x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 23 - MAR ADAMS

  • 66001 words
  • 69000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 528

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
auta ."
yana da shekara ashirin da takwas  a duniya ya fara aiki a gidansu bilkisu  ta sanadiyyar abokin   abban sadam  abdulwahab wanda shi gadi yake a makotansu ." mahaifinki ussein ya kasance direban ne gidansu bilkisu wanda Ke kaita school , idan lokacin tashi yayi ya koma ya d'aukota duk inda zata shike kaita hussein ya kasance mutun ne mai tsananin kirki gashi kyakkyawa aji farko illarsa dai shi din ya kasance talaka ne mai son  jin dadi  arayuwarsa km yana harka da yammata da shaye shaye  sai dai bai ta'ba barin gidansu bilkisu sun san da zaman wannan halin nashi ba a boye yake yi saboda tsira da   aikinsa ."

Maryama  ta  runtse  idanunta tana jin wani tuttukin bakinciki   a zuciyarta. ta d'aura kanta  akan cinyar  umma  ko  zata  samu  sausaucin zugin da zuciyarta take  ,dan tun  baaje  koina ba   ta   fara datasanin  jin  labarin   iyayenta  , mahaifinta manemin mata ne ga shaye shaye a iyan nan  ma kad'ai  ta raina kanta ta sake yarda su   din  marasa gata ne ."

" tun farkon ganin bilkisu da ussein taji  ya  burgeta     daman   shi  Allah   yayi masa  farinjin  mata  dan  atarihinsa  bai  ta'ba  cewa yana  son  mace  ba   dan  har  prouding  yake , wannan yasa ya qara samun kusanci daita sosai , duk abinda taci sai ta rage masa idan zai kaita school ta bashi tun abun yana bashi mamaki har yazo ya daina bashi mamaki ya ajiye  abun amatsayin ita din mai alkhairi ce , shima kma yana kulawa daita sosai dan hatta murfin mota kafin ta fito ya fito ya bude mata sannan  idan   sun  iske an gama assembly  zai tabbatar  da ta  shiga  class  akan  idanunshi  sannan zai  juya ya koma  gida ,ga iya  bada  labari,  ussein ya iya bada  labarin da zai saka mutun nishadi  amman fa ga wanda  yake da mahimanci  a wajensa duk wannan yana cikin abinda yasa bilkisu ta sake sakewa dashi , shiyasa kullum bata da magana sai na fadar kirkinsa a wajen iyayenta wanda har hakan yasa iyayenta suke son batunsa tana sa ayi masa alkhairi na mussaman kullum da irin kyautar da take sa  ayi masa ."

haka rayuwa tai ta tafiya mubarak na kiranta a waya amman sam  bata  bashi  lokacinta  yayinda wata irin shakuwa mai karfin gaske ta shiga tsakanin ussein da bilkisu lokacin da ta kai shekaru sha bakwai ta fahimci ba shakuwa bace kawai a tsakaninsu soyayya ce mai karfi wanda shima zuwa lokacin ya kamu da matsanancin soyayyarta ta yadda ya kasa hakuri sai daya zaunar dani ya fad'a min ciwon dake zuciyarsa yace zai yi qoqarin ya boye nashi domin itama bilkisu ya fahimci irin son da take masa bazai ta'ba barin wannan soyayya ya tabbata a tsananinsu ba domin dai yasan tafi karfinsa tafi  karfin aurensa ita din ba sa'ar
aurensa bace babu ta yadda zai sameta arayuwarsa ."

"Nima na karfafa masa gwiwa ya  danne abinda yake  ji akan  bilkisu na nuna masa bambamci dake tsakaninsu  daita  samun auren irinsu akwai wahala duk  da babu yadda allah baya al'amarinsa shi yayi talaka kum shi yay mai kudi nace yayi addua sai allah ya kawo masa sauki da mafuta , amman alokacin ya sheida min zai ajiye aiki ya nemi wani still dai nice na hana na bashi kwarin gwiwa ya cigaba da aikinsa ya dai rage sakar mata fuska da kusanci daita ."

yana cikin wannan halin kwatsam bilkisu ta bayyana masa soyayyata da fari yaki amincewa hakan yasa ta shiga damuwa mai tsanani har rashin lfy ta kwanta batare da iyayena sun san akanshi take ciwon ba wanda ta kai har dakin daaka bashi a gidan take biyosa tana kukan ya amshi soyayyarta "ya zaunar daita ya fad'a mata gsky soyayya atsakaninsu ba abu ne mai yuwu wa ba duba da matsayinta da nashi , kuka take tana nuna masa babu wani bambamci a tsakaninsu dashi duk abu daya ne a wajen Allah da kalamai masu sanyaya zuciya da soyayya tasa ussein ya amince tunda daman shima yana sonta ranar daya amince aranar yan gidansu suka ga ikon allah domin dai bilkisu ta warke daga rashin lfy da take suka fara gudanar da soyayya ."



" tun tana boyewa har tazo ta fara bayyanawa zuwa lokacin a family's duk wanda yasan bilkisu yasan ussein idan har kana son kaga kyautar bilkisu ko yalwataccen fararta to kayi mata mgnr ussein family's dinta babu wanda bai san ussein direba ba idan ya dauko ta daga school zasu samu waje su parka su sha soyayyarsu ussein yana da yammata masu son shi amman soyayyar bilkisu tayi karfin da bazai iya cigaba da soyayya dasu ba ,wata irin soyayyar ussein Ke nuna mata mai karfi wanda har ta kai yana iya ta 'bata batare data hanashi ba nasan wannan ne saboda ussein na kawota gidan nan wajen mahaifiyarsa akwai lokacin dana shiga bangaren hajiya bata nan na iske su a dakin tana kwance ajikinsa sanye da kayan makaranta ajikinta suna romance ."hajiya mahaifiyar ussein ba ƙaramin jin daɗin haɗuwar bilkisu da ussein tayi ba ganin yadda yaron nata ya fara natsuwa ba kamar daba ba yanzu duk wani harkar mata ya jinginar da ita, haka zalika shaye shayensa yayi sauki sai wanda ba'a rasa ba."

Bayan bilkisu ta kammala karatunta na secondary akace ta fito da miji saboda masoya sunyi mata yawa kowa na sonta da aure km mafi yawansu cikin yanuwa ne sai kawai ta gabatar da ussein amatsayin mijin da zata aura hajiya rahma na gama jin abinda bilkisu ta fad'a ta mike tsaye tana dubanta abun ya mugun girgizata a matukar firgice tace "bilkisu banji abinda kika fad'a da kyau ba ina son ki sake maimaita min ,fad'a min naji da kyau tayi magana a tsawace batare da wata fargaba ba ta sake maimaita abinda ke ranta ai nan take mahaifiyarta da yan'uwanta da suka fito ciki d'aya suka nuna rashin amincewarsu mamakinta ne ya kamasu daman shakuwarsu ba iya nan ta tsaya ba ,har ta kai matakin soyayya juyin duniya akayi daita tace ussein take so har da ikirarin muddin zatayi aure to shi zata aura ,nan fa suka fara raba jaha da mahaifiyarta yan'uwanta kowa zaginta ya shiga yi me zatayi dashi ta rasa wanda zatayi soyayya sai direba common direba zata aura ? ita dai jinsu kawai take amman ita aranta ta kudurta komai zai faru sai dai ya faru amman ita ussein take so km har lokacin mahaifinki na shaye shayensa sai dai ba kowa ke iya fahimtar hk ba km nasan yawon tsaftansa da amfani da turaruka masu kamshi yasa baa ganewa amman mu dake rayuwa a gidan nan mun sani tunda idan yana gida yana shan kayansa a bayan dakin salma lokacin baa gina ba ."


Tashin farko mahaifiyarta tasa akayi kiransa cike
da matsanancin fargaba da tashin hankali ya nufi part dinta bakinsa dauke da sallama ya shiga falon tana zaune akan kujera na alfarma bata amsa sallamar da yayi ba haka zalika bata dubeshi ba tun kafin ayi masa gurin zama yayiwa kanshi yana mai yi sunkuyar da kanshi a kasa agabanta tmkr mai neman gafara ahankali ya furta" hjy barka da dare ta dago kai daga Kan tv ta maida kanshi tana qare masa kallon tsab tana nazarinsa ko kayan kirki ma babu ajikinsa kana kallonsa kasan mataiyaci ne mai yaci bare ya bawa bilkisu shi kuwa kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewar ba cikin natsuwa da kwanciyar hankali yake ba tunda ya samu kiran gaugauwa daga hajiya rahma bai sake samun kwanciyar hankali ba har zuwa yanzu da yake durkushe agabanta sai data gama qare masa kallo sannan ta numfasa ta fara magana a kausashe "meke tsakaninka da bilkisu ?da sauri ya girgiza mata kanshi alamun babu komai ."

Shiru tayi tana cigaba da kallonsa kafin daga bisani ta cigaba da magana cikin bacin rai "kace babu komai ?da sauri ya girgiza mata kai alamun Eh !
"ni nasan akwai komai amman tunda kai da kanka kace babu komai to ya tsaya a babu komai din domin idan ya zamo akwai komai zaka hadu da mummunar bacin raina zan maka abinda har ka matu bazaka manta dani ba sannan daga wannan lokacin aikinka ya qare acikin gidan nan ya dago da sauri yana kallonta a tsorace "haka nake nufi ko kana bin mu bashi ne da ka wani tsareni da ido .?"


ya sake girgiza mata kai alamun a'a ! "to maza ka tashi yanzu yanzu ka tattara komai naka ka bar mana gidan matsiyaci banza kawai ,kaga yarinya qarama shine kake son kayi mata wayo,  guda nawa bilkisun take da zata auri me shekarunka ? Idan km kwadayin  kudin  ubanta  kake  kayi  kad'an kaci . matsayinka  bai kai nan ba, ka  bari ya'yan manya ya'yan  masu  arziki  irinta  su more ba kai matsiyaci ba , matsiyacin  ma wanda ko rigar kirki baka dashi tana zuba ruwan bala'i ya zabura ya mike da sauri zai wuce tace " ba estate din nan ba ko a bakin get din estate din nan aka gaya min anganka wallahi wallahi sai nasa an daure min kai ko nasa a 'batar min da kai idan ma ba son abun duniya da son zuciya irin naka ba ina kai ina bilkisu? kai yanzu kaga dacewarku daita ?da sauri ya girgiza kai "a she kasan gsky maza tashi ka bani guri matsiyaci banza kawai ko maza sun qare a duniya mai bilkisu zatayi da kai da sauri ya qarasa barin  falon bai tsaya jin sauran karashen zancen ba yana fita daga falon bilkisu ta fito daga d'akinta  daman km hayaniyar mahaifiyarta ce ta fito da daita ta tmbyeta ita da wa ye ."

"Nida wannan matsiyacin ne dake neman cutar da rayuwarki "ta bata amsa atakaice tana dauke kanta bilkisu tayi shiru tana nazarinta idan har ta fahimceta da ussein take ? da sauri ta nufi kofar fita ta dakatar daita "idan kika sake kika bar falon nan sai na tsine miki albarka cak ta tsaya tana kallon mahaifiyarta " shasha shar banza da bata san ciwon kanta ba duk cikin yanuwanki wani dan iskan kika ga ya kawo miji Kmr wannan tsukakken da ko kayan kirki babu ajikinsa kullum yana yawo cikin kodaddun kaya ,kisani ko zaki mutu bazaki auresa ba na haramta miki aurensa ke intakaice miki baki da miji sai mubarak dan albarka in sha allahu
a ranar useein ya tattara ya bar gidan ya dawo dakinsa dake nan byn makaranta faidiyya ."


Tun daga ranar lamari ya sake lalacewa domin tunda bilkisu tasan ya bar gidan hankalinta ya tashi ta shiga damuwa sosai ta kauracewa kowa numfashi kawai take acikin gidansu amman rayuwarta da komai nata yana wajen ussein  ta kirasa yafi sau babu adadi bai daukar kiranta da kyar da ban hakuri da turo sakonin ya sauko sannan ta dawo daidai, acikin satin tasan yadda tayi  suka  hadu da ussein maganar gsky ussein na sonta shima bazai iya rayuwa babu ita ba ,sai  dai wulakancin da mahaifiyar  bilkisu tayi masa  da kiransa matsiyaci da tayi  shi  yafi  komai  tunzurashi   ,domin  duk gargadinta a banza ya daukesu babu abinda yasa aransa  kamar cima burin  sake kwace mata yarinya ta kowani hali   sannan bai boye ma mahaifiyarsa komai da irin wulakanci daakayi masa itama kwarin gwiwa ta bashi tunda yarinyar tana son shi a matsiyaninsa talaka  kar ya kuskura ya rabu  daita ai su suke da mace sune a wahala ,  ina son nayi mgn  alokacin  amman  babu halin yi a gabanta domin ussein shine auta km soyayyarsa dabam ce  acikin yayanta  amman dana fad'a masa gsky ya janye kudinrinsa ya rabunmusu da  yarinya "


"nasan duk wannan ne sbd ni abokiyar hirarsa ce
dan duk  gidan nan da yan'uwansa mata bai yarda
da kowa ba sai ni domin yace ina da sirri  wasu abubuwan ma a gabana suka faru ,ussein ya sha kawo min bilkisu bangarena ta yini anan bilkisu na da matukar kirki da son mutane sannan bata da rowa idan zata zo wajena tana kawo min abubuwan amfani ga aiki da take min sam bazakice diyar mai kudi bace bata da son jikinta tana son aiki sosai da son mutane sadam kam ya sha gata a wajenta dan komai ta gani na yara zata siyo ta kawo masa wanda hakan yasa naji ina matukar qaunarta har cikin raina nake jin tausayinta domin tana sakewa ta fada min damuwarta da duk halin da take ciki a gidansu da yawon mgnr aurenta da mubarak da mahaifiyarta ke mata tana nuna mata mubarak yafi ussein sam bata dace da ussein ba ."

"ni kaina nazo na gano bata dace da ussein ba a wani zuwa datai na zaunar daita nace ina son nayi magana daita a matsayinta na kanwata da muka fito ciki daya baa matsayin matar da kanin mijina keso ba ta bani hankalinta ni kuma na fara magana bilkisu ko kinsan ussein yana shaye shaye ? ."tace min "eh !tasani km tayi masa mgn yace da zarar ya auret zai daina ,na numfasa nace "ke kin yarda zai daina ?tace min "eh ! Ko kinsan yana da yammata byn ke ?ta sake ce min eh ai ya rabu dasu Ina son na bata shawara ta auri mubarak ta bar ussein amman ina jin tsoro kar taje ta kwashe ta fada masa tunda idanunta sun rufe shi kuma ya fadawa mahaifiyarsa na samu matsala na kama bakina amman duk wanda ya kalli bilkisu km yasan family's dinta gsky yasan basu dace da juna ba ."

Soyayya ta sake yin karfi a tsakanin ussein da bilkisu dan babu abinda barinsa gidansu bilkisu ya janyo sai tabarbarewar rayuwar bilkisu dan a tunanina ussein ya fara saduwa da bilkisu batare da aure ba ni kaina alokacin naso ace iyayenta sun barta ta aureshi tunda ita taji kuma tagani amman mutanen nan suka ki saboda kyamar talaka , dan da irin rayuwar da suke gara ace aure sukayi, bazan ta'ba mantawa ba wata rana bilkisu ta sameni tana kuka na tmbyeta bata boye min ba ta fada min ciki gareta nan take na shiga damuwa mai tsanani nace "haba bilkisu me yasa zaki sakewa nmj jiki haka ?bakya jin tausayin iyayenki da yan'uwanki bakya gudun ranar da ussein zai juya miki baya ?ina ta mata fad'a Kmr kanwata ta jini ita km tana kuka tace ."na taimaketa acire mata cikin nace babu ruwana bazan saka hannu a kashe rai ba ,muna cikin wannan halin hjy ta shigo ashe taji duk mgnr mu itama cewa tayi abarshi kar acire taje gida zata samu iyayenta sai ayi mgnr aure kawai abu ya bani mamaki kamar wasu yoroba tunda sune ake irin wannan rayuwar dasu sai kayi ciki zaa yi aure km su yin ciki ba wani aibu bane a wajensu murna ma zaayi da samunsa tun daga nan na fahimci duk abinda ussein yake da saka hannun hjy ciki ."

Tô tun daga ranar ban sake saka bilkisu acikin idanuna ba a she byn ta bar wajena ussein ya bata maganin zubar da ciki ta sha koda ta koma gida sai ciwon ciki kwana tayi tana murkususu ciwo har garin allah ya waye ,cikin yaki fita ga ciki yaki daina ciwo iyayenta dai suka gaji suka kira doctor ya dubata byn ya gama dubata ya rubuta mata scan tô a wajen scan ne likita yaga ciki a mahaifarta tunda likita ya soma bayani mahaifiyarta ta rikice ta dimauce ta kasa gane takamaiman abinda yake fada ganin ta rude yace mata wani abu ya gani me kama da gas a mahaifarta amman ta kira wani daga gida yazo nan ta kira Aisha yayar bilkisu hankalinta a tashe  tazo ta samu hjy rahma a reception zaune tayi  tagumi bilkisu zaune a gefenta cikin tsoro da fargaba scan taso cikin ya fita cikin sauki batare da kowa yasani ba hjy rahma  tace Aisha tashiga taji me doctor yake nufi da gas din da ya gani a mahaifar bilkisu ta shiga nan likita ya fad'a mata komai itama tashin hankali tashiga mai tsanani amman sai ta boye ta fito tana cewa uwar ulcer ke damunta nan hankalin mahaifiyarsu ya dan kwanta suka koma gida ."

Aisha ta kira bilkisu zuwa gidanta tana qarasowa bata tsaya wata wata ba ta rufeta da duka sai datayi mata mai isarta kamar zata kasheta sannan ta barta byn ta gama dukanta ta kira kaf yan dakinsu ta sheida  masu sannan  tasa akayi mata wankin ciki aka cire cikin lokacin da hjytr ussein taji babu cikin Kmr ta mutu dan bakinciki har da kuka
End Ads