Umma tayi murmushi sannan tataimaka mata takarasa tashi tsaye,
Faisal dake tsaye a gefe duk mamaki yacikashi waye shi wannan majnoon din dahar fadar sunansa zai saika rumaisa dariya da farin ciki haka, kodai shine wanda takeso?
Basu kula Faisal ba har suka fita daga cikin dakin suka nufi dakin jinyar majnoon,
Faisal ya tsaya turus yana mamaki, zaiso yaga wanda rumaisa takeso, yaga dame yafishi,
Kasa hakura yayi dole yabi bayansu,
A tare suka shiga dakin umma da rumaisa, sai kuma ga faisal a bayansu,
Hajja luba, likita , da kuma abban rumaisa duk suna cikin dakin,
Majnoon ya dube mutanen dake zagaye a dakin yana mamakin suyawe su,
Edo kawai ya kura musu yabisu da kallo
Likita yakarasa kusa dashi yace "ya jikin naka, me kakeji a yanzu"
Majnoon ya dube likita yana mamaki, muryarsa na rawa yace "miya samenine "
Likita ya sauke ajiyar zuciya, a lokaci yatuna matsalar ciwon mantau da kedamun majnoon, sannna yace "kasamu hatsarine akan titi"
Cike da mamaki majnoon ya ke maimaita maganar "nasamu hatsari" ya dube likitan yace "a ina nayi hatsari, kuma a yaushe, suwaye wa dannan" ya nuna su abban rumaisa,
Likita ya dube su abban rumaisa yayi murmushi sannan ya juya gurin majnoon yace "wadan nan yan uwan kane"
Majnoon yakara maimaita maganar " 'yan uwana kuma?, ni harda yan uwa nake dasu"
Likita yace "sosai makuwa "
Majnoon duk komai yadaure masa kai a hankali ya dube likita yace " Waye ni ?"
Gaban kowa dake cikin dakin saida yafadi...
(Nimadai mamaki likitan yabani, sai kace ya manta da dacewa majnoon ya manta komai)...
Likita ya juyo ya kalli abban rumaisa, cike da tsoro wace amsa zai bawa majnoon,
Dakin yayi tsit, majnoon sai kallon su yake, rumaisa kuwa duk jikinta yadau rawa, tana fargabar kar majnoon yakasa fahimtarsu,
Wata idea tafadowa likiti, dasauri yace "amm wannan sunansa abba, ya nuna abban rumaisa yana murmushi
Sannan yajuya gefen umma "wannna kuwa sunanta umma" ya nuna umma,
Sai kuma yakara juyawa gefen hajja luba "wannan kuwa sunnan ta kaka" ya nuna hajja luba,
Yana kai ga rumaisa sai kuma yayi shiru, taya zai yiwa majnoon bayanin cewa wannan itace masoyiyarsa mutumen dako kansa baisaniba,
Likita ya nuna rumaisa yace "wannn kuwa itace matarka"
Gaban majnoon yafadi, da sauri yamike zaune yana kokarin tashi, likita yamaidashi kwance yadafe kansa, har saida yayi kara kadan, wani irin zafi yaji kwakwalwarsa tafara dauka, yana nishi kadan kadan, edonsa suka rikide zuwa jan launi,
Likita yace "lafiya kuwa, meke faruwa"
Majnoon ya dago kansa da karfi ya kalli rumaisa yace "ina yarona,,,,"
Tashin hanakali ya ziyarci zuciyar rumaisa, jitakeyi kamar ta zube a gurin, tambayar kanta take, me yake nufi da ina yaronsa, kardai ace majnoon yanada aure,
Rumaisa tasoma ganin jiri, habar bakinta tasoma rawa kamar zatayi magana, likita ya kifta mata edo, alamar tayi shiru,
Likita yayi saurin yin mumushi ya dube majnoon yace "ai bakuyi auren ba tukunna kafin kusami yaron"
Majnoon yayi shiru kamar mai nazarin wani abu, sai kuma yajuyo yaci gaba da kallon mutane,
Kan abba kallonsa yatsaya, yakurawa abba edo sosai, cikin saukankiyar murya yace "abba naji kowa an fadi sunansa amma ni banji anjira sunanaba, meye sunana"
Abba da duk ya tsorata da lamarin majnoon, cikin inada2 yace "amm ...umm..sunanka....ammm."
Likita yakarbe maganar dacewa "sunanka *KABIR*"
Majnoon yayi dariya yana maimaita sunnan sai kuma yayi shiru, ya koma kwance,
Likita yayi ajiyar zuciya sannan ya juya ya dube abba yace "muje waje zamuyi magana" yana gama maganar yafita yabar dakin, abba yabi bayansa,
A office suka karasa, bayan abba yazauna likita yace "saidai kuyi hakuri domin shi a yanzu komai sabone a gurinsa, saikun dinga nuna masa abubuwa, sannan kuma kusaka rumaisa ta shiga jikinsa sosai ta yadda zai saba da ita, kafin ranar aurensu"
Ajiyar zuciya abba yayi ya duban likita " toh shikenan likita insha Allah zamu kiyaye"
Likita yace "yawwa, zuwa nan da kwana biyu idan yakara samun sauki zamu iya sallamarku"
"Tohm" abba yafada yana kokarin tashi, yafita yabar office din,
A harabar asibitin sukayi kicibus da faisal yafito yana kokarin gita daga asibitin,
Kala baicewa abba ba, yasa kai yafice abinsa,
Abba yatsaya yana kallonsa cike da mamaki, girgiza kai kawai yayi yakara dakin jinyar Kabir (majnoon),
■■■■■■■■■■■■■■■
Koda faisal yafita zuciyarsa cike da k'una da kuma wasu wasi kala2,
Daman akan wannan ne rumaisa takasa karbar soyayyarsa,
Toh me wannna yafishi,
Motarsa yashiga, ya kunna, Sannan ya hau hanyar komawa gida, amma duk hankalinsa yana kan majnoon, duk sai yaji garin yafita ransa, zaiso ma ace a yanzu yabar garin,
Tun acikin mota yayanke shawarar bazai kwana a garin abuja ba, domin yaga abin yazo masa wani iri, daman duk akan mahaukaci ne Rumaisa take wannan abun,
Daddy bai hanashi adu'a kawai yamasa yace Allah yakaisa lafiya,
Sannan yajuya zai fita momy ta kwalla masa kira yajuyo, tace "dan Allah faisal karka saka damuwa da tunani a cikin zuciyarka idan kaje cen" yayi murmushi yace "insha Allah momy bazan yi hakanba, kudai kawai kutayi da adu'a"
Nan dai sukayi bakwana cike da kewar juna, sannan yafice yabar dakin
Yana fita harabar gidan yakarasa bakin motarsa yasaka kayansa a but sannan yashiga motar yatada yafice yabar gidan,
Tafiya takeyi yana hawaye duk tunanin rumaisa ya hanashi sukuni, tukin kawai yake amma hankalinsa gabaki daya baya kan tuki,
A hakan yaketa tsala uban gudu akan titi, yafi rabin tafiyarsa dare ya raba sosai,
Ta hasken motarsa yake hango kamar Mutune kwance cikin jini, babu nunfashi a tattare dashi, a yashe a gefen titi, sassauta gudun motarsa yayi harya karaso gurunsa, yatsaya yana kallon mutumen, kamar bazai fitoba,
Jin wurin yayi tsit babu alamar motsin mutum, ko dabba hakan yasa ya bude kofar motar yafito amma har alokacin jikinsa rawa yake,
Yakarsa kusa da mutumen yana kallonsa, babu alamar harbi ko alamar sukar wuka a jikinsa,
Durkusawa yayi a gaban mutumen yadora kunnensa akan kirjinsa, sai yaji kijirin na duka a sannu2, zuciyar mutumen tana harbawa,
Da sauri yamike yana mamakin meya sami wannan mutumen,
Jiyayi yanason yatai maka masa domin yabashi tausayi, kuma mutumen yana bukatar taimakon gaggawa,
Tallabosa yayi yasakashi a motarsa sannan ya shiga motar yatada yabar gurin,
Gudu yakeyi yana juyowa yana kallon mutumen, ko zai farka amma sai yaji shiru.. haka dai yaci gaba da tafiyarsa
Kusan asuba yakarsa cikin garin kogi,
Da shigarsa bai tsaya ko inaba ya zarce asibiti,
Cike da tsoro yakarasa cikin asibitin,
A nan yayi kicib'us da wani doctor yana kokarin fitowa daga wani daki,
Dasauri yasha gabansa, doctor yace "malam lafiya"
Faisal yace "ina tare da marar lafiyane, tun jiya yake a some har yau bai farkaba"
Dr bukar yace "subhanallah yana ina"
Faisal ya nuna kofar waje sannan yace "yana cikin motana "
Dr bukar yace "to yanzu zan saka nurses subiyoka da gado aje a daukosa kafin naje nadauko wani abun a office"
Kai kawai faisal ya kad'a masa
Da sauri Dr bukar yasaka nurse suka janyo gado aka biyo bayan faisal
Suna karasawa bakin motar yiya sauri ya bude musu kofar motar,
Suna ganin wadda ke cikin motar kwance cikin jini suka zare edo, suna mamaki, daya daga cikin nurse din tace " wannan ai Prince Adnan ne " dasauri kaji sauran suna fadan eh wlh shine,
Dr bukar nafitowa daga cikin office dinsa, wata nurse cikin wadanda suka dauko prince Adnan ta karaso gurin a tsorace, ta sanar da dr bukar cewa ga Prince Adnan cen a emergency room, bayi wata2 ba yabi bayanta suka wuce dakin,
Faisal yana zaune a kujera dake cikin harabar asibiti, har alokacin hankalinsa bai kwantaba duk tsoro yakeji,
Yana zaune har gare ya washe,
sannan likita yfito yana dube2 shi yake nema, dasauri yakaraso gurinsa,
"Doctor meye faradu dashi "
Dr bukar yace "dimuwace da firgita, sai yan wasu kananun raunuka dake jikinsa, amma yanzu komai nomal"
Faisal yace "alhmdullah" yana fara'a
Dr bukar yayi saurin katse masa fara'a dacewa"a ina kasamu sa ne"
Nan Faisal yamasa bayanin komai tayadda yasamu Prince adnan,
Dr bukar ya girgiza kai yace "yaron chief ne na garin nan, kuma shine kadai yaronsa daya rage masa a duniya, gaskiya zaiji dadi idan yasamu labarin kaika taimaki yaronsa, kuma nasan zai maka alkhairi sosai"
Faisal yayi murmushi yace " hakane, amma ni yanzu bashine a gabanaba, inason naje masaukinane na huta domin agajiye nake"
Likita yace "bakomai zaka iya tafiya, amma yanzun nan zan kira gidan chief domin susan halin da ake ciki, mezai hana kabayar da number ka koda mai chief yanemi yasan wanda yatai makawa yaronsa"
Murmushi faisal yayi sannan yadauki numbersa yabawa dr bukar,
Haka yayi sanadiyar dawowar mai martaba da faisal duniyar tunanin dasuka shiga,
mai martaba ya juyo ya kalli haj zainab,
Haj zainab tace " kullum kazo gurin photon nan saikayi hawaye, yakama murika manta abunda yawuce, tunda wannna yaron ya mutu adu'a itace kadai abinda yake bukata"
Mai martaba yashare hawayensa sannna yace "nima naso nayi hakan amma bazan iya mantawa da Mubarak ba, yatafi yabarni a lokacin da nake bukatarsa, Allah yajikansa da rahama"
Duk falon kaji an kwashi sautin ameen,
Shikam faisal jukum yayi yana mamaki, to idan wannan ya mutu, toshifa wancen daya baro abuja waye shi, kuma shin taya akayi wannan ya mutu, kuma a ina" duk a zuci yake wadan nan tambayoyin, yana so yasan amsar wadannan tambayoyi kafin yabar gidan nan,
A duk lokacin dataga mai martaba yana yiwa photon Mubarak kuka, jitakeyi kamar ta mutu saboda bakin ciki, amma bata nunawa mai martaba hakan, kullum cikin lallashinsa take,
hannun prince adnan taja sukabar falon suka wuce sashensu,
Bayan haj zainab tabar gurin mai martaba yasa aka kai faisal masaukinsa...
***** **** ****
Suna karasawa sashensu, dasauri haj zainab tasa makulli ta kulle kofar dakin ta zaunar da faisal kan gado tana dubansa tace "jiya kana gayamun magana saikuma wayarka ta tsinke, meke faruwane"
Cike da tashin hankali, a lokacin datayi masa tambayar a lokacin ya tuna da yadda yaga fuskar majnoon cikin jini, saida gabansa yafadi sannna yace " umma Mubarak nagani a grin abuja"
Mummunan tashin hankali ya ziyarci zuciyarta, tuni gumi yafara karyo mata, muryarta na rawa tace " Mubarak fa kace, daman bai mutuba "
Prince Adnan ya fashe da kuka cike da tashin hankali yace "ina gudu a mota zan dawo gida, akan titi wani mahaukaci ya hauro titin da karfi,ni kuwa ban anakaraba saina kad'esa, bayan nakadesa nafito domin na dubasa, shine naga Mubarak kwance cikin jini ga dukkan alamu yanzu yamutu, yadan yi shiru yana shanshekar kuka kafin yaci gaba dacewa " tashin hankali dana shiga yasa nabar gurin, tsoro da firgita suka kamani, bayan na shiga mota nakara gudu sosai domin nayi saurin isowa gida ina cikin gudu kuma wata dabba takara karamun akan titi, nayi yunkurin na kauce mata amma nakasa, kukan dukan danayi mata kawai naji amma dagashi bankara jin komaiba, bansan meya faru daniba farkawa kwai nayi naga kaina a cikin ciyawa, da kyar na iya fitar dakaina nasamu nahauro titi , ina haurowa kuma sai jiri yafara dibana naga duniya tafara juyamun nan nazube kasa, tun a lokacin bansan meya sake faruwa daniba sai kawai farka nayi nagakaina a asibiti" yaja majinar data cika masa hanci, yana kuka yashare hawayensa, haj zainab duk tafita hayyacinta, tsintsar fargaba ce karara akan fuskarta, tama rasa mezatace, duk jinin jikinta ya tsaya,
Prince adnan yana kuka yace " yanzu umma idan yaya Mubarak yadawo shikenan nayi asarar sarautar nan, saida komai yazo karshe yanzu kuma kOmai na neman jagulewa..."
Haj zainab tatoshe masa baki ta hanashi karasa maganar, tana girgiza masa kai itama hawaye take "bazamu rasa sarautaba adnan, kaine sarki a wannan masarauta, ai ta yadda muka kawar dashi tsawon shekaru biyu hakan kuma zamu kara karashi lahira, mudin bokana yana raye to insha Allah babu kai babu asarar masarauta, gobe zanje nasami boka zamuyi magana dakai idan nadawo tashi kaje dakinka, karka nunawa kowa kana cikin damuwa"
Prince adnan ya mike jiki bakwari yafita yabar dakin, haj zainab tabishi da kallo harya fita sannan tayi ajiyar zuciya ta share hawayenta, a hankali bakinta ya furta " tabbas akwai lauje cikin nadi,
Faisal kuwa yana zaune yana tunanin lamarin majnoon yaji an turo kofar dakinsa, anshigo,
Wata ma'aikaciya tashigo da farantin abinci a hannunta tazo har gabansa ta jibge masa abincin, sannan ta juya tana kokarin fita, da sauri yace "kee"
Matar ta juyo tana kallonsa " yallabai kada matsalane "
Matar ta tashe hawayenta ta dube faisal tace "koda biyana kudi zakayi bazan iya fada maka abinda yafaru da yarima Mubarak ba dimin saurauniyar gidan nan tahana kowa yabada labarinsa, duk wadda zaka tambaya a gidan nan bazai gaya maka ba, dazakabi shawarata danace maka kadaina tambayar kowa labarin yarima mubarak, domin zaifi maka sauki, kaga tafiyata " tana gama fada tajuya tabar dakin, faisal ya tsahi kamar zai bita yana kiran ta amma taki juyowa,
Bayan tafita yasauke ajiyar zuciya a hankali ya furta "ya Allah" sai kuma yafara zancen zuci " yau naga ikon Allah mutum yana raye sannan za'a rika kiransa da margayi, kodai mafarki nakeyi ba photonsa nagani bane, to idanma majnoon ba yaronsu bane, to to to.... sai kuma yakasa karasa maganar,
Shidaikam zaiso yaji labarin nan, to inama zai samu labarin kuma a gurin wa,
Prince adnan yatuna, yace "yes gurinsa zanje nafada masa gaskiya akan cewa nasan yarima Mubarak kodan yafadamun labarinsa....
Cikin sand'a yafita daga dakin, leke leke yake ta ina zaiga hanya fita, nan yaji an tabashi tabaya ya juyo da karfi cike da faduwa gaba,
Edo hudu sukayi da wanda yatabashi, faisal yayi yake yana sosar kai kamar marar gaskiya,
Ganin fuskar bodyguard din babu ko fara'a, yasa faisal yace " ina nen dakin prince adnan"
"Uhimmm" kawai bodyguard din yace masa tare da kida kansa, sannan yace "muje" yana gama fada yayi shiru,
Nan yafara tafiya faisal yabi bayansa, har suka karasa bakin kofar dakin prince adnan,
Bodyguard din ya dube faisal yace "nan ne dakin" yana gama fada yajuya yabar gurin,
Faisal yayi tsaye a gurin yakusan minti biyar kafin ya tura kofar dakin yashiga,
Zaune yasamesa akan gado ya hada kai da gwuiwa, jikinsa yayi wani suku-suku,
Dago edonsa yayi ya kalli Faisal, a daidai lokacin faisal yasakar masa murmishi tare da cewa "yallabai gurinka nazo" yana magana yana noke kai ganin yadda prince adnan ke kallonsa,
Kamar bazaiyi magana sai kuma yace "shigo zonan kazauna" ya nunawa faisal gefen gado kusa dashi,
Bayan faisal yazauna sai kuma yayi shiru, adnan ya dubesa yace " meke tafe dakai,
Faisal yayi ajiyar zuciya yanakallon adnan yace " magana cee akan dan uwanka da akace yamutu, ni ina ganin kamar yana raye"
Tsorata sosai adnan yayi, da sauri ya dube Faisal cike da firgita yace "yana ina, kasansane ?"
Faisal yace " indai har hasashena yazamo gaskiya , to tabbas nasansa, ina son insan taya akayi dan uwanka ya mutu"
Gaban adnan yayi mummunan faduwa, baya son tuna lamarin domin yana kara kunar masa da zuciya, edonsa sukayi ja sosai yadube faisal yace " kai dan wane garine"
Faisal yace "abuja"
Gaban adnan yakara faduwa, tabbas anan yayi karo da Mubarak, indai kuwa hakane to tabbas Mubarak yana raye, nan yafar zancen zuci,
Faisal ya katse masa tunani dacewa " taya akayi dan uwank ya mutu"
Cike da firgita adnan yace "hatsarin mota yayi akan hanyarsa tazuwa garin kaduna, labari kawai mukasamu nacewa ya mutu acikin motar kuma motar