x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 54 - MAR ADAMS

  • 159001 words
  • 162000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 480

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
,ana zanawa nana hauwa'u lallen mumy na yabawa "Woww gsky lallen nan yayi matukar kyau meera ai kudin lallenki yafi karfin yadda kika caza dole ma na qara miki kudi ."gabadayansu sukai dariya meera tace "na gode hajiya koda meera ta gama mata bata wuce ba dan zata tsaya tayi mata make up din zuwa wajen dinner kowacce ta kama gabanta domin shirya kanta aunty shahida tazo ta d'auki maryam  ta wuce daita domin shiryata ."

karfe uku daidai aka fara tsara wa nana hauwa'u kwaliya sosai tayi kyau cikin doguwar rigar less red wanda mumy ce ta kawo mata daman kuma ta tanada ne dan nuzla komai red tayi amfani dashi kasancewarta fara sol tayi kyau sosai abun sai wanda ya gani shima a 'bangaren hisham red din yadi yasa ba qarami had'uwa yayi ba nana hauwa'u gani take ba ya ita amma tana ganin hisham ta raina kanta saboda wani irin kyau da yayi mata ya zarta kyau sosai  ."


Tsura masa ido tayi tana kallonsa tsaye shi kuwa ko kallon inda take bai yi ba illa ma cigaba da amsa wayar da'aka kirasa yayi ,wata qawar mumy ce ta riko hannun nana hauwa'u ta kawota kusa da yaya hisham suka jero suka shiga mota zuwa hall koda suka shiga mutane suna ta d'aukansu pic jikin nana hauwa'u yayi sanyi sakamakon kalon baza da yaya hisham yake mata ji tayi kamar ta hana daukar hoton amamn bata damar aikata haka duk tajita a takure kamar ta koma gida ."


Bangaren maryam kuwa an tsara mata kwaliya ta ban mamaki tayi kyau iya kyau cikin wani hadadden lace farin anyi mata dinki weeding gwan duk wanda ya daura kwayar idanunshi akanta sai dai yace Masha allah dan kyau kam tayi shi sai daukarta a hoto ake kafin angonta ya bayyana yayinda ango na can a buge mb, salim ,yasir suna tsaye akanshi sun zuba masa idanunsu cikin tsnanin tashin hankali dan sun razana da ganin halin da yake ciki hannunsa ya kai daidai saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take bugawa da karfi yayinda gefensa hoton zanen princess dinsa ne yana kallonta yana zukar sigari."


Ahankali ya dauke gajiyayyun idanunshi da suka canza kala saboda bugawar da yayi akanta ya dan waresu akansu yaga still shi suke kallo kwalban whisky's guda uku agabansa inda yake dagasu daya bayan daya yana sha yana zukar sigari cikin tashin hankali ,idanunshi sun qara rikidewa sunyi ja sosai ,ganin bashi da niyyar daina shan giyar yasa a matukar zuciye mb ya ture cup din daga gabansa yace "why ATA ?" akanka aka fara irin wannna auren ?wallahi ka sani shan wannan abu bazai amfaneka da komai ba don't forget mami yau tana cikin farinciki kuma ta tara jamaa me kake tunani zataji idan taganka cikin wannan halin ?kana son heart attack ya kamata ne ?."


'Dago jajayen idanunshi yayi ya kalli mb bai ce masa komai ba ya kunna sigari ya kai bakinsa yana zuka yana kallon wani bangaren dabam "wannan wani irin kaskanci ne haka ATA kalli fa ,kalli irin rayuwar da ka jefa kanka daga shan sigari ka dawo giya ni har yaushe ka fara shan giya ?"ban sani ba kuma babu ruwanka da rayuwata haka ya kamata nayi ko na zama wannan ciwona ne ni kad'ai babu ruwan kowa dani ."

"why ATA? saboda wata soyayyar banza zaka kashe kanka akan wata yarinyar banza da ba gaskiya bace kana qoqarin 'bata rayuwarka, ka manta da wannan yarinyar ka kama wacce aka baka ka d'aura rayuwarka daita "salim !"ya kira sunansaa tsawace shiru salim yayi yana dubansa ya dauki kwalban giya ya kai bakinsa sai daya shanye tass sannan ya fuskancesu "akan mafarkina nake yi wannan abu ko ba akanta bane ni dai abinda nasani soyayyar da nake mata gaske ce kuma har abada domin Itace duniyata tana cikin nan  a duk inda take nasan itama tana jin yadda nike ji acikin zuciyata."


"dan allah princess ki tausaya min bazan iya rayuwa babu Ke ba , idan babu Ke bazan iya cigaba da rayuwa ba ,ya mike da kyar yana layi ya dauki kwalbar giya ya fasa sannan yace "an hadani aure da wata guntuwar yarinya ita kuma nana hauwa'u an hadata da heart attack ,ajiyar zuciya ya sauke sannan yace idan hisham ya cutar da nana hauwa'u zan yanke komai dake tsakanina dashi wallahi wallahi I promise to make his life in to hell he will end his life in prison a firgice suke kallonsa zukatansu na duka tara tara idan kuma ban kaishi prison ba zan kashesa matsawar ya cutar min da yaruwata ."

ya nufi kofar bedroom dinsa sauran kadan ya fadi mb yayi saurin kai hannu zai tarosa ya buge masa hannu yana cewa "don't don't touch me just leave my room ya fad'a yana shigewa dakinsa yana shiga ya kwanta flat akan bed tamkar wani matacce ."
Dakin suka shigo gbdy suka rufa akanshi kamr zasuyi hauka mb ya hauro har saman gadon ya dagosa ya kwantar dashi ajikinsa ya kai hannu ya kamo fuskarsa yana dan marin kuncinsa tare da kiran sunansa "ATA ka tashi please karka zama haka yayi maganr yana kuka me yasa zaka mana haka ?"


salim da Yasir ma sunansa suke kira "wannan fa ya rigada ya bugu babu inda zai iya zuwa kamata yayi a fadawa mami "wa zai iya wannan karfin halin ?wa zai iya tun karar mami da wannan maganar ?bazan so mami ta gansa cikin wannna halin ba inji cewar yasir "to meye mafuta yanzu me zaa bashi ya dawo daidai ?abu daya ne zaa iya bashi shine kokin shi kuma yana fara shanta matsala ne arayuwarsa gara kawai duk mu kwashe duk wani kayan maye dake dakin mu barsa yayi bacci idan ya farfado zai dawo daidai ."


Ahankali ya motsa lip's dinsa "I can't marry this stupid girl I can't marry her coz she's not my type shine maganar da yake fitowa daga bakinsa "yanzu me zamu cewa mami ?a gaya mata gsky kawai yasir je kazo da mami ."Okay ya fad'a yana mikewa tsaye ya nufi kofar fita tare da mami suka dawo ai tana ganinsa ta daura duka hannuwanta bisa kanta ta fashe da wani irin kuka tana kallonsa tana furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun tana qoqarin zubewa kasa ganin gaba d'aya ATA baya cikin haiyacinsa ,dan tuni bacci yayi awon gaba dashi jikinsu a sanyaye ganin mami na neman zaucewa suka tarota suna cewa "kiyi hakuri mami Kiyi masa addaua " yanzu abinda adamcy zai min kenan ana gabe daurin auresa?" yanzu ka kyauta min adamcy ?


"gsky bai kyauta ba mami amman Kiyi hakuri girgiza kai mami tayi sannan ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta mike da kyar ta fice daga dakin ."da kyar take jan kafafunta ta sauko ta tashiga 'daki  tana kuka Allah ya taimaketa babu kowa acikin dakin domin mutane duk sun wuce zuwa hall ta kulle dakinta kuka mami take sosai ta kira aunty shahida kiran na shiga amma bata 'dauka ba dan haka ta kira aunty khadija ita kuma wayarta a kashe mami tarasa abinda Ke mata dadi sai da zaa fito da maryam aunty shahida ta lalubo wayarta nan taga missed call din mami yafi goma cike da jin tashin hankali ta soma neman layinta mami ta dauka cikin yanayi na damuwa tace "shahida !".



"Naam mami ya naji muryarki haka wani abu na damunki ne ?babu komai shahida ku wuce da maryam hall yau ma dai kamar jiya ita kadai zata zauna "shiru aunty shahida tayi kafin daga baya tace "mami ina adam din yake ?hakan nan mami ta kasa fad'a mata halin da yake ciki tace "yana kwance babu yadda yake bashi da lafiya ina maryam din take "gata nan a kusa dani "bani ita aunty shahida ta mika mata waya ,ta karba tana jin faduwar gaba mai tsanani".


"hello mami !" maryam ykk ? lafiya lau mami ya naji muryarki kamar kinyi kuka ? babu komai maryam fatan kinci abinci ? ta gyada mata kai tana cewa "Eh naci numfashi mami ta sauke "kina jina mrym ? tace "eh mami ina jinki "nasan zaki fahimceni zaa wuce dake hall yanzu yau ma kamar jiya Ke kadai zaki kasance bana son kisa damuwa acikin ranki kinji ki dinga tuna kina dani "to mami !" ta fad'a hawaye na cika idanunta aunty shahida ta girgiza mata kai alamun karta yi kuka jiki a sanyaye ta mikewa aunty shahida wayr sukai sallama da mami ."

Shiru aunty shahida tayi tana tunanin yadda yau ma maryam zata zauna ita kadai batare da ango ba ,bata ki maganar mami ba domin tasan rashin mafuta yasa ta fadi hakan amman ita dole ta nemo mafuta dan baza bari maryam ta zauna ita kadai ba ko hisham daya tsinci kanshi da auren nana hauwa'u acikin kwana daya ya yarda ya amince har ma sun isa hall bare adamcy da aka dauki sama da watanni ana abu daya ,sosai kwakwaluwarta ta shiga tunanin abunyi zuciyarta ta bata shawarar ta nemi salim ya maye gurbin ango tunda daman jiya babu wanda ya gansa ."


da sauri zuciyarta ta amince da haka nan da nan ta shiga neman layin salim kira daya tayi masa ya dauka adaidai lokacin da suke shirin shiga mota dan zuwa hall "yaakayi my aunty ?kana ina salim ?gamu muna shirin zuwa hall ,yauwa salim dan allah kazo ka maye gurbin adamcy babu dadi maryam taje wajen diner ita kadai kafadansa ya daga alamun babu damuwa yace "okay shikenan an gama aunty ya yi discounneting din kiran yana duban sauran abokan tafiyarsa tare da yi masu bayani ,gsky aunty ta kawo shawara wallahi maryam na bani tausayi dan allah ya hadata da wani irin mutun mai shegen taurin kai, bari mu jira a fito daita sai mu mubi bayan motar ku, suna tsaye aka fito da maryam salim ya bude mata bayan mota ta shiga ta zauna shima ya shiga ya zauna aka rufe murfin mota yayinda mb da sauran abokan ango suka shiga motocinsu suka bar gida ."


Tamkar ango da amaryarsa salim yayi active suka jera har zuwa mazaunin ango da amarya aunty abida ta kallesu ta kwashe da dariya tana kallon mahaifiyarta ,"mumy kinga abinda nagani kuwa ?na gani abida jiya bai zo ba ga yau ma ,ai halin adam sai ahankali ,shiyasa nake ganin da wahala ki iya shawo kanshi ya auri sultana"kai mami karki hada sultana da wannan yarinya sultana ta kereta a komai duk yadda zamuyi ta shiga gidansa sãi nayi idan allah ma ya taimakemu sai ya sota kinga komai zai zo mana da sauki ato allah yasa ,wannan lamari yayiwa abida dadi dan haka ta dinga jinta cikin tsananin farinciki ."

Hall ya cika makil da jama'a ta bangare dabam dabam maryam tayi shiru tana rike da jaka yayinda masu hoto da vedio suka dinga daukarsu hoto har sanda aka kira hisham da amaryarsa zuwa fili ahankali ya mike atare suke daga kafafunsu suka tsaya a fili tamkar wasu gumaka hajiya zulfa'u ta shigo da 'kawayenta da ankonsu iri daya ta dinga likawa nana hauwa'u 1k amma ko kalon hisham bata yi ba MC ne yayi magana wai ya yaga hajiya iya amarya takewa liki ."

murmushi tayi tace mishi "ai itace tafi cancata yar albarka yar gidan arziki gaba da baya irin albarka kaga dole ita ta dace da naiwa liki" aikuwa gurin ya 'dau shewa da tafi mutane wasu suce " wannan haka yake hajiyarmu Allah ya 'kara arziki hisham kuwa ya cika makil dan ganinsa tozarci ne abinda mumynsa tayi masa suka koma suka zauna aka kira maryam da angon bugi,maryam dake zaune wasu irin hawaye masu ciwo suka zubo mata ta yunkura ta tashi tsaye salim ya rike hannunta cikin nashi saurin kallonsa tayi sam bai damu ba ya kauda kanshi kawai ya soma tafiya daita ba dan ta soba ta dinga daga kafafuwanta ."

da zata taka step ya tsaya ta sauko ahankali yana daga mata rigarta d'an kar ya hardeta abun ya burge mutane mc kuwa ya dauka angon gaske ne nan ya fara zuba "kai wannan ango yana ji da matarsa yana son matarsa see love ai nan hankalin mutane ya sake karkata kansu aunty abida tace "dama shi ya aureta muka huta dan sunfi dacewa dashi sultana kuma da adamcy "ke dai kina qaunar sultana da wannan mai shegen taurin kan tsiya "duk zai daina ne bari dai ya shigo hannun mace ."

sosai salim ya kwashi rawa tare da maryam lokacin da aunty abida ta tashi taje liki byn tai liki ta kai bakinta daidai kunne maryam "karshe mai naci kenan da kin nuna baki raayi kamar yadda ATA yayi da yau baki wayi gari da aron ango ba wannan kawai ya isheki misalin irin halin bala'i da zaki shiga a gidansa "har aka gama taron aka watse aunty abida tana mata habaici wanda bata san dalilinta nayi mata hakan ba salim ne ya maida ita gida kai tsaye ta fito ko kallon inda yake batayi ba tashige gida ta rabu dashi dan taji haushin hannunta daya rike shima bai damuba yai tafiyarshi gida mrym tana shiga dakinsu kuka ta saka ranar  yadda maryam taga rana haka taga dare ga kuka datasha kamar ranta zai fita."


Karfe daya daidai ata ya farka daga baccinsa ya mike da kyar ya shiga bathroom yayi wanka ya dauro alwala ya fito ya sanya vest da boxer sannan ya daura jallabiya mai garen hannu akai ya qarasa inda daddumarsa yake ya tada sallah bayan ya idar da salolinsa ya zauna yana tunanin awannin daya kwasa yana bacci , can ya mike ya fito zuwa falonsa ya bude fridge bai ga whisky dinsa ba ya kalli inda ya ajiye kwalayen sigari ko karan sigari daya bai samu ba ya maida murfin fridge din ya rufe da karfi yana jan tsaki ."


ya koma ya zauna ya zubawa zanen princess dinsa idanu yana kallonta yana zaune mami ta turo kofar dakin ta shigo idanunta ya sauka akanshi idanunshi sunyi wani irin girma ta zauna a kusa dashi bai yi magana ba har sanda ta soma mgn "adamcynah ka tashi ?"eh na tashi! ya fad'a kawai yana duban zanensa yanayin yadda ya amsa kamar yana jin haushinta."

ta numfasa kana tace "me yasa baka tashi lalata rayuwarka ba sai alokacin bikinka ?me ya kaika shan giya adamcy ?yanzu ka kyauta min kenan ?ka kunyatani acikin mutane kowa sai tmbyrka yake ka kuwa san adadin karyar da nayiwa mutane ? "ni fa bikin nan bashi da wani mahimanci agareni dan Allah sweetheart ki daina min magana akanshi sake daga min hankali yake "jin haka yasa ta canza magana "me zaa kawo maka? "shiru yayi yaki cewa komai dan idan ya bude bakinsa ba abinda zai ce a kawo masa sai giya da sigari su kawai yake buqata "bari naje na kawo maka abinci ta fad'a tana mikewa ta shafa kanshi sannan tayi gaba ."

Tana fita Ya kira yaronsa yace ya siyo masa giya amman wacce tafi duk wanda yake sha karfi da sigari yana ajiye wayar mami ta dawo dakin ta ajiye masa plet din abinci agabansa kaci yanzu da zafinsa ta wuce bai ci abincin ba har sanda yaronsa ya kirasa ya dauka yana cewa "ka shigo mana " mami tana falo okay ina zuwa ya mike tsaye ya sauko lokacin daya sauko mami ta tashi ta shige dakinta ya fita "ya ka dade ?yallabai go slow yafi yawa a shagon siyar da giya fiyye da shagunan siyar da abinci bare adaidai wannan lokacin "okay kaje kawai ya karbi ledar hannunsa kwalba biyar ne aciki sai kwalayen sigari ya dawo dakinsa ya ciro daya ya balle bai tsaya sirkawa ba ya kafa abakinsa bai sauke ba sai daya shanye tass sannan ya daura da sigari haka yayita sha har karfe biyu da rabi ya koma bedroom dinsa wanda alokacin ya shanye kwalba hudu yana kan ta biyar ."


*****
Washegari sunday ya kama daurin aure hisham bai tashi ba mumy ta dinga kiransa a waya gajiya yayi da kiranta ya dauka ya mike zaune yaji dalilin takura masa da take yi, yana dauka ta rufeshi da bala'i "wallahi hisham ka kiyayi fushina  idan ba so kake nayi maka baki ba wallahi ka natsu ka shiga hankalinka ka bari ayi komai a gama lafiya "yanzu mumy me nayi ?daurin aure ne a daura mana ai ba lalle sai naje ba "okay ni zaka fadawa haka ?" to dan girman allah karka zo "da taimakon salim hisham ya shirya tsaf cikin wata dakakkiyar shadda gezner fara sol koda suka fito mutane sun cika acikin haraban estate din ."

Ahankali mb da sauran abokansu suka shigo falon ATA kowannensu sanye da farin yadi mai shegen tsada ,basu ganshi ba dan haka mb ya tura kofar bedroom dinsa anan ya gansa kwance a kasa shame shame tamkar matace ,da wani irin sauri ya qarasa inda yake kwance ya durkusa a gabansa yana cewa" Kai adam ka tashi mana lokacin zuwa daurin aure yayi fa "ya fad'a yana kallon kofar shigowa dakin "kai yasir kuzo ku ganshi ya qara shan giya ya bugu fiyye da jiya ya sake kallon fuskar ATA yana shafa fuskarsa ," kai wai meye haka ne ?subuhallah ya bugu kuma? inji cewar salim da yasir da suka shigo atare cikin tsananin tashin hankali."

" kamo shi mb yayi yana cewa "ku taimaka min mu daga shi gbdy suka kamo shi zuwa kan bed dinsa suka kwantar dashi suka dinga jijiga shi" ka tashi dan girman allah lokacin daurin aurenka  yayi ,amman shiru kake jin ATA dan ko motsi baya yi numfashi ma da kyar yake fitarwa yasir ya kai hannu ya bude idanunshi yana kiran sunansa," kai ku duba fa kugani kwayar idanunshi sun dauke inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kai abokina ka bude idanunka muna tare da kai dan allah karka min haka bana son na rasaka ."mb ya fad'a cikin tsananin tashin hankali mara iyaka .

"kana jina abokina ka bude idanunka yana magana yana jijiga shi amman har lokacin ATA bai motsa ba bai ma san a halin da yake ciki ba duk yadda sukayi su tashesa
End Ads