x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 30 - MAR ADAMS

  • 87001 words
  • 90000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 501

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
mata kafin mami tayi wata magana hindu ta cigaba da mgn cikin rawar murya "dan girman allah mami karki yi min tsakani da ya adam kullum zuciyata tafasa take akan sonshi Ke kad'aice zaki iya taimakawa zuciyata idan ba haka ba zan mutu cikin rawar murya mami tace "mutuwa kuma ?"kanta ta gyada mata tare da cewa "da gaske zan kashe kaina shine fansa akan soyayyar ya adam "na shiga uku ni zulai "mami ta furta acikin zuciyarta "kiyi addua hindu ni kaina zan só adamcy ya auri mata fiyye da biyu amman raayinsa ne auren mace daya macen dayan ma da kyar ya amince amman Kiyi addua nan gaba idan rabo sai ya qara dake da sauri ta runtse idanunta kana ta koma ta jingina bayanta da kujerar da take zaune tana jin wai irin faduwar gaba mai tsanani ahankali take zubar da hawaye ganin da gaske tarasa farincikin rayuwarta "anya kuwa mami nada tausayi da imani ."Anya mami bata da son zuciya ?"Tayi wa kanta tambayar tana jin radadi acikin zuciyarta bazata iya jurar rashinsa ba ,bazata iya ganin da wata a matsayin matarsa ba, yadda bazata zama matarsa a farko ba to babu wacce zata zama "hindu bari naje naga yayanku nazo hindu ta bude idanunta da kyau tana kallon bayan mami dake taku ahankali."

Kai tsaye kitchen ta shiga ta bud'e firdge kwalin dynsimo mai sanyi ta ciro ta rufe ta qarasa inda cup's suke ta dauki daya ta daura akan qaramin tray ta fito ta wuce a parlour ta samesa zaune akan kujera yana sanye da singlet da gajeren wondo ta bude kwalin juist din ta tsiyaya a glass cup taja qaramin table din glass din dake tsakiyar dakin ta dora tray ta mika masa cup ya girgiza mata kai tace "na kawo maka ruwan sanyi ?ya sake girgiza mata kai "coffee fa ? still dai kai ya girgiza aranta tace yau dai akwai damuwa ta d'an zauna gefensa "ka daina barin damuwa na hana zuciyarka sukuni "naji sweetheart amman ba wani damuwa bane zazzabi nake ji kawai "sannu bari naje na kawo maka magani ka sha "no need sweetheart thank you "kai har yanzu bakasan ka girma bane meye abun gudu a magani ?ni dai kawai bana só né da zarar na kwanta nayi bacci zanji daidai ,tô karka kwanta yanzu magariba ta kusa ya gyada mata kai yana mai runtse idanuwanshi ta mike tana cewa "me zaka ci dan tuwon shimkafa kayi yau idanunshi ya dan bude kadan "karki damu sweetheart yau bazan ci komai ba amman zuwa anjima I need coffee tasan haka tsarinsa yake wani lokaci sai ya kwana ya yini bai ba ."

*****

Tsawon kwana Uku kenan rabon maryama ta shiga harka mahaifiyarta har ma da habibi hakan kuwa ba qaramin taga masu hankali yayi ba gabadaya gidan yayi wani iri saboda rashin walwalar maryama ,ta kuma san duk akan abinda take son tayi ne domin tasan halinta tasan abinda take so da abinda bata só tana da tsananin hakuri amman idan kaga ta kafe akan abu to dole abun zai zama gaskiya ne ko alkhairi ga rayuwar mutun ,ta sani gsky take fad'a mata amman bazata iya abinda take bukata ba bazata ta'ba komawa garesu ba duk runtsi duk wahala zata daure ta cigaba da rayuwarta a yadda take yi , maryama fa ta dauki zafi sosai akan aunty da habibi duk lokacin da ta fito parlour'n tagansu sai ta koma daki ko taje bangaren umma bata dawowa sai dare da zarar tashigo kuma zata shige daki tayi kwanciyarta ko ta dauko kayan zanenta ta fara aiki ."

Da misalin karfe tara na daren ranar litini maryama tana zaune akan kujera ta cilla pencil a bakinta tana taunawa a hankali idanunta na kallon celling dakin tana nazarin abinda zata zana taji an turo kofar d'aki ahankali ta kai dubanta ga kallon kofar dakin ,aunty ta gani tsaye ,ta dauke kanta daga kallonta, aunty ta maida murfin kofar ta rufe ta soma takowa zuwa inda maryama take tana ganin haka ta mike tsam ta haye saman gado tayi kwanciyata tare da kamkame jikinta tana jin tausayin kansu na sake ratsa ko ina ajikinta musamman  take jin kewar yanuwan mahaifiyarta da bata taba daura kwayar idanunta akansu ba amman tana jin ajikinta zasu samu kulawarsu da soyayya a duk sanda suka had'u kamar kowani dangin uwa tana kallo aunty ta zauna daidai inda fuskarta take dan hk da sauri ta runtse idanunta tana son tayi bacci ."


bacci bai samu nasarar d'aukarta ba ta juya dayan bangaren sakamakon kukan da Ke shirin kufce mata dan ita kanta dauriya kawai take akan sabon canjin data kawo a tsakaninsu hakan bai hana aunty ganin abinda take ba ,daidai inda  fuskarta ke kallo ta dawo ta zauna tana dubanta hade da kamo hannuta cikin nata "me nayi miki my princess kike qoqarin Kaurace min byn Kinsan bani da kowa bani komai sai ku ? Kafin maryama tayi yunkurin cewa wani abu aunty ta sake jiho mata wata tmbyr "yanzu na cancaci haka a wajenki ,"?"Na lura kina bukatar rayuwata princess "idan kika bari damuwarki ta kasheni shikenan sau ki huta ai .... "
a d'an zabure maryama ta mike zaune daga kwance da take suna fuskatar juna da aunty yayinda hawayen idanunta suka shiga xubowa sharrrrrrrrr....."

  " meye kuma abun kuka daga magana "kiyi hakuri aunty nasan damuwata na damunki ina kukan ne saboda an cuceki an rabaki da yanuwanki da iyayenki alhalin suna sonki , bansan yadda zan misalta miki yadda nakeji ba, aunty ki taba zuciyata kiji yadda take bugawa tayi mgnr tare da  kai hannuta ta kamo hannu aunty ta d'aura daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa tamkar ana buga mata guduma, tabbas aunty taji kokawar da zuciyar keyi amman bata yadda zatayi gurin raba zuciyar da damuwa addua dai ce kuma tana kanyita babu dare babu rana kuma tasan  ubangijinta baxai barta haka ba batare daya duba lamarinta ba.

cikin murya me cike rudanin rayuwa maryama ta cigaba da mgn "bansa me zanyi abubuwa su dawo mana daidai ba har ki cigaba da rayuwarki kamar da? " aunty ki daina daukar iyayenki da yanuwanki a matsayin makiyanki ,iyayenki suna sonki fiyye da tinaninki ,sun nuna miki so da kauna tattare da kulawa da gata alokacin da kike zaman lafiya dasu aunty kema kanki Kinsan irin soyayyarsu garenki "aunty !!! ki daina ganin laifinsu sannan ki dai jin zafinsu dan su dauki fushi dake ?"

Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin  yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin  farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ."


"Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka
Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har  ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali .


Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ."

ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ."


Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ".





Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗


*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.


        Page 15


"Aisha ,  saber, da   mahamud ,  ta  gani   tsaye  akansu  suna   huci   kamar   zakuna  cikin  matsanamcin  tashin  hankali   mara misaltuwa  suna   kallonta   kamar   zasu  cinyeta  ai  babu  shiri  daga  bilkisu  har  ussein   suka   mike   daga   jikin   juna  hankalinsu yayi  mugu  mugun   tashi   ."

    bilkisu  ta  tsaya  tana  kalle  kallen   inda  zata  boye  acikin d'akin  tare  da  cure  hannayenta  waje   d'aya  jikinta  na sake d'aukar  rawa  bata  ta'ba   shiga  tashin  hankali  da  nadama  irin  na  ranar  ba domin  har  ga  Allah  bata  ta'ba  tunanin   zasu   bibiyi takunta  ba ."

Nan da  nan  idanunta  ya   kawo ruwan  hawaye ba  tace  komai  ba, ta    durkusa qasa  bisa  gwiwo
winta   dan  tasan  sai   na  lahira  ya  fita  jin  dadi  mahamud  ya  rike  kungunsa  yana  cigaba  da  kallonta  ,mamakinta  kawai   yake  dawainiya   dashi  idan  aka  fad'a   masa  cewar   zata  biyo  nmj   har  d'akinsa   bazai  ta'ba yarda  ba,  watakilla   ma  da  sai  ya  wankawa   wanda  ya  fad'a  masa  hakan   mari  "dan   girman  Allah  kuyi   hakuri   ku  yafe   min  ku rufa  min  asiri   kar  mumy   tasani  ta  karashe   mgnr   tana   kuka  cikin  tashin  hankali mahamud   ya  buga  mata  wata  razananniyar  tsawa  data  hargitsa  mata  lissafi "yi  min  shiru  makira  bana  son   jin  komai  daga  bakinki ."

nan   take   tayi   shiru  kukanta ya  qaru ta   kalli  inda  ussein  yake  tsaye    shima   kana  kallonsa  kasan  baya  cikin natsuwarsa  "mahamud   tsayawa  kayi  kallonta  bazaka   fara cin  ubanta  tun  anan  ba ?  Aisha  ta  fad'a  tana  mata  wani   irin kallo  shi kuwa wanda aka kira  da  mahamud  tunanin yake  idan  yace  zai  ta'bata to  babu  shakka  zata  mutu  idan kuwa bata  mutu  ba  zata  jikata ."

"dan  girman  allah  Aunty ai.."ai  bata  kai  ga  fad'ar  abinda  take  son fad'a  ba  taji  wani   gigitaccen mari   hagu  da dama akan  kuncinta "you  are  very  stupid   bilkisu  , akanki  aka  fara  soyayya?"  kin  haukace  kin  makance  akan  wannan  banzar  ,me  yasa zaki  mance  ko  ke  wacece ?  wato soyayya  tasa  kin  manta  matsayinki ? cikin  muryar  kuka tace " a'a   Aunty  aisha   ban   mance   ba  amman  kuyi  hakuri  wallahi  bazan   sake  ba  "hayaniyar  yan   yan'uwanta  ya sake   d'aga  mata  hankali   shi kuwa   ussein  sunkuyar  da  kanshi. kasa  yayi   yana  tunanin  ficewa ya  bar  d'akin  dan  yasan Allah ne kawai  zai   kwacesa  a  hannunsu ."  

Kai   tsaye   bilkisu   ta  nufi   bayan kofa  ta   boye  jikinta  na  wani  irin rawa  sakamakon   jiyo  muryar hajiya  rahma  tana  cewa "ina bilkisu  take  naga kun  tsaya  jugun   jugun  ko  ta  gudu ne ?  kafin  kace  me  an  samu  wanda   yazo ya  fad'a  mana   halin   da'ake  ciki a guje  na  bazamo  na   bar  hajiya  dan   bazan  iya   jiranta   ba kasancewar  tana  fama da  lalurar  ciwon kafa ."

" ina  tafiya  ina  neman layin  yan' uwansashi   da  kyar  na  samu ta  abban  sadam  yana  gama  jin bayanina  cewa  yayi  babu  ruwansa  dan  yasan  halinsa da tara  yammata , babu  yadda banyi dashi  ba yace  bai  zuwa  koina  ya kashe  wayarsa  jin abinda  ya fad'a yasa  na  kira  yayyensa   mata ."

Ina   shiga   unguwar  naga   jamaa  sun   yi   cirko   cirko!!  ga   manya  manyan   motoci  na  gidansu  bilkisu  jere a  kofar  gidan ,haka  ina  shiga   cikin  gidan  mutane  na gani  makil   kowa  na   fadar  albarkaci   bakinsa ,yayinda  muryar   mahaifiyarta  ya  karad'e  koina   acikin   gidan   "da  gaske  ne  bilkisu   tana  cikin wannna  ru'babben  d'akin ? Aisha ta  nuna  mata   bayan   kofar d'akin  "tana  ciki   kuwa  ga  makira  nan a bayan  kofa   ta  fad'a  tana   zubar  da  hawayen  takaici  ."

"inna  lillahi !  hjy  rahma ta furta  a fili  cikin  tsananin  tashin hankali "kunji   abinda  naji  kuwa  wallahi  ji  nayi   zuciyata  kamar ta  buga ?hankalin  bilkisu  ya bar duniyar da  muke  alokacin  dan  sai  wuri  wuri  da  idanu  take  shi  kansa  ussein kana  kallonsa  kasan  nadama  ne  acikin   ransa  nadama  irin  wacce bata  da  wani rana ."

" amman  bilkisu  bakince  min kin rabu  dashi  ba  ?jikinta  na  rawa ta  shiga  gyada  mata kai  alamun Eh! tana   bawa mahaifiyarta  hakuri  da  wani  irin  fushi  ta  juya  inda  ussein  yake   cike  da  nadama ta shiga  zabzabga  masa  mari  ta koina "bana  ce maka  ka rabu  mun  da  yarinya ba  ? ba  banace karka  sake   shiga   rayuwarta  ba?"Ko kaga  yarinyata   tayi  kalar  wacce  zaka ce  kana so ? ta  juya  zuwa  ga  bilkisu  " Ke yanzu  har  wannan  qazamin  ne  abun  so  a wajenki  ? ta  fad'a tana sake   juyowa ta  d'aga hannu  zata  sake  tsinkawa  ussein  mari  nayi saurin   rike   mata  hannu  ina bata hakuri  "kiyi   hakuri  hjy sam  ussein  bai  kyauta  ba  daya  bawa  yarinyarki damar  zuwa  inda  yake  ,ya  karbi laifinsa  ayi  masa  afuwa   in sha allahu  hakan  bazai  sake   faruwa ba   Kinsan   kowa da irin jarabawarsa  dukkanin  rayuwa  rubutaccen   lamari ne daga  Allah ,kuma   kowani  dan  Adam yasan  da  haka  ,yanzu  tunda  abun  ya  zama  haka ku bamu  dama  sai  mu  turo ayi maganar  aure "."


Wani  irin  kallo  gabadayansu suka  bini  dashi  ,hjy  rahma  tace  "Allah ya  tsareni  na   had'a  zuria da wannan  ta  nuna  ussein  da  yatsanta  tana  hararsa "wallahi   bilkisuna  tafi  karfen  aurensa  ki kalleta  sama da qasa  ki  kallesa ta  ina   hadin yayi daidai  ?  duk  nasan  da  haka  hjy  amman  a wajenta  shine daidai    bugu da qari   rayuwar  yarinyar ku  zaku duba  domin  ita  diya  mace ce zata  iya fad'awa  kowani hali ."

"Ba kowani  hali  zata  fad'a ba ko  mutuwa  zatai  sai dai ta mutu na yarda  na   rasata   gbdy  akan na bawa wannan   matsiyacin aurenta ta  numfasa  tare  da sa  tafin hannunta ta  share hawayen idanunta  "hjy  ki  daina furta  haka  shi  soyayya   allah ne  yake had'awa  , kuma  babu  ruwan soyayya  da  tsiya ko arziki  yarinyar  nan tana  qaunarsa  shima kuma  yana  sonta dan  girman  allah  ki  barsu  suyi  aurensu  kowa ya huta  sannna  babu  wanda  yasan matsiyaci ko  mai arziki  sai Allah  sannan babu wanda  yasan mai gobe  zata  haifar  ku barsu  su  aure juna   domin   samun  kwanciyar hankali ."

bata   kulani  ba  har  na  dasa aya ta fuskanci  bilkisu  yayinda  gabadaya  yanuwanta   kacokan  suka  maida  hankalinsu Kan  ussein  duk  sun qagu  suga hukunci  mahamud  akan  ussein kasancewarsa  soja ,  hjy  rahma  ta  matso  sosai  kusa da 
End Ads