mai daukar hankali ," wallahi princess da kinsan irin son da nake miki da tun tuni kin bayyana min kanki , nasan da zarar mun hadu zaki kamu da matsanacin Sona sannan zaki bani kulawa kamar yadda zan baki a yadda nake jinki idan ban mallakeki ba kin cuceni har abada ,wallahi bana kallon mata a matsayin mata , ki bayyana gareni ki tsotse min baki ,ki tsotse min joystick dina, ki tsotse min nono kinji princess dina yayi kasa da muryarsa sosai kmr zai mata kuka "dan Allah Princess ki bayyana min kanki a zahirin Ina son ganinki yana magana yana shafa fuskarta da gashinta,ya d'auki lokaci yana kallonta yana jin soyayyarta na bin jinin jikinsa hannunsa ya Kai yana cigaba da shafa kwantaccen sumar kanta sannan ya mike ya shafa superglue a bayan cavenperpa din ya manna ajeren zanenta ya dawo ya kwanta akan kujerar kushin dake ajiye a d'akin yana kallonta.
a hankali ya yaye rigar jikinsa sama kad'an ya d'aura hannunsa a daidai saman mararsa yana shafawa a hankali yana furzar da iska mai zafi yayinda sha'awarsa ke sake motsawa wani irin yanayi ya dinga ji a sansar jikinsa ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa a haka bacci ya daukeshi cike da mafarkinta, cikin mafarkinsa ya ganta tana gudu sosai tana haki tayi gudu sosai sannan ta tsaya ta dafe gwiwowinta da hannuwanta can sai ga wani hayaki ya llubeta ta koina a jikinta can sai kasa ta dinga budewa ta soma yin kasa tana ihu tana daga hannuwanta sama domin neman d'auki a daidai wannan lokacin wasu mutane su uku mata biyu maza biyu suka k'araso gurin a lokacin da kasa ta rufeta mutun biyu acikin wadan mutane kuka suke sosai suna kokarin taimaka mata ."
shi kuwa dayan wanda ya kasance babban mutun Tare da mace suka cigaba da tsayuwa rungume da hannunwa a qirji suna dariyar mugunta "a matukar firgice ya farka yana dafe grjinsa gumi ya rufesa kmr babu ac a d'akin zuciyarsa cike da mamaki mafarkinsa na yau "Anya kuwa mutun ce wannan yarinya ?Anya maganar yan'uwa da abokan arziki bazai tabbata ba kuwa ?ba mutun bace aljana ce yarinyar nan ya furta a fili "da sauri ya girgiza kanshi "Allah bazai sa haka ba inshallahu a mutun zata kasance ,idan km mutunce hakika a duk Inda take tana cikin damuwa da tashin hankali nan take shima ya shiga damuwa da jin tsoro , ranar dai bai iya komawa bacci ba dakinsa ya koma ya dinga juyi cikin tsananin damuwa ."
washegari sukusuku ya tashi jikinsa babu kwari kana kallonsa kasan bashi da natsuwar zuciya shirun nasa ya qaru fiyye da sauran lokutan baya, mami duk ta damu da ganin yanayinsa sai dai tambayar duniya yace babu komai ya boye mata saboda muddin taji abinda ke damunsa sai ta fishi shiga damuwa yau kwana biyu kenan bai sake d'aura maryam a cikin kwayar Idanunsa ba bai damu ba dan damuwarsa tafi rashin qaunar data nunawa yan'uwansa tana yi masa ."
yana zaune a part dinsa yayi shiru yayinda
MB ke zaune a gefensa "ka daina damun kanka da tunani kada wani ciwo ya kamaka kasa mu shiga uku meye ma matsalarka?sai daya furzar da iska yace "ka kasa fahimtata ne kawai amman matsaloli gasu nan takoina kuma ace mutun bazai ji babu dadi ba.
"friend abinda zaka dinga dubawa Allah ya baka Lafiya ya baka tarin dukiya bila'adadin wanda Kai kanka baka san adadin kudadenka da gadarorinka ba ,Allah ya baka komai da komai me yakamata kayi sai ka gode masa ?komai mai wucewa ne inji cewar MB "to alhamdulillah na gode masa amman bangaren damuwata ba mai karewa bace.
"kaga duk wannan mai sauki ne ni sai nake ganin kamar har da rashin amincewa da aurenka da mrym yasa damuwar tayi maka yawa koma nace yana cikin abinda ke damunka karka ji komai zanji dashi.
"Me zai sa damun tunda ba sonta nake yi ba kawai zan auri maryam ne saboda darajan mahaifiyata kuma zata kare rayuwarta a gidana sbd darajanta "Kai yanzu kana ganin zaka aureta?" zan aureta saboda sweetheart "angama zan san abun yi sun dade suna tautaunawa kafin daga baya ya mike ya fito a parlour ya iskesu har hjy zulaiheart yayi mata sallama "har zaka wuce muhammadu bello bazaka tsaya Kaci abinci ba ? a'a mami a koshe nake da zai fice daga falon yace "Maryam muje na dan ganki tace "to ! tare da d'aukar mayafinta ta yafa ta fito a haraban gidan suka tsaya ."
"wato maryam kinsan abinda yasa na kiraki ?ta girgiza masa Kai "ba'a kan komai bane sai akan maganarki da ATA me yasa bazaki amince da aurensa ba ?"banason ki rufe min komai idan kin boyewa su aunty nasan ni zaki fada min gasky menene dalili ? Numfashi ta sauke tana lumshe ido"ina jinki ? a natse ta fara mgn cikin raunanniyar murya "abu na farko ya Adam bai sona sannan abinda na fahimta kamar dole akayi masa ya aureni , ni km bazan iya auren mijin da baya sona ba gsky .
"da zai fada miki da kanshi zaki yarda ki auresa ?"a'a bazan auresa ba saboda bana son shi shima km baya sona "shiru yayi yana kallonta "ki dai yi tunani ba yabon Kai ba abokina yana da nagarta da za'a auresa ke ya'yan manyan kasar nan fa binsa suke suna rokonsa ya auresu babu wacce ya amincewa zai aura sai ke "gsky sunyi kokari da son aurensa ni Kuma kaga banason shi zaka iya fada masa gara ya zabi daya acikinsu ya aura "bazaki duba darajan mami ba dan itace me son had'in ko shi baya so sbd mami ne ?ya fada cike da Jin haushin furcinta ."gaskiya da wahala duk ta Inda
MB ya bullo mata sai ta kawo masa hujja haka ya gaji yayi mata sallama sai dai yasan ko giyar wake ya sha bai Isa ya fadawa ATA cewar mrym bata bashi had'in Kai ba ."
washegari ranar mr ATA yayi tafiya zuwa hollond Kan harkokin kasuwancinsa gbdy ya manta wata aba maryam a rayuwarsa harkokin gabansa kawai yake da tunanin princess dinsa ."Kwana biyu da tafiyar ATA maryam ta soma hada kayanta da abubuwa amfaninta ta fad'awa hjy zulaiheart da nana hauwa'u cewar ranar juma'a inda Allah ya kaimu zata Abuja zatayi sati biyu ta dawo "Kinsan sati biyu zakiyi shine baki bari mun tafi tare ba ?inji cewar nana "kiyi hakuri sister nayi kuskure nest time inshallahu iya haka kawai ta fad'a saboda taikaita maganar .
Ranar juma'a jirgin karfe goma tabi zuwa Abuja tana sauka ta tarar da kannenta da mahaifiyarta sunzo tarbarta dake sun san da zuwanta daya byn daya ta rungumesu ajikinta suna murnar ganin juna "nayi kewarku sosai "muma mun yi kewarki inji cewar izza ta k'arasa ta rungume mumynta dake tsaye tana sakar mata murmushi "mumy na sa
meku lafiya ? Lafiya qalau maryam ya mutanen lagos ?tayi mata tambayar tana shafa bayanta da gani kasan akwai soyayya mai karfi a tsakaninsu,
Ta zareta ajikinta ta rike hannunta suka d'auki hanyar gida tun akan hanya mumy ta fara mata magana akan ATA tayi matukar mamaki da Jin tasan komai "eh haka naji sai dai gaskiya ni bana son shi dan bazai yi caring din mace ba shi kenan kullum cikin dacin rai no yayi gaba ya nemi mata nima Allah zai bani nawa mijin ."
"karki soma wannan maganar ke Ina ruwanki da dacin ransa tunda yana da kudinsa ,shi fa mai kudi sai a hankali har suka karasa gida mgn daya suke yi Koda mahaifinta ya dawo yayi murna da ganinta nan ya shiga zolayarta "Hjy mrym ko ace maryamu damtso ko amaidashi irin na turawan nan ace mary
duk ke kadai gilashina a she babban kamu kikayi alagos ? Kin tashi daga diyata kin zamo surukata matar d'ana da nake ji dashi gskiya naji dadin wannan had'in, kwarya tabi kwayar kenan kinyi sa'a da dace miji na gari .mrym ta zumburo masa baki "Allah dady ka daina cewa hk ni yarkace ba wata suruka ba km ni babu wani dacen miji danayi tsokanarta sukayita yi har dasu izza..."
"zamanta a Abuja taji dadinsa tana zaune cikin yan'uwanta cikin kwanciyar hankali da annasuwa babu tsana babu tsamgwama Kuma kullum suna waya da nana hauwa'u da hjy zulaiheart sati daya sati biyu mrym shiru taki komawa lagos tun abun bai damun hjy zulaiheart har ya fara damunta wani tunani tayi tasan halin d'anta Allah yasa ba wani abun yayiwa maryam ba kafin ya tafi hollond yasa tayi musu wayo ta koma gurin iyayenta ".
da yammacin ranar asabar hjy zulaiheart ta kirasa yana dauka tasa masa kuka "wallahi muddin baka auri mrym ba babu ni babu Kai Adamcy "subhanallah sweetheart ki kwantar da hankalinki menene ya faru kike kuka da fad'ar haka ? ni dai ka auri maryam shine kawai abinda nake bukata ,Idan km kana son kwancinyar hankalina Kuma tabbas ni ce rayuwa agareka kmr yadda kake fada lallai kayi wani Abu mrym ta dawo gidan nan sannan ka hanzarta aurenta acikin kankanin lokaci na ganta acikin gidan a matsayin surukata ". Sai daya sauke numfashi sannan yace "shikenan naji ki daina kuka zanyi yadda kike so nayi miki wannan alkwari zan aureta sai da yayita rarrrashita sannan ta sake , suna gama waya Kiran MB ya shigo wayarsa byn sun gaisa mgnr minti biyar sukayi sukayi sallama .
kullum abu daya ke damunta har yasa gidan ya fita ran mrym kullum sai mahaifiyarta ta dameta da batun ATA cikin zafin rai tace "mumy nifa inada Wanda nake so jira lokacin nake zan bashi dama ya turo" ke ban son zance banza da wofi ni na haifeki ko yar riko ce ke arzikin rikon danayi miki nace ki auri Adam zaki min alfarma ballanata ni na haifeki acikin cikina har nace ga abinda nake so kiyi min gardama to ki d'auke soyayyar wancan ki maye na adam agurin dan dashi za'a yi babu fashi munafukar Allah butulu kawai , shiyasa kika wani tattaro kika dawo nan? " to dan ubanki sai kin koma tana gama fad'ar haka taja tsaki tana zuba fada ."
mrym ta fashe da kuka mai tsananin har ana iya jiyo kukanta "zance banza zance wofi ba kuka ba idan idanunki zai fado tsakiyar d'akin nan aure babu fashi sai anyisa saboda haka garama ki daina kuka karki je kisawa kanki bacin rai hawan jini ya kamaki dan ko hawan jini zai kamaki sai na zama surukar adam, wannan aure babu fashi tana magana mrym na sharba kuka kmr wacce aka aikowa da sakon mutuwa ".Iskanci banza har da cewa Ina da Wanda nake so to ni wannnan nake so Kuma shi zaki so wancan kisa masa kiyayya daga yau na gaya miki ki dauko soyayyar wancan ki d'aurawa Adam ki dauko kiyayyar Adam ki d'aurawa wancan shashar banza shashar wofi munafuka kawai mai yiwa kanta bakinciki ta k'arasa maganar tana sake jan tsaki ,
Yayan zamani Allah ya shirya wannan maganar fa tun asalin iyaye da kankani uwa ko Uba suna da iKon da zai d'auki duk wanda yake so ya bawa yarsa batare da yar taí yi gardama ba dan yanzu zamani ya rigada ya canza nan ta mike ta barta tana surutai da zaginta ."
Tana kwance a d'akinta tana kuka faiza ta turo kofar dakin ta shigo ta hau har kan gadon ta rungumeta tana rarrashinta nan kukanta ya qaru "aunty mrym ki daina kuka dan Allah sheshekar kawai take "wai me yake faruwa ne kike kuka haka?, Kin cewa komai tayi tana cigaba da kukanta nan Faiza ta fashe da kuka tana cewa "Dan Allah ki fad'a min ki Daina kuka cikin muryar kuka tace "wallahi bazan auri ya Adam ba sbd banason shi "Amman aunty mrym yakamata ki duba daranja mami tunda tana sonki sosai "wallahi bazan iya ba bazan iya ba tunda ba da ita zanyi rayuwa aure ba ta k'arasa maganar tana sake rushewa da wani sabon kuka ...."
Da daddare ta iske mahaifinta akan batun auren "mrym naji duk bayaninki sai dai banji dadi ba Amman Ina son ki rike abinda zan fada miki mrym karkice zaki yiwa yar'uwata haka karki bari wannan abu yayi silar rugujewar zumuncinmu mrym , idan har kika ki wannan auren zakiyi danasanin a rayuwarki dan bazan yafe miki ba a matsayina na mahaufinki bazan so kiyi nadama a rayuwarki ba, duk d'a na halak so yake ya rabu da iyayensa lfiya ki d'aure kiyi ta addua da sannu soyayyarsa zai shiga zuciyarki idan wannan auren alkhairi ne arayuwarki allah ya tabbatar dashi idan ba alkhairi bane mrym Allah ya canza miki da wanda yafi shi zama alkhairi bare Ina ji ajikina wannan auren alkhairi ne ni kaina bazan so Adam yaje ya auri wata ya barki ba, ni kaina na dade Ina wannan mafarkin duk da na gari zai so ya rabu da iyayensa lfiya Ina sonki mrym hk zalika Ina son aurenki da Adam kuka take a tun sanda ya fara magana har ya dasa Aya yana gamawa ya mike ya shige bedroom dinsa ya barta tana kuka ..."
*******
Barrister hayat ne zaune a gaban hadiza lawyer da suka dauka domin kareta "Ina son ki fad'a min gaskiya menene gaskiyar abinda case din yake ciki domin mu san yadda zamu kareki "menene gaskiyar halakarki da wadan wukaken da ake tuhumarki da kisan Kai dasu karki boye min komai yadda zan fuskanci shara'a na kareki "barrister zan fada maka gaskiya yadda alamarin nan yake bazan boye maka ba saboda Ina bukatar na fita acikin wannan matsalar tayi shiru tana numfasawa tare da fargaba fadar abinda ke zuciyarta ...."
Bayan wasu mintuna ta cigaba da magana
"Wallahi barister bani da halaka da wad'an nan wukaken ban san komai akansu ba , yadda ka gansu haka nima na gansu kawai dai na shiga track ne a sanadiyyar furucina. shiru barister hayat yayi yana kallonta tare da nazarinta "ka yarda barister bani na kashesu ba ta sake fad'a tana rushewa da wani kuka mai ta'ba zuciya "mai zai sa na kashesu bani da wani halaka da kisansu gara ma ita sadear mun samu matsalata daita har nayi furucin zan kasheta amman ita wannan yarinyar da naji ana fad'ar sunanta sam ban santa ba hasalima ban ta'ba ganinta a rayuwata ba tayi maganar tana sheshekar kuka.
Ganin yadda barister hayat ke kallonta yasa ta shiga furta kalmar "na shiga ukuna ni hadiza na jawowa kaina rashin kwanciyar hankali, ni kaina a daren ranar da sadear zata mutu naga shigowar mutun cikin bakaken kaya an shiga d'akinsu amman sam ban kawowa zuciyata cewar kashe sadear za'ayi ba , Ina da tabbacin da police zasuyi aikinsu yadda ya kamata zasu gano ko waye yake da saka hannu cikin mutuwar wad'an nan mutane guda biyu da'ake tuhumata akansu ta k'arasa maganar cikin tsananin tashin hankali ."
kuka take sosai kamar ranta zai fita "naunayen ajiyar zuciya barister hayat ya sauke "tabbas na yarda dake Kuma inshallahu zanyi iya qoqarina naga kinsamu ku'buta duk da mahaifiyar mubina ta tubure lallai sai an kar'bawar diyarta hakinta shi dai mahaifinta alhj jamilu ne yace ya barwa allah amman kiyi addua sosai dan idan mahaifiyar yarinyar ta rinjayi mahaifinta gsky sai dai wata bake ba , bangaren su sadear wannan mai sauki ne da kansu zasu gaji da zuwa kotu kar'ban kwana wata su hakura , amman su alhj jamilu suna da baki a kasar nan suna da fad'a aji akoina dan haka ki dage da addua sosai . "na gode sosai barister da k'okarin, "karki damu Allah ya bamu sa'a inji cewar barister hayat "Ameen ta furta tana kuka sukayi sallama da zumar zai sake waiwayota kafin a zauna kotu ."
******
Zaune mahaifiyar mubina hajiya sha'awanatu take a had'ad'd'en kujera a parlour'nta kallo d'aya zaka mata ka fahimci tana cikin tsananin damuwa domin kuwa idanunta sun kod'e saboda kuka dan tunda jami'an tsaro suka zo musu da bayanin anyi kisan Kai da irin wukar da aka kashe mubina har anyi nasarar kama mashekiyar take cikin damuwa da kuka , duk yadda mijinta alhj jamilu ke k'okarin shawo kanta taki yarda burinta bai wuce a gurfanar daita a yanke mata hukunci daidai da abinda ta aikata ba .a yanzu ma zaune yake a gabanta yana fuskantarta domin son kawowa zuciyata natsuwa "dan Allah ki bar maganar kisan mubina da ma duk wanda yake da saka hannu cikin kasheta mubarwa Allah ,haka Allah yaso bazamuyi rayuwa mai tsawo tare daita ba , yanzu karshe wad'an da basu ji ba basu gani ba sune zasu zo suna cin wahala bana jin wannan yarinyar zata iya shigowa har cikin gidan zainab ta kashe mubina , dan haka ki natsu dan Allah ki samawa zuciyarki salama da hakuri ".
"uncle jay ........." da yake haka itama take kiransa kamar yadda ATA ke kiransa " kace na hakura na bar maganar alhalin an kama wacce tayi kisan ?ya gyada mata Kai al'amun haka yake nufi" nifa say Inda karfina ya tsaya, wallalhi sai nayi shari'a daita Koda duk zan qarar da abinda na mallaka ,
Kai bari ma na takaice maka sai na rakata har zuwa gidan yari sannan ruhina zai samu salama , ai tunda asirinta ya tono bazan yarda ba sai itama an sha jininta kamar yadda tasha jinin di........."
Nace kiyi hakuri mu barwa Allah ya katse mata numfashi ta hanyar fad'ar haka " duk wani matakin da zaki d'auka bafa zai dawo mana da diyarmu da muka rasa ba ,ta kwa'be. masa baki da fuska dan sam maganarsa basa shigarta ya mike tsaye yana dubanta "muddin Ina da iko akanki ki bar maganar nan mubarwa Allah Komai yana gama fad'ar haka ya shige bedroom dinsa ya barta tana girgiza Kai hawayen bakinciki rasa tilon diyarta na zubowa akan kuncinta bata Jin