x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 43 - MAR ADAMS

  • 126001 words
  • 129000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 530

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
."

Nuzla ta rufe idanunta gam tana jin yadda maganarsa ke tashi acikin kunnuwanta da zuciyarta so take ta sakawa gangar jikinta hakuri da jarumta har zuwa waadin daya dibar mata ya cika amman ta kasa bata jin zata iya, a halin yanzu ma ba mgnr aurensa bace a gabanta illa mafuta lallai tana bukatar mafuta ta mike tsaye tana zariya acikin parlour'n "ko na gudu ne na bar gidan ne ?ta tmbyi kanta ,gudunki bashine mafuta ba nuzla hakan ma qara min laifi zai yi idan kuma maganar ta fito shikenan kin tabbata mai laifi a wajen kowa dakinta ta shiga tayi zaman dirshan tana saqa da warwara ni dai wallahi nasan bani na kashe mubina ba haka zalika banyi yunkurin kashe mrym ba ,"shin ta ina zan fara ?ni kaina ina bukatar gano wanda yayi hakan , ta lumshe idanunta tana tunani dan dole tayi bincike dan gani wacce tayi yunkurin kashe mrym kuma ko wacece acikin estate dinsu take km itama tana son adam ne Kmr yadda take son shi jikinta ya dauki zafi sosai ."



Zaune mr ata yake akan kujera kushin dake d'akinsa yayi zurfi cikin duniyar tunani yayinda hankalinsa gabadaya ke sake tashi a duk sanda ya tuna da maganar aurensa da mrym sai ya dinga jin hankalinsa na sake tashi , yayinda a kullum ya daura kwayar idanunshi akan yarinyar sai ya dinga jin tsananin tsanarta ,shi da kansa ya kasa sanin takamaimain dalilin dayasa yake jin tsananin tsanarta haka dan bazai ce dan rashin tsawonta bane da kuma kasancewar ta fara bane ya janyo haka yanayinta dai ya taimaka wajen tsanarta ne ,duk yadda yake qoqarin yakice tsanarta da sanyata ko kadan acikin ransa zuciyarsa taki amince da zamanta a tsakaninsa tafe tafe har tunaninsa ya kawo kan zanen wukar dake ajiye akan bedside dinsa wanda aka kashe mubina daita kuma ake qoqarin kashe mrym dashi shine ya zana ya ajiye a wajensa kafin a mika wukar ga hukuma ."



ahankali ya sauke naunauyen ajiyar zuciya ya sake gyara zamansa sosai akan kujerar da yake zaune tunanin duniya yayi akan wacce tayi karfin halin shigo masa gida da taadanci , baya da tabbacin ko nuzla ce domin kuwa har ya gama kallon mai shi ta camerar d'akinsa bai iya gane ko wacece ba zargin nuzla kawai yake bisa yanayin jikin wacce ta shigo da kuma furucin bakinta amman bashi da tabbas akanta bincike ne kawai zai tabbatar masa daita ce ko kuwa wata ce dabam ta kashe mubina km tayi yunkurin kashe mrym "idan wata ce dabam meye dalilinta ?meye hujjarta ? me yasa take yunkurin aikata hakan ?iya tunaninsa yanzu ya fara gane wasu abubuwa akan me kisan wala akanshi ake yi kisan kmr yadda kwakwaluwarsa take haska masa wala kuma wani laifin suka aikata mata take masu dauki dayday ,cikin sanyi jikin nan nasa tamkar mara laka ya matso ya kunna CCTV camera .


idanunsa kawai ya zubawa camerar yana kallon wacce ta shigo masa gida cikin bakaken kaya wondo da riga gabadaya babu inda ta bari wanda zai kafa hujja akanta amman dai tabbas yanayinta ya nuna macece "to wacece wannan yarinyar ?tunaninsa ma yadda ta iya shigowa securities din bakin kofar shigowa basu ganta ba ? ko da yake ta yuwu wani abun tayi masu amfani dashi domin gusar da hankalinsu dan kuwa duk tashin hankali daaka shiga bacci suke basa ma cikin haiyacinsu har sai da aka taimaka masu ,tunda yake a rayuwarsa bai taba ganin mai kaifin baseera irin na yarinyar ba Sannan tunda yake bai taba samun kansa cikin damuwa irin na lokacin ba ,sam sam ya qasa kwanciya yayi bacci sai wurin karfe biyu saura bacci barawo yayi awon gaba dashi ."


bangaren nuzla ma yadda taga safiya haka taga dare ga wani zazzafan zazzabi daya rufeta kafin gari ya waye ta sake yin wata doguwar rama jikinta ya dauki zafi kamar garwashin wuta dan haka dole da gari ya waye aka kira doctor ya dubata nan ya tabbatar masu da damuwa ce dan har jininta ya hau ya wuce kaida yayi ja hankalinta akan yawon tunani sannan ya daura mata drip ya kama gabansa hjy salema ta tsura mata ido kawai tana kallon yadda numfashinta ke fita da kyar ta riko hannunta cikin nata zafin jikinta ya ziyarci tafin hannun hjy salema bata son ganinta cikin damuwa da tashin hankali duk sai taji itama ta shiga damuwa yanzu da tana da dama data cire mata ciwon ta dawo dashi kanta "nuzla !."ta kira sunanta ta bude idanunta dake lumshe ta zubawa mahaifiyarta "meke damunki ko akan hisham ne ?ta gyada mata kai kawai alamun "eh! .


"Halan akan maganar adamu yazo jiya ?ta sake gyada mata kai kawai dan bazata iya magana hjy salema ta numfasa kana ta cigaba da magana "me yasa zaki saka maganar aranki har haka ?tunani shine abu na farko dake fara nukurkusa rayuwar dan adam ,kiyi hakuri ki fallawa allah komai shi keyi a lokacin da yaso haka shi Ke hanawa alokacin daya so fatana Ki barwa allah lamarinki Kiyi addua abinda yafi zama alkhairi atsakaninki dashi Allah ya tabbatar mana, amman ina kyautata zaton zaki ji dadi agidansa zaki samu kwanciyar hankali a hannunsa domin hisham yaron kirki ne amman dai mu cigaba da addua mu barwa allah komai nuzla ta runtse idanunta kawai tana ji da abinda ya dameta ."



tun safe mami da mrym har ma da nana hauwa'u suka shiga kitchen suna had'awa ata breakfast suna hira ,mami ta fito tana amsa wayar hajiya nuriyya wanda adaidai lokacin ata ya sauko hannunwansa duka acikin aljihun wondonsa, sanye da riga brown colour mai hannun long sleeve da dogon wando baki "eh ke dai nuriyya abinda ya faru kenan wallahi acikin estate din nan ne amman yanzu tunda ya dawo in sha allahu bazai wuce a saka sati uku zuwa hudu ba ba ,eh babu damuwa tunda open ticket zakuyi nan ata ya wuce yayi nufi hanyar dakin jim dinsa domin motsa jiki ."


Har yayi taku biyu ya soma jiyo sautin magana kasa kasa kuma abinda yaja hankalinsa shine sunansa da yaji an kira ,ya dan dawo baya kad'an ya tsaya ya kasa kunne yana jin tautaunawarsu "matar yaya adamcy ikon allah miko min kayan ingredient din can na zuba ko ke kadai zaki hadawa mijinki breakfast na cire hannuna na kama gabana?"kai sister kina son kasheni da raina ."
"dan nace matar yaya adamcy ikon allah shine zan kasheki da ranki ?mrym ta gyada mata kai alamun Eh ! ai in sha allahu sai anyi wannan auren ko ana so ko baa so kuma muna bayan ki kamar doro ki zuba mulkinki son ranki a gidansa dan kinci dubu sai ceto babu abinda zai faru "Allah yasa sister dan irin mijin da nake so kenan .

"gashi kuwa kin samu kin yiwa sauran mata zarra ,na yiwa sauran mata zarra ko na fisu shiga matsala ?kina ganin dadi zanji a gidansa ni tun yanzu na fara tunanin yadda tunani da damuwa zai haukatani a gidansa ga rashin sonshi da bana yi ga matsalar taurin kai da wanne zan ji ? ." kina bani mamaki wani lokacin kamar ba mace ba ai ina gaya miki tsab zai sauke komai mrym ta girgiza mata kai kawai tana cewa "taimaka ki zuba min maggie dai dan ni ban san dalili ba duk yadda zan saka maggie a miyya sai yayi yawa ."


"gsky matsalarki kenan sister mman da sannu zaki qara samun gogewa agidan yayana ,wannan yaya dai ana sona dashi shi kuma baya sona,ana son na shiga gidansa shi kuma yace aa wanne zaayi aciki ? "Ke manta dashi wuyarta ayi auren ,ko da yaushe sister haka kike fad'a min wani lokacin sai naji na amince da samu natsuwa ,wani lokacin kuma sai naji hankalina yayi kololuwar tashi ni kaina zan so na ganni a matsayin matarsa dan nasan da sannu zan iya son shi da yana son kenan matsalata a halin yanzu rashin són da ....."


saurin datse harshenta tayi da karfi sakamakon ganin mutun tsaye ta bayan nana hauwa'u daman ta juya da niyyar fuskantar nana hauwa'u ne shirunta yasa nana hauwa'u tace "lafiya sister kikayi shiru ? bata iya bata amsa ba illa numfashi data dauke da karfi tana cigaba da kallon bayanta ."
ya tako a natse ya shiga cikin kitchen din sosai kamshin daddan turare da takun da nana hauwa'u taji yasa ta dan juyo ,ta dan tsorata da ganinsa nan take gabanta yayi wani irin mummunar fad'uwa amman sai ta dake ta bude baki da sauri tana cewa "san ..sannu ya.. "saurin d'aga mata hannu yayi yana qara had'e fuska , nana hauwa'u tayi taku biyu zata bi gefensa ta wuce domin ta tsira da lafiyarta taji yace "munafukar allah Koma ki tsaya wato kina d'aya daga cikin masu bawa wannan guntuwar mummunar yarinyar kwarin gwiwar aurena ? tayi saurin girgiza masa kai alamun a'a "zan kifa miki mari yanzu idan kika sake girgiza min kai koni saanki ne ? ta sake girgiza masa kai cikin tsananin tsoro ."

"Kika ce da zarar anyi aure shikenan?idanuwanta sukayo waje wani gumi ya soma tsatsafo mata akan hanci ,sannan kika ce ta manta dani wuyarta ayi auren ni zaa manta dani ?yayi maganar a matukar tsawace cikin bacin rai ,dan allah yaya kayi hakuri nifa ba wani abu nake nufi da hakan ba ina qoqarin gyara au...."ai wani mugun kallo da yayi mata batasan sanda tayi shiru ta qara shiga hankalinta ba ,kinga nayi miki kamata da irin mazan da zarar anyi aure shikenan ?ko kinga nayi miki kama da bawan mace ?ta girgiza masa kai alamun a'a ki shiga hankalinki wallahi idan ba haka nayi sadaka dake na bawa duk wanda naga dama aurenki mu huta sha sha banza da wani katon bakinki a wajen ."

ita kam mrym hannuwanta duka tasa ta rufe fuskarta sakamakon hawayen daya cika mata ido idan akwai abinda ta tsana a kalamansa gareta bai wuce munzantata ta hanyar zagin halittar da Allah yayi mata "Ke kuma na dawo kanki nan da wasu kwanaki zaki zama mata agareni ban isa na hana hakan faruwa ba amman kamar yadda kika furta tunani da damuwa ne zai haukataki a gidana tabbas haka ne domin bakinciki da damuwa zaki aura bani adam ba ,daman tunda kika shiga rayuwata kema kinsan bazakiyi farinciki arayuwarki ba, har karshen rayuwarki a wahala zaki qare a gidana gara ma kije kiyi kuka da Kururuwan a fasa auren nan shine kawai mafuta agareki da kwanciyar hankalinki nonsense kawai da bata san me take yi ba ,yanzu ke kina ganin kin dace dani ?common maggie baki iya sakawa acikin abinci ba sai an taimaka an saka miki stupid girl kawai wallahi gara ki taimaki kanki tun wuri yana gama fadar hk ya juya ya fita daga kitchen din yana jan tsaki ."


kuka mrym ta qarasa fashewa dashi ta koma bayan kofar kitchen ta hade kanta da bango tana jin wani irin zafi mai radadi duk da yadda take jin rashin sonshi amman haka ta bawa zuciyarta hakuri ta karbi aurensa amman shi burinsa yaci mutuncinta ya tozarta tasan yadda ya fad'a haka ne zai kasance rayuwar bakinci zatayi a gidansa zai hanata kwanciyar hankali da walwala ,zai hanata sukuni da jin dadi cike da jin haushi nana hauwa'u tace meye kuma abun kuka ? kina jin tsoron yaya fiyye da kaida ,"shiyasa naga kin iya mutsa masa alokacin da yake magana yake ci min mutunci , ko kin iya taka masa burki alokacin da yake cin zarafina ?tayi mgnr cikin bancin rai tana mai juyowa gbdy ta fuskance nana hauwa'u hawaye na zuba akan kuncinta."

"Sarai kijin abinda ya fad'a yanzu ,kuma Kinsan zai iya aikata fiyye da abinda ya fad'a ,shikenan nan ni haka rayuwata zata qare , kisa hannu sister ki saurari zuciyata kullum cikin bugawa take da karfi kin kuwa san abinda nake ji ?"gano yanayin tsoronki yasa yake miki haka wallahi ni ace nice zai aura bazan dauki abubuwansa ba ,"ki daina zugani sister yana fad'a min duk maganar daya ga dama, yana tozartani a duk sanda yaso , lallai ya kamata nayi kuka nayi kururuwan ataimakeni a kawo min dauki fasa auren ."nan tana gama fadar haka ta fice fuuuuuuu ta bar kitchen din ."

kai tsaye dakinsu ta shige ta fad'a saman gado ta kwanta ruf da ciki sai nana hauwa'u ce ta qarasa hada masa breakfast."wuni ranar babu abinda mrym take sai cika take tana batsewa tana jan tsaki tana tunanin mafutar da zatasa a fasa auren ta huta
abinda mami ta kasa ganewa bayan rashin son da yaya adam baya mata har da kasancewarta farar mace sol mara tsawo ne dan tasan yadda bai son farar mace yafi son chocolate colour yar doguwa mara kiba baa siyar da tsawo data siya ,baa siyan baki da ta koma baka Kmr yadda yake só tunda baya sonta kuma babu duk abinda yake bukata daga macen da zai so tô meye amfanin auren ?gara itama ta kawowa kanta mafuta tana kwance ta zabura ta mike tsaye ta fito ta nufi dakin mami lokacin karfe biyar daidai na yammaci"


Mami na zaune a dakinta abakin gado kunneta manne da waya maryam ta shigo duk jikinta a sanyaye kallo daya mami tayi mata ta fahimci akwai damuwa dan haka ta katse wayar da take ta hanyar cewa "khadija zan kiraki zuwa anjima sannan ta ajiye wayar a gefenta tace "lafiya maryam naga kin shigo wani iri? duk da wuni yau na lura bakya cikin walwala , hawaye mrym ta share tace "gsky mami na gaji da abinda ya adam yake min ,ina ganin lokaci yayi da komai zai zo karshe ,numfashi mami ta sauke cikin tsigar rarrashi "haba maryam haba diyata ki daina fad'ar haka ,kece fa karfin gwiwana idan baki auresa ba nasan hk zai qare rayuwarsa bai yi ba kiyi hakuri wata rana sai labari ."


"Amman mami ni haka zan qare rayuwata yaya baya fahimtar nima biyayya kawai zanyi ?nasani mrym amman ina ji ajikina wata rana Adamcy zai sauya zai zo har gabanki neman afuwan abubuwan da yake miki ido mrym ta zaro waje tace "mami ko kin manta halinsa ne ?"ban manta ba maryam amman na yarda da allah kuma Kinsan lamarin ubangiji ya wuce nan karkiyi mamaki wata rana ya zamo bawa agareki barin ma idan kin haihu dashi kuma gani a tsakanimu muddin ina raye bazaki shiga uku a gidansa ba ,ajiyar zuciya maryam ta sauke haka ne mami lamarin ubangiji ya wuce nan nima ikonsa ne yasa har zan zama mata agaresa ."

"Haka mami ta zauna ta dinga tausar maryam tana bata baki har mrym ta saki ranta ta manta da batun wulakanci ata ta cigaba da harkokin gabanta ranta fari kwal washegari aka tsaida ranar dazaa daura auren ata da mrym hisham da nuzla nan da sati hud'u masu zuwa kamar yadda mami ta tsara shima dan alfarma cousing sister dinta nuriyya ne domin tana son yaranta suyi hutu tazo dasu gbdy bugu da qari lokacin zai yi daidai da hutun karshen shekara wanda daman kusan lokacin da yan'uwanta dake kasashen duniya ke zuwa hutu kenan bancin hk ai da kwanaki goma kawai zata saka ayi a wuce wajen shi kam mr ata kam ko ajikinsa dan babu ruwansa da ko sati nawa zaa saka idan ma an ga dama a daura a ranar ba damuwarsa bace ."


A hankali yake saukowa daga saman mattakala jikinsa sanye da complete black suit yayinda kafafunsa ke sanye da brown shoe's agogon rolex ke daure da tsintsiyar hannunsa ,idanunshi na manne da wani hadadden farin glass ,a hankali ya cigaba da takowa cikin isa da izza alamun shi din wani ne a fadin nigeria ,yana saukowa sanyayyen kamshin turarensa REED ya soma tashi ta koina kamshin turarensa ne ya kaiwa hancin maryam ziyara da sauran jamma'a wurin sakon fitowarsa .

Maryam ta dago idanunta a natse ta tsura masa tana kallonsa tun daga sama há qasa tamkar ranar ta soma ganinsa arayuwarta ji tayi gabanta na wani irin mugun bugawa da karfin gaske, hakan nan yau ta tsinci kanta da kasa dauke kwayar idanunta akansa
sister dake zaune a gefenta ta bita da kallo tsab domin dai ta fara fahimtar wani abu akan maryam a din a game da yayanta a tun dawowarsa daga kasar france duk da ita taki yarda da zarginta tana nuna mata alamun bata son danuwanta amman kuma ita kar take kallonta domin kuwa akwai dinbin son shi makale a ranta da kwayar idanunta wanda itama bata san tana yi ba . "

"taya zaka samu miji kmrshi kace wai baka so ai sai dai idan abun yafi karfinka nmj da mata suke nema har suke rububi akansa itam saa taci da kuma darajan mahaifiya if not har abada sai dai ta tsaya akansu abbas da anas shi kuwa kallo ne daga nesa dan fin karfi kam yafi karfin aurenta ."daga inda yake yana iya jiyo sautin muryoyin mutanen dake zaune a bangaren dining area, a natse ya tsaya idanunshi karrrr akan sister dinsa da maryam wacce ta zama tamkar doluwa a wurin rike da cup din tea a hannunta tana kallonsa abinda yafi tsana kenan kallon kurulla daga mace ,kallo daya yayi masu ya dauke kwayar idanunshi akansu yana busar da iska daga bakinsa tare da furta "nonsense "! a fili wanda hakan daya furta yasa maryam tayi saurin dawowa haiyacinta tana sauke naunayen ajiyar zuciya sai dai ta qasa dauke idanunta akanshi ta cigaba da kallonsa"

bai tsaya akoina ba kai tsaye dinning área ya nufa yana shan kamshi , har ya samu wuri ya tsaya tare da soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa ,Still maryam bata dauke kwayar idanunta akanshi ba ,sister ta zungureta da sauri "ke ki dawo hankalinki mana wannan kallon da kike masa kin dai san halinsa , idan yaga dama sai ya sakaki kinyi
End Ads