x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 42 - MAR ADAMS

  • 123001 words
  • 126000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 494

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
kyau biyu biyu ya dinga taka step yana gama saukowa ya karya zai shiga parlour'nta na biyu nana hauwa'u tace "tana dakin mu kai tsaye ya wuce bai tsaya jin dalilin ba atare suka shiga dakin cikin tashin hankali mami take masa bayanin abinda ya faru ."


shiru kawai yayi yana duban mrym dake wani irin kuka bai yi mamaki jin abinda mami ta fad'a ba sannan babu wacce tazo cikin tunaninsa sai nuzla domin ta tura masa da sakon lallai idan bai amincewa aurenta ba zata ga byn mrym sai dai itama idan ta kasheta a kasheta lokacin daya ga sakon shi ko ajikinsa dan kuwa da allah yasa tayi nasara kasheta data taimaka wa rayuwarsa ita taje da Allah shi kuma ya huta da qaya."


kiran mutanen estate din mami tasa nana hauwa'u ta dinga yi suna nan tsaye a daren sai ga jama'ar gidan duk suka rude iyayen mubina sunfi kowa shiga tashin hankali yayinda mrym Ke kuka har lokacin mahaifiyar mubina kam ta yarda domin kuwa me wukar tazo yi dakin maryam kuma exactly irin wukar ce babu tantama ,mami ta qaraso ga mrym dake  zubar da hawaye "me yasa zasu kashe min mrym ?ince duk esatate din nan yanuwan juna ne babu bare acikinmu ?
"me yasa zaa dauki ran wani ?dan girman allah ku taimaka ku fad'a min cewar duk wannan abun dake faruwa a mafarki ne domin bana tunanin haka daga cikin ahlin nan, bana tunanin wani zai iya aikata min haka kuce min wasa ne ba niyyar kashe min mrym akayi ba ?"mrym ta sake fashewa da sabon kuka tana rungume mami ajikinta gbdy ta tsure ta nemi natsuwarta ta rasa itama mami rungumeta tayi tana shafa bayanta ."


"Sweetheart kukan ya isa ki bar kuka ki kwantar da hankali kowaye acikin estate din nan zan fito dashi Ke kuma malama kin cikawa mutane kunne da hayani just keep queit I don't want to hear any sound please ya juya ya kalli wadan da suka hallara a dakin dan ba kowa ya shigo ba, dan wasu na can na bacci bama su san meke faruwa ba na kusa kusa ne suka samu damar shigowa yace "kowa ya tafi ya kwanta zai dauki mataki , ya dauki wukar ya fice .

daya byn daya suka dinga fita daga dakin cike da jima min , mrym da nana suka bi mami dakinta kowace ta haye gado sai dai ba da niyyar bacci ba dan mrym kam kuka take sosai  babu abinda take gani sai mubina cikin jini shikenan da yanzu wani labarin ake ba wannan ba ,da yanzu tana cikin jini tana wannan imagenation din tana kuka nana hauwa'u kuwa  zaman dirshan tayi da mami suna tautaunawa dan bacci kam ya kaurace masu ."


Washgari baba babba ya tara manya gidan tun daga kan kannensa har zuwa kan yayyansa na sama dasu dana kasa dasu dake esatate din acikin dakin na musamman da suke ganawa a duk sanda abu makamancin hk ya faru ,ya dade yana bayanin abinda ya faru a daren jiya tare da jan kunne da nasiha mai ratsa zuciya a karshe yace zaa yi bincike duk wanda aka samu da sa hannusa zaa mikasa hannun hukuma dan maganar da nake daku yanzu haka nayi report wajen police har na mika masu wukar domin a fara bincike duk hankulansu a tashe mrym kuwa har wanna lokacin kuka take aunty shahida da khadija kaf yayan mami tun safe suka yiwa gidan diran makiya jama'a kuwa sai zuwa jaje suke yi wa mami haka ma iyayen maryam sun kira yafi sau babu adadi  wuni ranar haka mrym tayi shi cikin dakin mami cikin tsananin tashin hankali  ."


Bayan kwana biyu da faruwar lamarin da misalin Karfe hud'u sauran wasu mintuna mr ata ya shigo estate dinsu drivenshi na tsayawa batare da bata lokaci ba masu kula da lafiyarsa ta hukumar dss suka fito da sauri kafin ma su bude masa ya bude ya fito yana gyara zaman rigar jikinsa kai tsaye masalacin dake cikin esatate din ya nufa domin gabatar da sallah bayan ya idar da sallah ya nufo gidansu nana hauwa'u da da maryama na zaune idar da sallar su kenan sai ga diyana ta shiga hira suke kadan kadan mrym na bawa diyana labarin abinda ya faru daita "amman Kinsan wani abu diyana duk yadda muke da nuzla bangata ba kuma nasan taji abinda ya faru dani har cikin daki aka biyoni zaa kasheni amman ta kasa zuwa tayi min jaje tunanina ni kuwa laifin me nayi mata? wallahi har da kwalla nayi na rashin zuwanta saboda banyi tunanin hk daga gareta ba ."

"gsky da mamaki kuma kinga ai ba haka take ba tana da kulawa da mutane most especially idan abu ya sameka na farinciki ko akasinsa amman Kiyi mata uzuri wata killa tana nan hanyar zuwa tunda duka yau kwana biyu ne da faruwar abun ,wannan gsky ne nuzla bata da haka amman baku lura a tsakankanin lokacin nan ta dan canza ba ?inji cewar nana hauwa'u"eh ta canza kam sosai ko Kinsan damuwarta ?ko daya ban sani ba wallahi na dai kula ta canza ko a yanayin jikinta zaki fahimci akwai abinda ke damunta mrym tace " to koma meye allah yafi mu sani Allah ya yayewa kowa damuwarsa Suna zaune mr ata ya shigo gbdy suka masa sannu da dawowa ya amsa Kmr yadda ya saba aciki sannan ya kalli auta yana tmbyr mami "ke auta ina sweetheart. ? "tana ciki ta shiga tayi sallah yana gama ji ya haye sama suka cigaba da hirarsu ."


Bai sauko ba sai bayan awa daya sanye da shirt ajikinsa da wondo ficewa yayi bai tsaya akoina ba sai gidansu nuzla ya tmbyi mahaifiyarta ta sheida masa tana dakinta bata jin dadi a natse ya nufi kofar dakinta ya tura kofar ya shiga tare da sallama akan lip's dinsa tana ganinsa ta mike zaune tana ware fararen idanunta akanshi tayi qoqarin ta sakashi cikin nashi idon sanda yake takowa zuwa inda take tana masa duban mamaki dan bata ta'ba expecting zata ganshi har cikin bedroom dinta ba ."

sosai ya dauki hankalinta yayi wani fresh yayi qara kyau kaman zane ta koina ya hadu matsalar dai shi din mugun miskili ne sai dai hakan ma qara masa kyau yake ahankali ya janye idanunshi acikin nata ya maida dakin yana qarewa koina kallo "Lafiya
yaya adam da wannan zuwan naka na bazata ?"

Shiru yayi yana cizan lips dinsa na kasa kafin daga bisani yace "bai kamata kiyi min wannan tmbyr ba domin kuwa Kinsan dalilin zuwana "ya fad'a alokacin daya jingina jikinsa da mirrow dinta yayi crossing leg's dinsa ya rungume hannuwansa duka a saman faffadan qirjinsa yayi da idanunshi ke kallon zara zaran yatsun kafafunsa."

da kyar ta mike daga zaunen da take tana cewa "ni ban san abinda ya kawoka ba idan dai ba kazo da niyyar karbar soyayyata bane amman kafin nan me zan kawo maka ?"yayi mata banza zuciyarsa na zafi jin yayi shiru km ta rigada tasan halinsa tayi  tunanin ta kawo masa ko ruwa ne har tayi taku biyu taji ya fixgota da karfi yana watsa mata wani kallo da idanunshi dake cike taf da bacin rai gbdy taji ta fara muzanta daga kallon da yake mata taji gwiwarta tayi sanyi ."Idanushi ya tsareta dashi yana kallonta yayinda gabanta ya fara faduwa tana adduar allah yasa ba wani laifi tayi masa ba ."

Sai daya gama kallonta sannan ya watsata akan katifa ta sauka da karfi sai da hantar cikinta ya kada still bai dauke idanunshi akanta ba ,nan take ta soma sheshekan kuka sannan ta fara mgn "yaya idan wani laifi nayi maka ya dace ka fad'a min amman wannan kallon naka na hargitsa min lissafi .kallonta ya cigaba da yi bai ce uffan ba har sai data gama ,cikin izza ya motsa labbansa "nasan kin san abinda kikayi sannan kuma kinsa shine dalilin zuwana " cikin mamaki da tsoro take kallonsa ya tsareta fes da idanunshi yana mata kallon banza ."

ranshi a bace ya daidaita tsayuwarsa yana cigaba da kallonta kallon dake qara kashe mata jiki da tsoratarwa "hakika kin tabbatar min da abinda kika turo min a kwanaki uku da suka gabata na zakiga byn mrym , kinyi yunkurin kasheta Kmr yadda kika kashe mubina dan tace tana sona ko?"Idanuwa ta zaro gabanta na faduwa a fili tace" na shiga uku tana dafe qirjinta tare da nuna kanta "ni din na kashe mubina sannan nayi yunkurin kashe mrym ?wani kallon banza yake mata yana jin Kmr ta raina masa wayo ne babu abinda yafi tsana sama da karya yafi son duk abinda ya tmbyeka ka fad'a masa gsky ta haka zaka samu sausauci daga garesa "ban kashe mubina ba me yasa zan kasheta ?"wallahi ban aikata komai ba sannan banyi yunkurin kashe mrym ba tabbas na tura maka sakon zanga bayanta amman wallahi ban aikata hakan ba ,amman ina da niyya to waye yasan da wannan shiri nawa da har ya rigani aiwatarwa?

"Lafiyayyen mari ya zuba mata yana cewa "ni kike wa wannan tmby ?nan take ta rude ta dafe kuncinta inda marin ya sauka abinda yafi damuna kashe mubina da kikayi me tayi miki nuzla ?kuka ta saka mashi tare da durkushewa kasa "wallahi sharri ake son min dan ban san komai akai ba .wani kallo ya watsa mata sannan ya juya mata baya "nasan tabbas kece kika kashe mubina dan hatta wukar da kika kasheta kinyi kuskuren barinta a yunkurin kashe mrym ."

"Da mrym kika kashe wallahi bazai ta'ba damuna ba saboda neman kai nake daita ,ni da zaki kashe min ita amatsayinki na yartaada kafin ta zama mallakina lallai ni kuma da nayi akawarin aureki .nuzla ta sake rudewa ta gigice ta soma jan gwiwowinta ta qaraso inda yake tana kuka "na baki kwanaki goma masu zuwa ki kashe min mrym kafin ta zama mallakina batare da an samu wata hujjar cewar kece kika aikata hakan ba , sannan kada asirinki ya tono ni kuma zan aureki idan kuma kika gagara kasheta har lokacin dana baki ya cika  ni kuma nayi miki alkwarin zan damkaki a hannun hukuma a kwatarwa mubina hakinta kin dai sani idan hukuma ta tabbatar da kece kika kasheta karshenki biyu ne, kisa ta hanyar rataya ko kuma zaman gidan yari na har abada muddin rai kenan yana gama fadar haka ya soma qoqarin ficewa daga dakin .."


Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 23



Ji tayi qasusuwan jikinta suna barazanar kasa riketa , lokaci guda zuciyarta na barazanar tarwatsewa bata san sanda ta kurma ihu da iyakacin karfinta tana d'aura hannuwanta duka bisa kanta mahaifiyarta hajiya salema ta shigo d'akin da sauri tana dubanta cikin tsananin kad'uwa da tashin hankali, zata iya cewa yanayin data ganta ciki bata ta'ba ganinta cikin irin yanayin ba sai yau wanda shine karo na farko da taga wannan yanayin atare daita , yanayi ne mai cike da firgici da tashin hankali."


Rawar da jikin nuzla yake ya qaru hjy salema ta matso kusa daita ta soma girgiza nuzla wacce ta koma tamkar mutun mutumi a wajen "nuzla nuzla!! lafiya what's wrong with you ?!me ke faruwa dake ? me adam yayi miki kike kuka haka ko ince laifin me kikayi masa dan nasan ruwa baya tsami banza tunda naganshi nasan akwai abinda kikayi masa ? ta jera mata tmbyoyin a rud'e tana riko hannunta cikin nata. nuzla tayi shiru tana wani irin kuka mai d'aga hankali "ki min magana mana ko hankalina zai kwanta ? ta mike a matukar firgice tana duban hjy salema sai dai bata iya amsa mata tmbyoyinta ba dan bata da amsar da zata bata a halin da take ciki ,dan haka ta cigaba da kallonta da rinannun idanunta dake cike da ruwan hawaye kafin daga baya ta fara kuka wiwi tana safa da marwa acikin d'akin hajiya salema na biye daita cikin tsananin damuwa ."


" tabbas idan har hasashe da yarda yaya adam akanta ya tabbata a zuciyarsa to fa tabani ta lalace ta shiga ukunta dan wallahi tasan zai iya aikata fiyye da abinda ya fad'a mata .hankalinta ya sake matukar tashi tabbas tayi niyyar aikata hakan amman daga ita sai Allah'n daya halicceta da zuciyarta da kuma yaya adam ne kawai suka sani ,"ba itace tayi kissan ba to waye yayi ?ta furta hkn a qasan ranta tana furta "wayyo allah na shiga uku ni nuzla ta ina zan fara ? waye yake son jifa rayuwata cikin maseefa ? da wani irin sauri ta nufi kofar fita hjy salema ta biyota tana kiran sunanta amman ina bata tsaya ba tunin ta kai kofar fita daga gidan ta biyo bayan ata ."


ya d'an yi nisa amman bai kurewa ganinta ba dan tana hango bayansa daga inda take ta kira sunansa da karfi cikin tsananin tashin hankali , shi kuwa ata yana jinta amman yaki waiwayowa ya cigaba da tafiya kmr baya son taqa qasa ."ta qara sauri sosai kamar zata hantsila , kallo d'aya zaka wa nuzla ka fahimci bata cikin haiyacinta da natsuwarta ."adaidai bakin kofar shiga side din mami ta iske shi tare da shan gabansa gif haka nuzla ta zube qasa bisa gwiwowinta agabansa idanunta na qoqarin sake kawo ruwa cikin wani irin murya mai gauraye da tashin hankali hade da rudani take furta "yaya ka taimakeni ka tsaya ka fahimceni karka yanke wannan hukuncin wallahi ban san komai akan lamarin nan ba."


ya tsura mata tsumammun idanunshi kafin ahankali ya soma magana cikin izza "taya zan iya yarda da hakan bayan kece da bakinki kika furta hakan kuma kika aikata ? "wallahi wallahi !! idan ka yarda da rantsuwata bani bace sam sam ban aikata abinda kake zargina akai ba hasalima ni yau tsawon kwanaki goma sha biyar kenan kafafuwana basu taka haraban gidan nan ba ina kwance bani da lafiya ."yadda take maganar zaka fahimci tana cikin rud'ani da tashin hankali kamo kafafuuwansa tayi cikin kuka tace "please yaya try to understand me bazan ta'ba aikata hakan ba kawai dai na fad'a maka haka ne dan ka tausaya min ka aureni amman ka yarda dani ban san komai akai ba ."

"Bazan ta'ba yarda dake ba domin nasan zaki iya aikata taadanci makamancinsa koma fiyye dashi a halin yanzu ba wannan magiyar bace ta kamaceki ki fara shirin yadda zaki aiwatar da aikin dana baki idan kuma zaki tonawa kanki asiri né tun yanzu bismillah ." jikinta da muryarta na rawa tace "baxan damu ba koda asiri zai tono dan ban aikata komai ba bare naji tsoron fallasa kuma Allah shine sheidata ban aikata ba amman zaka iya bincike akan wanda ya aikata abinda kake zargina akai amman ni bani bace kuma duk inda zaa kaini zan tsaya ne akan gskyta bazan ta'ba karban laifin da bani na aikata ba ."

a natse ya soma daga kafafunsa dan wucewa ya barta dan ya gaji da jin sautin muryarta da kukanta yana shiga kanshi over ,yaga tana qoqarin jan gwiwowinta domin biyosa ya kalli securities din dake tsaye a wajen "karku sake ku barta ta shigo ciki "okay yallabai an gama ya shege ciki ya barta durkushe tana kallonsa tmkr wani sabuwar halittta a wajenta ."mikewa tayi tare da cure hannayenta waje daya tana bugawa da juna bata ta'ba shiga tashin hankali da nadama irin ta yau ba har ga allah bata san haka abun zai rikice ya dawo kanta ba ta dauka idan ta fad'a masa haka zataci bulus ne ashe masefa zai zame mata ashe bazataci bulus ba wahala zata sha ?"me yasa batayi shiru da bakinta ba ?me yasa ta gaza hakuri har sai data fito ta fad'a masa shirinta gashi ta kai kanta ta baro ? kaicona ni nuzla bakina ya janyo min matsefa na tarowa kaina bala'i da kaina ta sauke ajiyar zuciya tare da furzar da zazzafar iska daga bakinta ."

"Ai kam wallahi sai dai yayi mata duk abinda zai mata idan ta kama ma ya mikata ga hukuma amman bazata ta'ba aikata abinda yake bukata ba sannan bazata ta'ba karban laifinta ba sai dai idan kasheta zaayi akasheta ta yarda amman bazata cika masa burinsa ba, shi idan har da gaske yake baya qaunar maryam din ya aikata lahira da kashi ba sai ya had'a daita ba da sauri ta juya ta soma tafiya kamar zata tuntsura kasa sai kace mahaukaciya ta shigo gidansu inda ta iske mahaifiyar tsaye cikin zullumi ."

Tana ganinta ta qaraso gareta tana tmbyrta nuzla ta zauna akan kujera jagwaba tana fidda numfashi duk tmbyr da mahaifiyarta take mata bata kulata ba illa hawaye dake zubar mata "wani laifi kikayi wa adam ?tayi shiru kawai batare da tace uffan ba hjy salema tace "to da alamun laifin mai girma kikayi masa yasa har ya biyoki "kamar ta bayyanawa mahaifiyarta halin da take ciki kafin ya damkata hannun hukuma a kashe mata ita a banza a wofi amman ta kasa dan gaskiya bazata iya ba domin tasan irin qaunar dake tsakaninsu kasancewarta auta a wajenta ,banda kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun babu abinda take furtawa tare da dafe kanta dake mata wani irin sara Kmr zai rabe gida biyu hjy salema ta barta ta koma dakinta dan ta fahimci laifi tayi masa mai girma wanda yasa ta kasa furta wa
End Ads