ta kone kumur ta yadda ko gawarsa baza a iya samuba"
Faisal yayi ajiyar zuciya yanzu kam shakkun zuciyarsa yakauyagane cewa ba majnoon bane Mubarak, domin yaji labarin cewa wannan a mota ya kone kurmus,
Kara duban adnan yayi wadda tun tuni yajima dakara tsundumawa cikin duniyar tunani, yana tunanin taya zai bullowa lamarin, ta yadda faisal bazai ganeba,
Faisal yace "to ita waccen matar fa da bata magana ta wajen falo"
Saida adnan ya zabura lokacin da faisal yayi masa wannan tambayar, bakinsa na rawa yace "mahaifiyarsa ce, tun lokacin da muka samu labarin ya kone a cikin mota, lamarin ya gigitata sosai, tun a lokaci batakara yin magana, yanzu kuwa kusan shekara byu,
Faisal ya girgiza kai matar tabashi tausayi, to mezai hana yatai maka mata, indai har ganin Mubarak zaisa tasamu lafiya, mezai hana yahadata majnoon ko Allah zaisa tasamu lafiya ta sanadiyarsa, tunda kaman nunsu daya da Mubarak dinta, duk azuci yake wannan zance a fili kuwa dago kansa ya dube faisal "ina dai taimakon dazamuyi mahaifiyar Mubarak amma fa saida tai makonka"
Dasauri Adnan yace "menene inajinka"
Faisal yace "mezai hana mudauko, mai kamannun Mubarak wanda yake abuja, mukawosa gidan nan a matsayin Yarima Mubarak"
Mamaki yayi sosai taya akayi faisal yasan kudirin daya yanke acikin zuciyarsa, shima hakan ne plan dinsa,
Jiyake yasamu hanya mafi sauki ta yadda zai kawar da majnoon,
Murmushi yayi yana kallon faisal "kamar kuwa kashiga zuciya nima hakan natsara a cikin tawa zuciyar domin muwarkar da umman Mubarak" adnan yayi shiru sai kuma ya mike tsaye yace "ina zuwa" yana gama fada yanufi hanyar fita,
Faisal yayi saurin cewa "akwai fa matsala daya"
Ko juyosa adnan baiba balle yatsaya yaji mezai fada, janyo kofar yayi da karfi yafita da gudu......
Da gudu yashigo dakin haj zainab, tana zaune ta rafka uban tagumi, tana tunanin yadda zata bullowa lamarin,
Taji shigowarsa saida tatsora data ganshi, tun bai zaunaba yake fadan umma nasan inda yaya Mubarak yake" yana kokarin zaunawa
Cike da Firgita haj zainab ta riko hannusa tazaunar dashi tana kallonsa edo cikin edo "yana ina ne adnan"
Prince adnan yana hawaye farin ciki yace " umma bakon nan dayazo yasanar dani cewa yasan inda yaya Mubarak yake, amma ban nuna masa alamar akwai wani abu dayake faruwa tsakanina dashiba, yace yanason atai makawa umman Mubarak domin tafita daga halin datake ciki"
Haj zainab ta ya mutse fuska tana hararar adnan tace "lallai wannan bakon yazo da sabon labari a gidan nan, yaushe yazo gidan kuma yaushe zuciyarsa tafara ganin umman Mubarak dahar zaice yaji tausayinta, toh idan sammakon taimako yake, mu a hanya muka kwana, kafin ya tai maka mata mukuwa munsamu munyi awon gaba da Mubarak, yaushe zakaje abuja ?"
Adnan ya dube haj zainab fuskarsa a murtuke "idan yauma kikace naje, yanzun nan zan tashi natafi"
Haj zainab tayi saurin cewa "a a ba yanzu ba, domin yanzu nasan dacewa mai martaba bazai barka kaje ko inaba saboda raunin dake jikinka, mubar wannan maganar sai na da sati daya, amma inason kahanawa bakon nan fadawa kowa wannan magnr, kasan duk yadda zakayi kamasa dabara, kafin nan zuwa sati daya"
Cike da inda2 adnan yace "umma ni bansan mezan masaba"
Haj zainab ta ja tsaki "kai matsalta dakai kenan, komai baka iyaba sai an koya maka, to kawo kunnen ka kaji"
Adnan yayi murmusshi sannan ya tura kunnensa kusa da bakin haj zainab, nan tashiga rada masa magana"
Sundan jima suna maganar kafin adnan yajane kunnensa yana murmushi yace "hakan za'ayi umma"
Haj zainan ta girgiza kai "haba kokaifa,
Sai kuma sukadanyi shiru, suna nazari wani abu , haj zainab tace "yanzu tashi kaje dakin ka kwanta, domin kasamu karfin jikinka"
"Toh" kawai yace mata ya mike tsaye yafice yabar dakin,
Koda yakoma dakinsa bai tarar da faisal ba , a hankali bakinsa ke furta "shikuwa wannan ina yayafi" tabi baki yayi bayan yagamaa maganar, yakarasa bakin gado yakwanta,
โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ โ
Faisal kuwa bayan fitar adnan, yaga yajima bai dawoba, zuciyarsa ta yanke masa shawara kawai yaje yafada umman mubarak cewa yaga yaronta,
Haka kuwa akayi kawai yatashi yafita, yana dube2 ta wacce hanyace suka tarar da umman Mubarak, yajima yana yawo a cikin gidan kafin yagano hanyar..
Tafiya yakeyi cikin natsuwa da kamala, harya karasa tangamemen falon da umman Mubarak ce kadai a ciki tana kallo photon dake manne a ginin dakin"
Karasawa yayi kusa da ita, yana kallonta yayi murmishi, yaga ita ko motsa edonta batayiba,
Tausayinta yakeji har cikin zuciyarsa, durkusawa yayi kusa da ita ya rike keken guragun datake zaune yayi gyaran murya sannan yace "inada labari akan yaronki Mubarak" yana gama fada sai kuma yayi shiru yana kallonta,
Duk inda jijiwowin jikinta suke saida suka motsa, bugun zuciyarta yakara karfi, yana rike da keken yaji keken yafara rawa a hankali yadago kasan yana kallonta , a daidai lokacin hawaye suka soma fita acikin edonta, a hankali take dago kanta tana kokarin furta magana sai kuma takasa,
Makwogaronta yasoma zafi, tari tasoma yi babu kakkatawa, kamar ranta zai fita, faisal ya mike tsaye cike da tsoro, yana fadan " lafiya kuwa meke faruwane"
Itakam tari taci gaba dayi da karfi sosai harsaida ta fado daga kan keken datake zaune, faisal yace " oh shet" nanfa yaji tafiyar mutanen suna kokarin shigowa gurin.....
Dasauri ya gudu yasami guri ya labe bayan kofar falon suna shigowa shi kuwa yafita da karfi, da gudu yakarsa dakin da aka saukesa,
Yana shiga dakin yafada kan gado yana sauke nunfashi,
Gabansa sai faduwa yake, Allah2 yake kardai ace shine silar tashin ciwon umman Mubarak, tunani barkatai suka rinka zomasa,
Ma'aikatan nashiga gurin sukaga halin datake ciki dasauri suka je suka sanar da mai martaba,
Cikin firgita ya iso falon ganin halin datake ciki yasa yayi saurin kiran dr bukar domin shine family doctor nashi,
Bada jima wataba kuwa dr bukar yakaraso, yadubata sannan yayi mata allurar bacci, saida ya tabbatar data samu sauki sannan yabar gidan,
Bayan fitar dr bukar, Mai martaba ya dube ma'aikatan cikin bacin rai yace "waya shiga sashenta"
ma'aikatan sukace su wlh basuga kowa yashiga ba,
Ajiyar zuciya kawai mai martaba yayi sannan yace su fice subashi guri, haka kowa ya watse akabar mai martaba shikadai yayi tsaye yana kallon umman Mubarak, yajima yana kallonta kafin shima yafita yabar dakin...
*BAYAN KWANA BIYU*
ABUJA
Majnoon yasamu sauki sosai, sun saka masa suna *kabir* haka suke kiransa, shikuwa yana amsawa,
Suna bashi kulawa sosai, A duk lokacin da akayi masa maganar aurensa da rumaisa, toh komai farin cikin dayake nan take farin cikin zai gushe,
Hakan yasa aka daina masa maganar auren, saidai kullum rumaisa tana tare dashi , abubawa kawai take koya masa, tasamu farin ciki sosai atare dashi,
Yauma kabir yana zaune akan gadonsa na jinya, rumaisa tana zaune kusa dashi, tana masa bayanin yadda ake alwala, har suka kammala, kuma yana fahimta sosai,
Rumaisa tayi murmushi tace "Yanzu dai kasan yadda akeyin alwala saura sallah, tayi gyaran murya, a lokacin suka hada edo tayi masa murmushi shima yamata, sannan tace "ita kuwa sallah idan zaka farata, zaka fuskanci alkibla, tadago kanta ta kallesa tace " kasan meye alkibla" kai kawai ya girgiza mata alamar baisaniba yana murmushi, tace "gabas itace alkibla, tanuna gabas da yatsanta,sannan taci gaba cewa "bayan ka fuskanci alkibla sai kuma kayi ikama...." tana batun fara karanto masa ikama
Sukaji a turo kofar dakin anshigo, suka tsayar da karatunsu, suna kallon mai shigowa, abba ne yashigo da takarda a hannunsa, ya dubesu yayi murmushi yace "saiku tashi kushirya muwuce gida domin likita ya sallamemu" yakarasa maganar yana dariya,
Rumaisa tajidadi sosai, ta dube majnoon tace "kabir zakaje gidanmu"
Girgiza mata kai yayi "eh zanje mana, ai gidanku gidan mune"
Nan fa suka shiga hada kayansu, umma da haj luba suka tayasu aka hada kayan sannan suka fita, bayan sun fita suka saka kayan a mota, sannan kuma kowa yashiga motar, Abba yaja motar suka nufi gida,
Bayan sunkarasa gida, abba yabawa kabir daki daya daga cikin dakunan dake gidan, tare da nunnuna masa komai na gidan,
Haka dai suka wuni cike da farin ciki da walwala,
Bayan sallar isha, suka taru a falo suna fira cikin nishadi da kwanciyar hankali,
Abba yakatse musu fira dacewa "munsaka ranar auren rumaisa da kabir nanda sati daya, me kukace?"
Haj luba tayi saurin karbe maganar cike dajindadi tace " hakan yayi, domin ni na matsu babbar garin nanba, banaso natafi banga auren 'yar jikan tawaba, Allah yatabbatar mana da alkhairi"
Duka falon suka amsa da ameen,
Rumaisa tana kwance akan cinyar umma, ta rufe fuskarta saboda kunya,
Kabir kuwa yana zaune akan kujera, tunda abba yayi maganar aurensu, yaji kansa na sarawa, kwakwalwarsa nai masa zafi, da sauri ya mike tsaye yabar falon, suduka suka bishi da kallo, sun kasa fahimtar lamarinsa, a duk lokacin da aka dauko zancen aurensu, sai kawai suga ya canza yanayi, wani lokaci kuwa saiya tashi yabasu guri,
Babu wanda ya furta ko uffan, domin inda sabo sunsaba da wannan halin nasan,
Sundan taba fira kadan sai kuma suka watse kowa ya nufi dakinsa...
Washe gari
Abba yasa akafara gyaran daya daga cikin gida jensa, inda rumaisa da kabir zasusha amarcinsu,
Umman mubarak tasamu sauki sosai amma dai haryanzu ba abinda ya chanza akan rashin lafiyarta , mai martaba yasa aka maidata falon da take ciki,
Taci gaba dazamanta domin tafison zama cen fiye da ko ina, acikin gidan
Faisal da adnan sun shaku sosai, kullum sai adnan ya fita yawo tare da faisal, domin yasamu ya gusar masa da tunanin fadawa wani labari akan Majnoon,
Kullum suna waje, idan kaga sundawo gida to sai dare idan sunzo bacci,
Kwanan faisal biyu a dakin da mai martaba yabashi,
A rana ta ukku, prince adnan ya umurcesa akan cewa yadawo dakinsa da kwana,
Duk dai sunyi hakanne dandai kawai su gusarwa faisal da tunaninsa daga fadawa wani labarin Majnoon,
Dominsu sunaji a jikinsu cewa shine Mubarak, ba wani mai kamadashi,
Yau dadare bayan sundawo daga yawonsu, dakin adnan suka dire,
Faisal yazaune kan gado yana nishi "waii wlh yau dukna gaji, kasala nakeji" yafada yana kokarin kwantawa,
Adnan yayi murmushi yace " hmm nima wlh nagaji, amma dai bazan kwantaba sainayi wanka"
Tabe baki kawai faisal yayi "uhim kaika sani nikam wanka saida safe, Allah bazan iya tashi ba yanzu"
Adnan yayi shiru yana murmushi, sai da yagama cire kayan dake jikinsa, dagashi sai singlet da boxer, ya juyi ya kalli faisal yace "yawwa daman mantawa nayi ban fadamaba "
Faisal yadago kansa "eh menene "
Adnan yace " daman umma ce tace, sati mai zuwa muje abuja muzo da wancen mutumen maikama da yaya Mubarak, "
Faisal ya koma kwance yana cewa "tohm shikenan Allah yakaima, sai kuma yadago kansa ya dube faisal yace "saidai kuma akwai matsala"
Dasauri adnan yace "matsalarme fa"
Faisal yace " daman naso nasanar dakai cewa shifa waccen mutumen, yanada matsala domin ya manta da komai daya taba faruwa dashi a baya, ma'ana yakamu da cutar amnesia"
Gaban Adnan yayi mummunan faduwa, awani bangare kuwa dadi yaji, domin ayanzu yanada damar dazai tunkare majnoon babu fargana tunda yamanta komai,
Ajiyar zuciya yayi, zuciyarsa cike da farin ciki sannan yace " ba cutarsa bane damuwarmu, damuwarmu shine munemawa umman Mubarak lafiya, domin na tabbatar dacewa tana ganinsa zata samu lafiya, bayan tasamu lafiya daga baya mayi mata bayani, wlh ni matar tausayi take bani" yakarasa maganar cike da makirci,
Faisal yace "toh shikenan nima ina goyon bayanku dari bisa dari, kuma zan baku duk wani taimako, daya dace, Allah yakaima sati mai zuwa"
Adnan yace "ameen, nidai na zanshiga wanka saina fito"
Yana gama fada yanufi toilet,
Faisal yayi yaja nunfashi sannan yajanyo filo yagyara kwanciyarsa,
Zuciyarsa cike da tausayin umman Mubarak,
Tun kwanan baya daya shiga sashen umma Mubarak yatayar mata da ciwo, tun daga ranar bai kara shiga sashen ba tsoronma zuwa gurin yake domin baya sonma taganshi....
Murmushi abba yamusu, suma sukai masa, yakaraso kusa dasu yayi tsaye a kansa yace "karatu kawai kukuyi"
Rumaisa tace "wlh kuwa ai mumma kusa gamawa"
Abba yayi murmushi yace "yawwa hakan yanada kyau" sai kuma yadanyi shiru kafin yace "amm daman maganar auren kune gobene, kuma ni banason yawan taron jama'ar nan, nasa angayyatomin malamai sannan kuma abban faisal shizai wakilci kabir a gurin daurin auren, sannan kuma cikin harabar gidan nan nakeson adaura auren, dan haka idan kinadawa wasu kawaye dazaki gayyato saiki sanar dasu, amma fa bada yawaba"
Farin ciki gabaki daya ya lullube rumaisa, tana murmushi race "ni abba banida wasu kawaye da yawa, yan skull dinmune kadai, kuma bazasu wuce mutum biyarba, sannan kuma suduka nasanar dasu"
Abba yace "yawwa hakan ma yayi"
Kabir ya dube abba yace "abba ni ina nawa abokanai"
Murmushi abba yayi sannan yace "gamu! ! ai mune abokananka, kuma danginka, kakwantar da hankalinka, kaji?" Abba yakarasa maganar yana kallonsa yana dariya,
Kabir ya girgiza kai,
Sannan abba yafita yabar dakin, yabarsu sukaci gaba da karatunsu,
sannan yadauko wayarsa yakira daddy faisal yasanar dashi cewa kafin 10:00 yakirawo malaman gabaki daya su hallara a harabar gidansa, zuwa karfe 11:00 a daura aure,
"Toh" kawai daddy yace sannan suka kashe wayar,
Suna kashe wayar daddy yakira faisal,
Yana kwance a cikin blanket yana bacci mai dadi, yaji wayarsa tadau kara, a hankali ya zuro hannunas yadauki wayar yakara a kunnesa, batare daya duba wayake kiraba,
Hello son" shine sautin daya daki kunnensa, sai lokacin yasan da cewa daddy ne kekira, cikin muryar bacci yace "daddy antashi lafiya"
Daddy yace "lafiya lau, amm daman tun jiya naso nakiraka nasanar dakai cewa yaune daurin auren rumaisa ita da wanna marar lafiyan"
Wani irin mummunan faduwar gata ya ziyarci faisal, da karfi yace " what! !!, da sauri yaye blanket dinda ke jikinsa, daddy yace " lafiya kuwa meke faruwane "
Cikin gaggawa faisal yace "daddy ina zuwa ..." da sauri ya tsinke wayar, yace "ohh shet"
Juyawa yayi gefen adnan, dake bacci sai kwasar minshari yake yasamesa yana bacci, da karfi faisal yake bubuga kafarshi yana kirana sunansa, "kai tashi akwai matsala"
A hankali yake bude edonsa ya dube faisal yace " lafiya kuwa ?"
Faisal yace " ina kuwa lafiya, yanzun nan daddy ya kirani wai yaune za'a daura auren, mutumen abuja mai kama da yayanka Mubarak,"
Da karfi adnan yamike cike da tashin hankali yace "ehhh, nashiga ukku" cikin gaggawa faisal yace " yadace ace mun isa garin abuja kafin a daura auren nan, domin kasan idan aka daura auren nan baza a barmu muzo dashiba"
Adnan yace "hakan za'ayi maza jeka dakinka kayi wanka nima yanzu zanshiga nayi wanka anan " dasauri adnan, yafada toilet,
Shima Faisal yakoma dakinsa yashiga wnka, bawani wankan kirki adnan yayiba domin duk ya tsorata, yana fitowa cikin gaggawa yasaka kayansa, yana gamawa yanfi dakin ummansa,
Yana shiga dakin yatarar da ita zaune akan sallaya, nan yashiga fada komai dake faruwa, bakaramar firgita tayiba, cike da tashin hankali tace " bazakuje a mota ba, jirgi zaku hau yanzu yasaukeku abuja, kushirya maza kuje airport kafin mai martaba yatashi daga bacci"
Haka kuwa akayi bayan sun gama shirya duk yadda abin zai kasance,
Atare suka fito shida umma,
Koda suka fita suka tarar da faisal tsaye a bakin kofar dakin adnan, shima haryazo bai gansa cikin dakinba shine yatsyawa waje yana jiransa,
Nan suka wuce zuwa harabar gidan, driver yadaukesu a moto ya lula dasu zuwa airport....