jikinsa kafin yadago kansa ya kalli daddy yace "menakeyi anan"

Daddy yayi murmushi yace "bakada lafiya ne, ana daf da daura maka aure mukaga kazube akasa"

Gaban kabir yafadi, cike da mamaki yace "aure kuma ni, bayan wanda nakeda, yaushe nayi auren na fari, dahar za'a ace za'amun nabiyu"

Daddy yadubesa da mamaki, yaji kalamansa na masu hankaline kodau yasamu hankaline, yana murmushi yace "kabir kodai kasamu lafiya ne" yafada yana kallonsa,

Maimaita sunan yayi cike da rashin fahimta, waye kuma kabir, sai kuma yadube daddy yace " waye kuma kabir anan, ni sunan Mubarak"

Gaban faisal yayi mummunan faduwa, tabbas hasashensa yayi gaskiya, to meyasa akace ya mutu, tabbas akwai wani mummunan alamari akasa, a hankali ya furta sunan a bakinsa kamar yadda yaji adnan yana fada "yaya Mubarak"

Faisal yayi saurin cewa "kaine yarima Mubarak koh? Kanada kani adnan, sannan kuma mahaifinka mata biyune dashi, kadai sarkine"

Da sauri Mubarak yace "eh nine, suna inane"

Daddy yana mamaki ya dube faisal yace "ina kasan wannan"

Faisal yayi ajiyar zuciya yace "zuwana kogi duk nasan wannan, ko a tarihin hikaya bantaba ganin lamari irin wannan ba, acen garin kogi kowa yadauka Mubarak ya mutu, a tarihinsa dana samu cewa akayi mota ta konesa kurmus tayadda ko gawarsa ba'a samuba, saka makon hakan yasa mahaifiyarsa takamu da wani ciwo na rashinsa, saidai ni abinda yadaure mun kai shine, a labarinsa dana samu, banji ance yanada aureba, wai meke faruwa ne haka"

Kuka sosai Mubarak keyi akan wannan labarin dayaji, cikin tashin hankali yake cewa "meya faru da mahaifiyata"

Faisal yana hawaye yace "nima bansaniba, kawaidai adnan yacemun mutuwarkace ta maidata yadda take a yanzu"
yace " ina adnan?"
Faisal yace "tunda yaga kazube kasa, ya gudu, bansan inda yajeba"

A daidai lokacin abban rumaisa da likiti suka shigo dakin, jikin abba yayi sanyi sosai domin tun daga cen likita yasanar dashi cewa kabir yanasamu lafiya, likita nashigowa yakarasa gurin kabir ya dubesa yace "alhamdulillah tabbas lafiya tasamu"

Dubansa yayi cike da mamaki yace "likita wai meke faruwane nifa bangane kuba"

Likita yai ajiyar zuciya sannna yace "kayi mahaukane a shekarun baya amm..."
Dasauri Mubarak yace "hauka kuma likita? garin yaya"

Nan likita ya labarta masa komai akan abinda yasani, akan haukarsa da kuma losing memory kansa dayayi harda aurensa da Rumaisa,

Hawaye Mubarak yakeyi yana fadan "innalillahi wa inna ilaihin raju un"

Duk jikinsa yayi sanyi, jinyadda labarinsa yakasance, ya tausawa kansa,

Likita yadube Mubarak yace " kai dan wane garine, kuma meye labarinka"

Mubarak yana kuka yatsayar da kukan yace "sunana Mubarak nidan kogi state ne, inada aure mata daya dakuma yaro daya mai suna Khalid, ni bansan meye faru daniba, sai yanzu dana farka daga mummunan bacci danayi"

Abba yayi saurin cewa "yanzu kai kanada aure"

Mubarak yace "tabbas inada aure harda yaro daya"

Abba yayi ajiyar zuciya yace "tabbas nayi babban kuskure, dana hada aurenka da 'yata Rumaisa"

Mubarak yadube abbq da mamaki yace "wacece kuka Rumaisa"...

https://free.facebook.com/Abdul-Mr-Smiles-Novels-220980808286357/?v=feed&_rdr
[10/20, 10:53 PM] β€ͺ+234 905 395 7618‬: _Title:-_ *MAJNOON*😴
_The mad man_

_Author_:- *MR, SMILES*πŸ˜ƒ

107 and 108
Via *OHW*
_A love story_πŸ’

Dakin kowa yayi shiru, faisal mamakin yake to meyasa baiji labari a gurin kowaba cewa yarima Mubarak yanada mata, hard yaro, kuma meyasa adnan ya gudu, kansa yake tambaya,

Jin kowa yayi shiru yasa Mubarak yayi yunkurin tashi yana fadan "yanzu gida zankoma, zanje naga mahaifiyata da matata"

Gaban Abba yafadi, sai yanzu yatuna da maganar da haj luba take fada masa, kar wata rana yaron nan yasamu lafiya yazo ya gujemu, yan idan yatafi wane hali 'yarsa rumaisa zata kasance, Abba yana hawaye yace " dan Allah karka tafi wlh idan katafi zan iya rasa 'yata, 'yata tafada sonka so marar misaltuwa, dan Allah kataima kamun ka aureta, karna rasata ita kadai nakeda"

Dakin kowa saida yaji tausayin abba,

Mubarak yadube abba yace "bazan iya auren kowace macce ba a yanzu, nidai dan Allah kubarni na naje gida"

Faisal yayi saurin cewa "tare zamu tafi, domin inason nasan gaskiya labarinka, kuma nizan maka jagora harzuwa gurin mahaifiyarka"

Mubarak yamike tsaye yana gyara tufafin dake jikinsa yace "yanzu zamu tafi, bazan iya kara awa daya a garin nanba"

Yayi yunkurin barin dakin abba ya rike masa riga, cike da muryar magiya yace "dan Allah kafin katafi, inason kaje kaga 'yata koda sau dayane domin nasan zatafi kowa farin cikin ganin kasamu lafiya"

Ransa baisoba, sai dai kuma abba yabashi tausayi, Mubarak yace
End Ads