x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 17 - MAR ADAMS

  • 48001 words
  • 51000 words
  • Out of 169502 words

Category: Romance Story +18

Views 465

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
na rawa "ke wa kenan ? ya sake tmby tayi shiru jikinta na cigaba da rawa hawaye na sake cikowa a idanunta  ta rasa dalilin  hawayen  nata  Jin shiru yasa ya taso da kyar yana mika  daga shi sai gajeren wando  army  green  iya cinyarsa da farar singlet wanda suka bayyana  surar  jikinsa a fili ake iya ganin  kwantaccen sumar dake kwance  a cinyarsa  da  qirjinsa haka kan nipples dinsa  sai farin silifas dake sanye da kafafunsa da farin agogo da alamun aiki yake ."

A tsaye ya ganta a bakin kofar gbdy bata cikin  haiyacinta a hankali ta d'ago ta  kare masa kallo saboda kusancin da suka samu muryarsa a kasalance yace  "ke lafiyarki  tsayuwar me kike yi anan  ya fad'a fuskarsa a murtuke"kayi hakuri please mami  ce tace nazo na tambayeka abinda zaka ci a girka maka "  ya tsuru mata Ido  a zahiri yake iya hango yadda qirjinta ke  bugawa wani dogon tsaki yaja a fili ya juya ya koma ciki ya barta tsaye . juyawa tayi tana daga kafafuwanta da kyar ta dawo parlour'n ta tsaya hjy zulaiheart ta dubeta "yaakayi me yace zai ci ?hannuwanta ta tsarke cikin juna sannan ta bud'e baki da kyar "wai a dafa masa komai."

mami  ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi , ita Kuwa nana hauwa'u sarai ta fahimci wani abu a tattare da marsi tasan sarai ba abinda yace mata  kenan ba   "to shikenan maza ki shiga ki dafa  masa  abinda  yazo cikin tunaninki amman ki natsu sosai kinji. "ta gyada mata tana cewa "sister muje ki tayani "me .....?dan girman Allah ki rufa min asiri na tsira da mutuncina ke dai kije Allah ya bada sa'a kiyi kokari yayi dadi  sosai ta k'arasa maganar tana kakkabe hannunta. "haba sister ki taimaka mana kin san fa  komai tare mukeyi ,nasani amman ban da wannan wallahi bazan Saka hannu ba abinci yazo bai yi dadi ba ya had'amu yaci ubanmu"  hjy zulaiheart tayi murmushi "Kai Adamcy hukuma kowa tsoronsa yake ji amman Kuma fa yana da sauki Kai Kinga mryam  yi tafiyarki kinji  duk abinda baki gane ba kizo ki tambayeni Simi Simi ta juya ta shiga kitchen kmr ta daura hannunta  tayita kuka dan tasan muddin tayi kuskure sai yaci ubanta duk iya k'okarinta na dafa  masa rice and stew bai ci ba ya wuce juma'a ."

*****
Da  misalin  karfe  biyu  na  rana  bayan  an  sauko  daga massalaci  hajiya   zulaiheart  da  kanta  ta fito  zuwa  haraban  gidan ta fara  rabawa yaran dake shigowa haraban estate din sadaka  wake da shimfa  acikin takeaway fari tare  naira dari  biyar biyar sababbin yayinda  ATA  ke tsaye daga can nesa kadan da inda take kunnensa manne da waya yana tafiya a hankali irin na jinin saurarata dan sauranta  yaki   barin jininsa komai nashi  irin nasu ne sanye yake cikin farin yadi voil  kafafunsa sanye da takalmi fari haka ma Kansa sanye da hula fari mai ratsin  baki  yayinda tsintsiyar hannunsa ke d'aure da  agogon silver rolex   yayi  kyau sosai kamar ka sacesa ka gudu  sai dai kallo d'aya zaka masa kasan   zuciyarsa dakushe take  da tsananin damuwa ."

tsayawa yayi cak yana cigaba  da kallon mahaifiyarsa  cikin haka ta  juyo  nan take  suka had'a  Ido daita ya sakar mata  taadaddaden murmushinsa dake sake bayyanar da ainihin bawar kyawun da Allah yayi masa wanda wannan murmushin babu mai ganinsa sai ita , murmushi
ta sakar masa cike da farinciki ganin murmushinsa  da ba kowa yake gani ba tana tsananin son kyakkyawan tilon  d'anta shi  din dabam ne acikin zuciyarta  ,uwa Uba nagarta   tana   masa so mai  tafiyar da ruhi shine karfin  gwiwarta ."

a hankali  ya soma takowa zuwa Inda take har ya k'araso gareta ya tsaya kusa daita yana tayata rabawa yaran kudi duk wanda ta bawa takeway sai ya mika masa kudi  ,tana raba abinci  tana dubansa tana murmushin jin dadi "thank you my beloving prince  " you're welcome my  queen ya fad'a yana kallonta  bayan sun gama  tare suka koma ciki  suna tautaunawa a falonta  sukayi  masauki ya zauna yana runtse idanuwanshi."Adamcy nah...." !
ya amsa  can kasan makoshi" inshallahu wannan satin zanyiwa su  baba babba maganar aurenku ayi a wuce gurin muryarsa a raunane yace "to sweetheart kuyi duk abinda ya dace na sallama miki komai ."


"bangane ka  sallama min komai ba kana nufin bazaka tabuka komai ba ?"me kike son nayi sweetheart idan akwai abinda kike bukatar nayi ki sanar min zanyi ganin  idan  ya  cigaba da biye mata  maganar auren zasuyitayi yasa yay  saurin  runtse idanuwanshi yana cewa "wayyohhhly sweetheart cikin kwantar da murya tace "ya'akayi Adamcy ? "sweetheart  yunwa nake ji cikina har ya fara zafi murmushi tayi   "ko kunya baka ji ba kmr wani jinjiri ka dai rage wannan shagwabar ka bar wa yaranka  "a'a sweetheart ki barni nayiwa uwata  suma idan sunzo ga guri nan kowa yayiwa mamansa "to ai shikenan bari nasa maryam ta samarmaka abinda zakaci "wace mrym kuma dan Allah kiyi min da kanki karki rage min Jin dadi wannan yarinyar babu abinda ta iya Kuma ma nafi son Ina cin abinci daga hannunki  ni dai gsky banason abincinta "ya Isa sarkin naci amman dole kaci daga hannun matar da zaka aura wata rana ."

"naji amman  ayi sauri ayi min please dariya ya bata sosai  wai ayi sauri ayi mishi  ATA  kenan ko  yaushe idan yana tare da mahaifiyarsa daukar kanshi yake kamar karamin yaro hjy zulaiheart ta d'auki wayarta ta soma Neman layin maryam  sai dai bai shiga ba ta ajiye wayar tana Kiran daya daga cikin masu aiki ."

Tana zaune a d'akinsu  hjy zulaiheart ta  Aiko mai  aiki akirata da hanzarinta ta Isa parlour'n tace "kije ki kawowa Adamcy wani Abu yaci yunwa yake ji ta Dan saci kallon Inda yake tana Jin mummunar fad'uwa gaba  sannan ta gaishesa  sai dai bai Kalli Inda take ba bare ya amsa gaisuwarta  ,Kai tsaye kitchen ta nufa sai dai ta rasa me zata dafa masa shap shap yaci ,kawai tayi tunanin daura masa indomi da kwai ta kawo masa a lokacin data  fito  bata  tarar da  hjy zulaiheart ba sai aunty khadeja  zaune agurin suna magana da ATA ta ajiye akan table din dake gabansa tare da gaishe da aunty khadeja kamshin  indomin da yaji ya ziyarci hancinsa ya balain ta'ba zuciyarsa na take ransa ya baci .

a hankali ta juya zata wuce dan Sam bata jurar tsayuwa a duk Inda yake muryarsa a kasalance yace"ke meye wannan kika kawo ? ta dawo a hankali ta tsaya  tare da cewa  "indomi da ......"a fusace ya dan gyara zamansa ya tsaidaita  "shine abinda kika iya dafawa?  jikinta na rawa ta dubi aunty khadeja dake zaune  tana juya masa Kai "nace shine abinda kika iya dafawa ?ta girgiza  masa kai jikinta na rawa gbdy a tsorace take a tsaye,shi kuwa  kallonta kawai yake da seyx eye's dinsa wanda hakan yasa hantar cikinta cigaba da kadawa  lumshe idanunshi yayi tare da yin shiru  ya  koma ya jingina  jikinsa  da kujerar da yake zaune ya soma motsa labbansa   "wai  irin wannan matar ake min  sha'awar  ajiyewa a gidana  ?yayi mgnr a fili  yana sake jan tsaki a fili "wacce irin  sakariya mata ce wannan khadeja saboda rashin tarbiya indomi fa me zanyi da ita ?

"tuni idanunta suka kawo kwalla bakinta na rawa tace " kayi hakuri bari naje na sake dafa maka wani abu bude idanunshi yayi fesss akanta Yana cewa "shut up me yasa baki dafa ba  tun farko ? ya karasa maganar yana buga mata  wata hadaddiyar tsawa nan take jikinta ya kama rawa  da hannu aunty khadeja tayi mata alamar ta wuce kmr jira take tayi gaba da sauri tana haki ."

"kayi hakuri adamcy   da sannu zata iya komai "har sai yaushe khadeja ? nifa akan wannan matsalar   zamu tabbata muna samun matsala daita bazan juri zama da macen da bata iya komai ba?" shekara ashirin da biyar da wani abu amman ace  mace bata iya girka komai ba  sai yaushe ? "gsky gsky ni dai an  ....... " sai Kuma yayi shiru ya kasa cigaba da mgn "yanzu dai kayi hakuri me zaka ci ni sai na shiga na girka maka da kaina  a fusace  yace "barshi kawai  juyin duniya  yaki yace bai ci haka ta hakura ta barshi  ."tsaki ya dinga ja bai san me ma ya jashi cewar zai ci abinci ba  mikewa yayi ya bar gidan gbdy Aunty khadija tabi da kallo gsky akwai kuskure atattare da maryam dan rashin iya girki babban matsala ne a gidan miji ba wai shekara ashirin da biyar da yan kai ba a tunaninta maryam zata kai talatin dan tsirarau da auta babu yawa .."

******

Maryama na zaune da yammacin ranar monday tana wanke kayan Aunty salma da kayan kanwarta sakina wacce ta kasance diya ga Aunty salma duk da lokacin makarantar islamiyya ne amman ita bata samu damar zuwa ba saboda aikin da matar yayan mahaifinta ta sata , wanke take da iyakar karfinta har ya zamo bata iya wankewa da karfinta sakamakon gajiyar data tsarketa domin ta jima batayi irin wannan aikin ba tun karfe biyu lokacin data taso daga makarantar boko gashi har yanzu biyar ta wuce sallace kawai ta tasheta daga tsugunno datayi tana faman dikar wanki ."
Sakina ta shigo cikin haraban gidan da sallama babu sukuni a fuskarta dan kallo daya tayi mata ta fahimci haka ganin halin data ganta yasa ta sake shiga cikin damuwa ta matso kusa daita ta tsaya cikin bacin rai " maryama daman wanki kika tsaya shine dalilin da yasa baki zo makaranta ba yau .?"
ta fad'a ranta a bace tana kallon cikin falon Aunty salma."

da kyar maryama ta kirkiro murmushin dole wanda yafi kuka ciwo dan komai ya wuce a zuciyarta dan bata qaunar sa'insar sakina da mahaifiyarta akanta muryarta a sake tace "kayan makarantar nawa ne basu bushe ba shine nace Aunty salma ta kawo wankinta na wanke da naki dan zaman bazai min dadi ba tunda bazan samu zuwa makaranta ba ta fad'a mata haka cikin zaro wani kaya daga cikin tarin kayan dake ajiye a gefe guda tana qoqarin dannashi cikin ruwan wanki sakina ta fixge cikin fushi tana cewa "wallahi karya ne nafa san halin mama itace ta hadaki da wannan aikin aikin daya yafi karfin ace mutun daya ne zai yi ni ban san me yasa mama take yin haka ba ..."


Aunty salma ta fito daga cikin dakinta sakamakon jin maganar diyarta "sakinata har kin dawo sannu da dawowa sakinata ta fad'a tana qarasowa ta dafa kafadarta cike da kulawa da tsantsar soyayya sakina ta zumburo baki "haba mama yanzu abinda kikayi ya dace dan meye zaki lodawa maryama uban wanki haka alhalin kina sane da cewa ko mu duka muka hadu bazai qare acikin kwana biyu ba haba ni wallahi wallahi bana só abinda kikeyi wa yaruwata sautari umma tana sanar dake illar haka karfa ki manta maryama ba baiwa bace a gidan nan ' ya ce kamar kowani d'a acikin gidan nan ko bakya kaunarta ita da mahaifiyarta bai kamata ace kina daukar abubuwan wahala kina sakata ba tunda ko babu komai yaruwata ce ko dan ni ya kamata kina son maryama saboda ina sonta ina qaunarta in har soyayyar da kike min ta gskiya ce ."

Aunty salma ta kwabe baki "sannu sarkin yan iyayi ta fad'a a zuciyarta amman a zahiri cewa tayi "meye acikin dan wannan aikin yanzu dan na saka maryama dan wannan aikin zai sa Kiyi zargin bana sonta ne ko wani abu ? tô idan baki sani ba bari na fad'a miki ina mata kwadayin samun lada ne shiyasa nake sakata aiki yanzu Ke kin san irin ladan da zata samu har idan ta gama min ."?

"To ni me yasa baki sani ba tunda aikin lada ne in har idan kwadayin lada Kike mata ?" Ki dinga hadawa dani daita gsky ni banaso ." maryama na durkushe hawaye suna son zubo mata daga cikin kwarnin idanunta amman ta dannesu dan kawai bata son sakina ta fuskanci damuwarta dan tasan dole sai ta qarawa yiwa mahaifiyarta bori ita km abinda bata só kenan taga suna samun sabani akanta da mahaifiyarta domin ita kam tarasa gane maanar hakan rashin kunya ce ko gaskiya take fadawa mahaifiyarta da ta kasance damuwa atattare daita da tata mahaifiyar "

"shikenan sakina daga yau na daina Kiyi hakuri ina sata ne dan tafiki kuzari yanzu muje kici abinci ai kuwa sakina taki binta "wani irin muje naci abinci ki dai zo mu hadu har dake mu qarasa wanke sauran kayan Aunty salma tabi wanki da maryama ta wanke sama da rabi ta waigo ta dubi sakina "a'a ki bari ta qarasa tunda sauran ka.." A'a wallahi ki tsaya dai mu qarasa tas ita ba mutun bace tun rana take ta faman aiki kamar wata inji."

Aunty salma tayi shiru tana duban yarta ta ja tsaki ta nufi hanyar dakinta tana cewa "ai sai dai idan ke zaki iya ni dai babu abinda zanyi taka nas naje na arota wajen uwarta shine dan tsabar iyayi irin naki zaki ce ga zance ga magana da yanzu Ke na saka bazakiyi ba dan yanzu kinga na saka maryama shine zaki zo da shegen iyayi shikenan ki tayata ku qarasa tare ta wuce tana bala'i maryama na tsaye batare da tace uhm ba bare uhm uhm dan bata son tayi laifi dan a yanzu ma tana hankalce da Aunty salma harararta take sakina ta gyara botiki ta cire hijab dinta ta sunkuya ta tura mayafinta da maryama Ke qoqarin turawa cikin ruwan wanki ta fara wankewa da sabulu data tsinta acikin ruwa ."

"Why sakina ? mai haka ki barni na qarasa mana bana son naga kina sai sa da mahaifiyarki akaina ki daina babu kyau tunda kinga ni bana yiwa Aunty haka "itama ai abinda take miki babu kyau ko dan ba itace ta haifeki ba kullum sai ta dinga zuwa tana aroki dan taga Aunty shiru shiru bata son magana aikin yau da dabam na gobe dabam ta hanaki zuwa makaranta malam mustaphata sau uku yana shigowa tambyarki nace bakizo ba kina gida bakya jin dadi "ai ba ita kadai Ke sakani aiki ba umma ma ina yi mata "eh kina yiwa umma amman ita tasan daidai dan bazata barki kina aiki har wannan lokacin bakije islamiyya ba kar ma ki hada mama da umma dan ba abu daya bane ."

maryama tayi shiru Tare da sunkuyar da kanta kasa tabbas akwai bambamci tana son aikin umma fiyye dana kowa ko babu komai tana qaunar mahaifiyarta kum tana tausayawa rayuwarsu tun kafin mahaifinsu ya bar duniya ta kalli sakina tana son hanata wanki amman tasan bazata yarda ba kawai ta cigaba da kallonta ita yanzu abinda yafi damunta yunwa take ji sosai domin Aunty salma bata bata ko ruwa ba wai sai ta gama sallah ma da kyar tayi ."

Sakina ta cire hannunta ta shiga kitchen ta dauko plet din abinci ta fito ta daura mata akan cinyarta "kici !ta tsurawa abincin ido tana kallona batasani ba itama sakina ita take kallo ta matsota da sauri tana son sani abinda yasa tayi shiru bata fara cin abinci ba maryama tayi tsuru itama haka ta kalli abinci ta kalli maryama "ko abinci yayi kadan ne?ta fad'a girgiza kai maryama tayi "ya ma yi min yawa "to me yasa kikayi shiru kina tunani ?" Kai sakina kina son damun kanki akaina ta fad'a tana soma cin abinci jikinta babu kwari ga rawar da yake saboda yunwar da take ji maryama bata bar bangaren su sakina ba sai daf da magariba shima da taimakon sakina ne ."

A matukar gajiye ta shigo part dinsu ta zauna akan kujera jikinta tattare da tsananin gajiya Aunty ta qaraso ta tsaya akanta "ya naga duk kinyi wani iri ko kin aikin da yawa ne ? numfashi ta fesar tare da waskewa dan bata son nunawa mahaifiyar ta damuwarta domin duk hakurinta taji irin aikin datayi yau sai taji ciwo aranta dan haka ta dubi mahaifiyarta tace "babu komai ai aikin ma bashi da yawa kuma har munyi mun gama tare da sakina sai lokaci ta saki jikinta ta zauna kusa daita "sannu princess dina shiyasa nake qara jin sonki araina ta fad'a Tare da shafa kanta da yake sunan datake kiranta dashi kenan atare sukayi shiru Aunty na matukar tausaya mata ita da danuwanta habib kasancewar sun taso cikin maraicin uba gashi dangin ubansu ba qaunarsu suke ba idan aka cire mahaifiyar babansu da yayan babansu da matarsa to babu mutun daya da zata cire."


Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page 12


Aunty tayi shiru tana duban maryama yanayinta kamar kazar da'aka tsamo cikin ruwa gaba daya alamu sun nuna gajiya a tattare daita amman dan karfin halin irin nata take boye mata damuwarta , hawayen da suka cicciko acikin kwarnin idanunta tayi qoqarin maidawa tana danne damuwarta saboda farinciki diyarta ."
ahankali ta dauke kwayar idanunta aKan tilon diyarta zuwa wani bangare dabam tana tunanin rayuwa da abubuwan da sukai ta faruwa daita ta sha wahala arayuwarta shiyasa batason maryama ta sha wahala irin wanda ta sha ,wannan aikin da aunty salma kesata yana matukar ta'ba zuciyarta domin ko ita da tayi sanadiyyar zuwanta duniya bata sakata aiki haka koda tace zatayi ma
End Ads