x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 49 - MAR ADAMS

  • 144001 words
  • 147000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 477

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
ta fixge tana zabga mata harara "ki miko hannunki na saka miki ankwa ko kuma na harbe kwakwaluwar kanki yanzu ." wani murmushin bakinciki ya bayyana akan fuskar hindu "bazan so faruwar haka ba ,dan bazan so na bar duniyar nan batare dana kawar da mutun biyu din nan a duniya ba,wannan hatsabibiyar yarinyar da kuma wanda zai aureta, duk da na shiga hannu amman ban yi nadama ba ,dan ni kadai nasa me nake ji a zuciyata yadda zan rasashi dole itama ta rasashi ."



Ta sake yin murmushi wanda kana gani na takaici da bakinciki né da rashin cimma buri "duk da na shiga hannun amman nasan zan fito dan mahaifina zai yi iya qoqarinsa sannnan zai kashe ko nawa ne akan yaga na fito tana gama fadar haka ta mika mata hannuwanta duka , sai da suka kalli juna da sauran yansanda nan take suka fahimci yanayin cewar hindu bata cikin hayacinta ,ta daba mata ankwa a hannuwanta tana cewa "duk abida kike taqama dashi wanda yasa muka bibiyi rayuwarki har zuwa yau din nan ya fiki kuma yafi mahaifinki komai ."

"idan taqamar mahaifinki nada kudi ya zartashi dan haka kisani matsawar bashi ne ya lamunce ki fito ba ubanki bai isa ba ,kuma bashi da kudin da zai fito dake oya muje ."ta qarasa mgnr alokacin da aka qaraso da maryam wacce ke kuka har lokacin ga wata zufa dake tsatsafo mata a dukkanin ilahirin jikinta kallo daya zaka wa maryam ta baka tausayi ."

Wani wulakantaccen kallo hindu tayiwa maryam sannan ta yunkura ta mike tsaye cike da d'agawa da isgilanci ta kalli macen yansanda tace "koma waye shi ina mai tabbatar miki mahaifina yana da karfin ikon da zai sa shi ya lamunce a fito dani ta qarasa maganar tana sake watsawa maryam mugun kallo "Ke kuma ki jira fitowata wallahi karon mu bazai yi kyau ba, bazan ta'ba barin kiji dadin rayuwarki ba, baqar makira wallahi nice ajalinki ki rubuta ki ajiye ."


wasu hawaye masu zafi suka gangaro acikin idanun maryam hankalinta ya qara tashi fiyye da lokacin da take cikin mota ,yayinda zufa ke sake karyo mata muryarta a raunane. tace "police kunji abinda take fad'a wai zata kasheni itace ajalina "ki kwantar da hankalinki babu abinda zata iya miki daga hannunmu sai kotu zaa kaita daga kotu kuma sai gidan kurku kinga babu wata hanyar data sauran mata "karya kake munafukin Allah bani ce zani kurku ba uwarka ce zata kurku shegu matsiyata kawai tass tasss!! taji saukar mari har sau biyu ajere akan kuncinta nan da nan ta rikice ta dinga zaginsu tana tsine masu albarka mrym tana kallo aka tasa keyar hindu da bala abayan motar yansanda ita kuma aka sakata cikin wata motar aka d'auki hanyar gida daita ."

Acikin mota hindu ta kalli macen yansanda taja wani dogon tsaki ta bude baki zatayi magana kenan taji sauka mari tasss!! ta sauke mata wani lafiyayyun mari "kina sake bude mana wannnan rubabben bakin naki zan qara miki wasu marukan dan haka ki kama kanki ki bari salin alim mu kai ki office idan ba haka ba zan sakar miki harsashi yadda taga matar tana mgn tana zazzaro mata idanuwa tana huci tasan da gaske take zata iya aikata fiyye da haka amman bata jin zatayi shiru ."


Ta dinga kallon matar zuciyarta na cigaba da yi mata zafi ranta da zuciyarta na wani irin tafasa ta dinga zagin yarsadar can kuma tayi shiru tana son sani waye yyi mata wannnan shishigi da katsalandar cikin rayuwarta ? cure hannuwanta tayi waje daya tana bugawa da juna batayi tsamanin shirinta zai ruguje haka ba ta dauka zatayi komai ta gama babu wanda yasani taci bulus ,wato mutuwar maryam ya tafi a banza bata kawo abun zai zame mata haka ba ."

Suna isa police station ta ciro wayarta daga cikin jaka zata kira number babanta amman taji an bata warning tare da kwace komai dake hannunta aka turata cikin wani qaramin daki wanda aka tanada domin masu laifi irin nata sannan suka maida kofar suka rufe garam ."kukan bakinciki bata cima burinta ba gashi kuma ta shiga hannun hukuma ya kufce mata ,dan haka ta soma maganganu cikin zafin rai tana zage zage tana tsine masu amman babu wanda ya kulata har sai data gaji dan kanta tayi shiru ta fara bin d'akin da take ciki da kallo kusuruwa kusuruwa banda duhu da zarni ba abinda ke tashi ciki ,ga kukan tsoro tun yanzu data kasance ranar allah ce ina ga dare yayi ? tsayuwa tayi taki zama dan bata ga wajen zama ba koina ta kalla kazanta né shiru tayi kawai tana tunanin mafuta ."


Cikin wani irin tashin hankali maryam ta shiga part din hajiya zulai tana kuka a parlour'n ta iske nana hauwa'u da mami zaune suna ganinta gabadayansu suka mike cikin tsananin damuwa suka isa inda take mrym ta zube jikin mami tana yi mata bayani abinda ya faru gaban mami yayi wata irin faduwa "yanzu d'an rashin imani hindu tayi qoqarin kasheki ? ta qarasa mgnr tana mai sake kamo maryam din zuwa jikinta ta rungume tana cewa " yanzu ina hindu take ? police sun wuce daita ."


Mami ta dafe kanta cikin yanayi na tsarkakkiya da shiga tashin hankali ,cikin tsananin' bacin rai mami ta zaunar da maryam ta soma magana "aikuwa wannna karon bazan yarda ba ,bazan zuba ido su kashe min ke ba ,"wannan ma ai rashin sanin darajan d'an adam ne ,wallahi da nasan police station din aka kaita da sai naje naci ubanta inji cewar nana hauwa'u " zagi kam babu wanda hindu bata sha shi a wajen nana hauwa'u ba, ita kuwa mami har da kwallar takaici ta zubar tana mai jin tausayin maryam wacce har lokacin kuka take ."

Suna cikin wannan halin na tashin hankali ATA ya turo kafar parlour'n ya shigo tare da sallama duk da bai bude muryarshi sosai ba fuskarshi kamar koda yaushe, cike da ladabi ya gaishe da mami yana mai zama akan kujera idanunshi a runtse ta amsa tana masa bayanin abinda ya faru "yanzu da wani abu ya faru da maryama shikenan taci bulus "

"Ina fa taci bulus ".
ya fad'a haka acikin ransa amman a filli yace "ai ni data samu nasarar kasheta ma da ta taimakawa rayuwata "ya fad'a yana ciza gefen lip's dinsa da d'an karfi yanayin yadda yayi maganar ya bala'i daurewa hajiya zulai kai ,tayi matukar mamakin jin abinda ya fad'a, ba ita ba hatta nana hauwa'u tayi mamakinsa kuma taji babu dadi aranta "yanzu abinda zaka fada kenan adamcy ? yayi shiru kawai yana lumshe idanuwanshi "rayuwar mutun kake fadar haka kamar rayuwarta baa bakin komai yake ba "?me zan fada sweetheart da wuce haka nifa kasancewarta a raye babbar matsala ce arayuwata ."

"Ka kuwa san abinda kake fada adamcy "?
"iyakar gskiyata kenan na fada sweetheart kuma kin san bana fadar abinda bashi né acikin zuciyata ba ,wannan kawai ya isa ki fahimci irin rashin son da bana mata ,wallahi da zata mutu da gaske da zanfi kowa jin dadi " ni kake fadawa haka adamcy ?a gabana kake wulakata min 'ya dan baka da mutunci na rantse da girman allah sai na sa'ba maka akan wannan maganar kuma matsawar baka d'auki mataki akan abinda akayiwa maryama ba sai ka had'u da fushina da baka gani ba ."

maryam ta sunkuyar da kanta kasa tana sheshekar kuka zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske wani irin tsoro ne ke ziyartar zuciyarta bata ta'ba sanin qiyayyar da yake mata ta kai haka ba sai yau din nan cike da fushi mami ta cigaba da magana "idan banda rashin mutunci irin naka agabana adamcy ,nice fa da kaina na zaba maka maryam yau ko aljanna ce maryam nace ka aura ai baka mata fatan mutuwa ba bare diyar mutun diyar ma tawa ko ka manta matsayin maryam ne a wajena "?

Yana jin mami yayyi shiru dan duk abinda ta fad'a din ya sani "wallahi ban ta'ba sanin rashin mutuncinka ya kai haka ba sai yau ,mutun sukuntu guda kuma jininka da ubanta da ni uwarmu d'aya ubanmu d'aya fa, amman dan rashin mutunci kayi mata wannan fatar ,wallahi yadda zakayi farinciki da mutuwar maryama nima nasan zakayi farinciki idan na fadi na mutu "ya bude baki zai yi magana tayi saurin katseshi ta hanyar cewa "wallahi idan ka sake min wata maganar banza a nan zan iya kafa maka hakora "bai ce uffan ba ya mike tsam ya haye samansa, jiki a matukar sanyaye mami ta mike tana goge kwallar idanunta ta nufi hanyar d'akinta."


tashin mami ya bawa maryam damar rushewa da wani kuka "banason na kawo damuwa acikin familes ,sister ya zaa yi a fasa auren nan kowa ya huta ? nana hauwa'u ta rungumeta tsam ajikinta tana rarrashinta"sister ki duba yadda yake nuna tsanata qarara wannan wani irin kiyayya ne haka me na kashe masa ?"."yasan adadin mutane dake bukatar aurena aka daukeni aka bashi ba dan ya cancata ba ?" wallahi gara na mutu tun kafin zuwan auren nan dan nima zanfi bukatar mutuwa ina jin kamar na kashe kaina da kaina kowa ya huta har ma dashi mai tsanartawa dasu masu bukatar ganin rayuwata ta tagayyara dan nasan aurena da
yaya Adam babu abinda zan tsinta acikinsa sai bakinciki ?ta qarasa mgnr tana sheshekar kuka ."

"maryam !
nana hauwa'u ta kira sunanta "me yasa kike fadar haka ai bashi zaki duba ba "sister wa zan duba ?zan rayu tare dashi ?karki manta tare zamuyi rayuwa dashi kuma acikin gida daya idan ma ta kama a daki d'aya idan damuwa yake kunsa min ni kadai zan shanye ,haka zalika idan farinciki ne ni kadai zan ji duk wani abu da zan tsinta acikin gidansa akaina zai qare kina tunanin zanyi farinciki a gidan mutumin da baya sona ?"bana jin akwai halittar da yaya adam ya tsana kamar ni, a wasu lokutan na Kan zauna nayi tunanin me yasa yake tsanata haka ?ta sauke numfashi mai hade da sheshekan kuka ya Adam yayi mugu mugun tsanata sister ."


"Na fada yanzu ma zan sake fad'a aurena dashi babu abinda zai haifar sai damuwa domin kuwa bazai yi yadda kowani magidanci yake a gidansa ba ,bazai dauki duk wani responsibility dina ba,zai watsawa mami qasa a idanunta domin zuciyarsa bata tattare da tsoron kowa ko shakkun kowa na sha jin yadda yake fadawa ya hisham da yaya bello cewar baya sona ,nima idan banki auren ba sister me kike son nayi ?ni da akwai yadda zanyi na tsaida maganar auren nan wallahi da nayi domin nafi bukata hakan ko kuma mutuwata dan wallahi zan so faruwar haka da dai na kasance a gidansa abar wulaqantawa ."

nana hauwa'u ta riko hannuwanta duka cikin tsananin damuwa tana cewa "tabbas akwai ciwo sister ciwo kuma mai zafi acikin zuciyarki nasan yaya Adam bai sonki sister amman bazan daina baki shawara akansa ba domin ina ji ajikina zai canza zaki canzasa sister ."maryam ta girgiza mata kanta alamun "a'a ! bazan iya ba sister bazan iya canzasa ba ,yaya adam yafi karfina yafi karfin hada rayuwa dani babu wanda yasan abinda Ke ransa gabadaya acikin halayensa bai gama fitowa dashi fili ba saboda babu wanda Ke rayuwar akarkashinsa ,sister zuciyata zata buga matsawar aurena ya tabbata dashi nasan nan gaba kadan zan mutu dan bazan cigaba da rayuwa mai dadi ba ".


"kiyi addua sister dayawa anyi irin aurenku karshe kuma yayi kyau kuma anyi farinciki ki hasasowa kanki haka ki daina tunanin bad things a tsakaninku ."at every step sister ta ina kike hango min jin dadi ki duba irin abubuwan da yake ta yaya kike son nayi scricfied din rayuwata akanshi ?"nasani sister amman ki bari ayi ki gani daga ranar ki fara Kirgawa day by day wata rana soyayya zata kasance a tsakaninku wallahi inada wannan tabbacin kirki zubawa mami kasa acikin idanunta domin kuwa ta yarda dake ta fad'a ta sake jadaddawa cewar zaki mata biyayya bazaki zuba mata kasa a ido ba dan allah karki karyar da yardar data tayi miki ."

"mami tayi alkwarin muddin tana raye sai anyi auren nan kuma sai kin samu farinciki a gidan yaya kuma ma shi ya Adam ya amince zai aureki har yau din nan bai ce ya fasa aurenki ba "bisa umarnin mami ba ?cewar maryam tana duban nana hauwa'u hawaye na turereniyar zubowa bisa kuncinta "ina ..!ina jin bazan .."sai kuma tayi shiru ta kasa cigaba da maganar gabanta na wani irin faduwa da karfin gaske." dan allah ki bar maganar nan haka sannan ki bar kuka nan tashi muje d'aki ki kwanta ki huta jiki a matukar sanyaye da taimakon nana hauwa'u ta mike tsaye tana jin wani irin sanyin a gabobinta tana jin kafafuwanta sun gaza daukarta nana hauwa'u ta rikota sosai ta makaleta a gefen jikinta suka nufi daki ."


ATA ya sauko tsaf cikin wata dakakkiyar gezner tamkar ranar zaa daura masa aure dinki ya balain yi masa kyau takalmin kafafunsa cover shoes ne yayi matukar dacewa da shigarsa kanshi babu hula sai agogon fata dake daure da tsintsiyar hannunsa
ahankali yake taka step yana saukowa yana duba agogon hannunsa har zai fita sai kuma ya dawo baya ya dauki hanyar dakin mami, ya tura kofar dakin a natse ya shiga ya isketa zaune hannunta rike da waya wanda ya nuna masa alamun waya ta gama tana ganinsa ta sake hade fuska tamkar bata ta'ba dariya ba dan kalamansa sun ta'bata sannan sunyi mata ciwo matuka a tunaninta ko mai aikinta bata cancanci adam yyiwa mummunar fata haka ba bare diyar danuwanta wanda su kadai iyayensu suka haifa suka bari a duniya."


cikin kankanin alokacin yaga sweetheart dinsa ta canza ganin irin kallon da yake mata yasa ta kawar da fuskarta aranshi yace "har abun ya kai haka ?."shiru yayi kawai yana dubanta a tsanake shi a ganinsa babu wani laifi acikin maganarsa dan so ba karya bane haka zalika rashin so ba karya bane , hakuri yake son ya bata amman daya tuna akan maryam ne sai yaji ya fasa ,yayinda ita mami hakurin tayi tsammanin ya shigo ya bata dan shi take bukata daga garesa amman sai taji sautin muryarsa can kasan makoshi kamar koda yaushe yana cewa "sweetheart ni zan fita amman bazan wani jima ba" bata juyo ta kallesa ba bare tace masa wani abu jiki a sanyaye ya fice daga gidan gbdy can qasan zuciyarsa cike da bakinciki da fargaban shirun sweetheart dinsa dan a duk sanda tayi shiru haka matsaloli ne zasu biyo baya ."


Daga shi sai direbansa acikin mota kira ne ya shigo wayarsa yana duba screen din wayar sunan aunty shahida ya gani bai dauka ba dan yasan kararsa mami ta kai wajenta yana kallo har kiran ya katse wani kiran ya sake shigowa sai datayi masa kira biyar bai dauka ba haka aunty khadija kiranta biyar har suka isa station kiransa suke yi amman yaki dauka ya fito daga cikin mota kai tsaye office din dpo ya nufa ya tareshi cikin farinciki ya mika masa hannu suka gaisa yana nuna masa wajen zama da hannunsa a hankali suka fara tautaunawa akan hindu."


"ranka shi dade yarinyar nan bata da mutunci ga rashin kunya ga bakinta baya mutuwa an kawo mata abinci ma ta kwafar tana zagin wanda ya kawo mata tun daaka kawota bakinta bai yi shiru ba sai tsinewa mutane take "dubansa ATA yayi yana cewa "baku ladabtar daita bane shiyasa "ai yalla'bai na dauka kamar wancar yarinyar ce da kace kar ataba lafiyar jikinta shiyasa nayi masu gargadi amman dai tasha mari a wajen inspector romoke numfashi ya sauke
"abinda ya kawoni yanzu ina son a tsanata bincike akanta fiyye da wanda akayi akan nuzla idan ta kama da duka duk ayi mata domin ta amsa laifinta ."

"bare ma wannnan yarinyar cikin sauki zata amsa laifinta dan ta tabbatarwa da jami'an da suka kamota muddin ta fito sai tayi ajalin yarinyar dakasa a bibiyeta ga dukkanin alamun itace mashekiyar da muka dade muna nema ATA ya gyada kai kawai yana saurarensa."dpo ya cigaba da magana "ko akawo maka ita ne ?ya fadi haka ne ko zai bukaci ganinta kamar yadda ya bukaci ganin nuzla."

ya girgiza masa kai kawai alamun baya bukata "abinda nake so bana son maganr kamata ta fita zuwa koina har ku gama bincikenku akanta sannnan bana son kowa yasan inda take har sai ta fad'a maku itace ta kashe mubina cikin girmamawa ya amsa masa da to "matsawar ta amsa itace ta kashe mubina ina son tasan girman laifin data aikata ku kaita kotu batare da sanin kowa ba alqali ya yanke mata hukunci daidai da laifinta a turata kurku wannan shine kawai abinda nake bukata "in sha allahu yalla'bai zaayi duk yadda kake so "tare da dpo suka fito yana sake jadaddawa dpo baya son tana tsare ya fito da kudi masu yawa kamar wancan ranar ya damkawa dpo sannan ya wuce ya tafi ."


Ahankali yake takawa har ya isa cikin dakin mami ya sameta zaune a saman abun sallah tana jan carbi kana kallon idanunta kasan kuka tayi kuma ba kadan ba ya qarasa ya zauna a gabanta
End Ads