Uban wa zaki tafi? baki isar man da saƙon dana aikeki dashi ba"
baki na rawa ta furta "Sorry Mah, tace gata nan sabkowa" taɓe baki tayi tana furta "da tsiya sai kinyi turanci kina ƴar matsiyata faƙiriya, maza zo yi Saving namu" dariya su Aunty Meera suka fashe da ita, sosai Muneebba taji ta muzanta da kalar cin mutuncin da sukai mata ga Mazan dake zaune waɗan da suke Binta da kallo hakan ya saka taji ta ƙara muzanta jiki ba ƙwari ta iso wajensu kamar ta fasa ihu, kallonsu ABEED yai yana ɓata rai "haba Mom miye laifinta za kuyi mata wannan cin mutuncin, shin shi talaka dan ya zama Silifas abin takawa? zakuna dinga mata cin mutuncin laifi ne dan tazo nema a karkashinku zaku wulaƙantata kunsan gaba yadda Ubangiji zaiyi daku ne, shin kun san kalar baiwa da ni'imar da Ubangiji zai mata nan gaba ne?"
harara Mom ta zabga masa tana furta "to sannu Malam, wace baiwa Ubangiji yaiwa talaka idan banda baiwar faƙiranci kaga riƙe wa'azinka"
shiru kawai yai yana danna wayarsa dan yasan ba zasu gane ba "Mom a kira Indo tai man Peppersoup" Zameer dake ida safkowa daga Step ɗin benen ya furta, hakan ya saka Muneebba ɗagowa tana dubansa "wow bala'in can Mom Ina kuka samu House maid balarabiya?" Zameer ya furta yana kafeta da ido, kawar da kanta ƙasa tayi taci gaba da yin Saving nasu, wata uwar harara Mom ta zabga masa "to na Mamajo sarki mata kai dai mace indai fara ce koda Mayya ce tana burgeka, ina ruwanka dama ko wace kala ce inda ƴar aiki ce"
"To ita ƴar aikin ba mace bace?" ARYAN ya furta , Zameer ne yace "a to gane Mani hanya, ke Ƴar nan ban son naga farar mace balarabiya kamarki tana wahala ajiye na ida Saving nasu ni dai indai akan farar mace ne na zama bawa daga yanzu"
"Alqur'an ban ga laifinka ba, dama baƙaƙen Ƴan aiki sunyi wa gidan nan yawa babu ƴan Farare" Afif ya furta yana dariya, dariya dukkansu saka saki harda shewa kamar wasu mata, Mom kuwa bata ƙara cewa ƙala ba, Maheer ce ta safko fuskarta wasai babu wanda zai kalleta yace ta sha kuka, a ladabce ta gaida Mom sannan taja kujera tana zama,dasu Aunty Meera suka gaisa a mutunce sannan su Zameer, Muneebba dake tsaye ta jawo Warmer tai saving ɗin Maheer "tnx pretty" Maheer ta furta da murmushi itama murmushin tayi tana ja baya ta tsaya, Tunda Zaidu ke sabkowa yake kallon Muneebba da kuma Mamakin abinda ya sakata sanya kayan House maid ya dai tabbatar wannan ɗin ita ce Matar Bobbi ba wata ba, Murmushin gefen baki ya saki yana kallon Muneebba, babu wan da yaiwa Magana,ya kalli Mom yana furta "Mom ki aika wannan House maid ɗin takai man Abinci a ɗakina" ya furta fuskarsa ɗaure tamau
tsam Zameer ya miƙe yana jawo Warmer ɗin Abincin yace "Yah Zaidu bari na kai maka Alharam abinda za'a aikata kasan muna kare martabar Musulunci babu yadda za'ayi zuƙeƙiyar budurwa fara tas jinin larabawa taje kai maka Abinci a Bedroom"..................
Da wani kalar kallo Zaidu yabi Zameer yana tauna leɓe,basarwa yai yana ɗaga kafaɗa "ok kai man a ɗaki"
Wata wahalalliyar Ajiyar zuciya Muneebba ta saki tana hamdala ga Ubangiji, "Mah an gama zan iya tafiya" ta tambaya bakinta na kyarma, wani banzan kallo Mom ta watsa mata tana faɗin "daman na riƙe maki ƙafafu ne na hanaki tafiya?"
jiki a sanyaye ta fita tana matso hawayen da suka tarar mata a fuska, da wani kalar sheɗanin kallo Zaidu ya bita yana sakin murmushin gefen baki
Koda ta fita kai tsaye Part ɗin da zai sada ta da ɗakin Bobbi ta nufa key ta zaro tana buɗe ɗakin, a hankali ta furzar da iskar bakinta tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce tai gudun tseral, bisa ɗaya daga kujerun Falon ta samu tana zama tare da dafe kanta dake mata Azababben ciwo,ɗan kwanciya ta samu tayi ko taji sawaba nan take bacci mai masifar nauyi ya ɗauke ta ba ita ta samu ta farka ba sai wajen 1:30pm sannan ta fara buɗe lumsassun idanunta,a hankali ta ida ware su tana miƙa tare da furta Addu'a, wata irin zabura tayi tana miƙewa jikinta na kyarma ganin wanda ke cikin Falon yana dannan Laptop ɗin sa hankali kwance, "ina....wuni" ta furta a rarrabe cikin tsoro, ba tare da Bobbi ya ɗago ba ya furta "miye ya shigo dake ɗakina?"
"gyara zanyi" ta furta tana matsa yatsun hannunta wanda wannan ya zame mata Al'ada cikin kallon tarin tsanar mace ya ɗago da fuskar sa yana dubanta fuska a haɗe tamau babu alamar sassauci ko rahama ya furta "daga yau bana buƙatar sake ganinki a koda sashen nan, kar ki ƙara shigo man ɗaki da niyyar gyara idan ba haka ba ranki zaiyi mummunan ɓaci"
murya a can ƙasa ta furta "ok sir" tana jifanshi da kallon tsana wanda lokaci guda wata kalar muguwar tsanar Bobbi ta dirar mata a zuciya,
cikin daka tsawa ya furta "miye na tsaya man a kai kina kallona maza fice man a Falo" ya faɗa kamar yai mata dan banzan duka
A hanzarce ta fice ta fita daga side ɗin ma baki ɗaya, waje ta samu tana fashewa da kuka, ita shi kenan duniyar nan kowa ya tsaneta kowa ta raɓa sai ya nuna mata tsana, duniyar nan wane laifi ta aikatawa Mutane da har suke nuna mata tsana har haka? kuka taci sosai dan sai da taji kanta na neman tsagewa sannan tai shiru tana nufar famfan dake gefe ta wanke fuskarta,
*Maheer*
tun shigowar Bobbi Maheer ta gani hakan ya sakata shiga bathroom ta wanka sannan tazo ta cancanɗa uwar kwalliya kamar zata tafi gasar kyau, ƙara kallon kanta take jikinta sanye da rigar dakakkiyar Shadda Arsh color ɗinkin Straight gown wacce taji aiki da Ado sai walwali take gashi ba ƙaramin fito da ainahin hasken fatarta tayi ba da kuma surarta, wuyanta sanye da sarƙar Gold wacce keta walwali da sheƙi, jikinta tabi da manyan turaruka ta feshe shi, Agogon Diamond ta ɗauka tana ɗaurawa a haɗaɗɗen tsintsiyar hannunta, ba ƙaramin kyau tayi ba dan babu namijin da zai ganta bai ji wani abu a kanta ba, ƙayataccen murmushi ta saki, tana ficewa daga ɗakin nata, kai tsaye Part ɗin sa ta nufa gabanta na tsananta faɗuwa koda tazo kan ƙofar shiga ja tayi ta tsaya tana furta sunan Allah shahada tayi tai Nocking,ta ɗan jima tana yi kafin taji an furta "come in" A hankali ta tura ƙofar Falon kanta a sunkuye tana tafiya cikin nutsuwa da kuma birgewa, cikin ɗaya daga cikin kujerun Falon ta samu ta zauna tana kallon Bobbi kamar ta cinyesa, sun ɗauki tsawon lokaci babu wanda ya cewa wani ci kanka, ɗan ɗagowa yayi yana furta "mi ke tafe dake?"
hawayen da take riƙewa ne suka samu damar zubo mata a kunci zuciyarta na mata zafi da ƙuna "Au haka ma zaka ce Yah BObbi? shin laifi ne dan kaso wanda zuciyarka ta Aminta dashi, dacewa ne Abin da ka aikata ace A daren farkommu baka ziyarceni ba,ina ga ko auren ƙiyayya mukai da kai bai kamata kai man haka ba akwai ciwo abinda ka aikata man" ta furta wani sabon kukan na sake kubce mata
tun da take kukan Bobbi ke jifanta da wani kalar mugun kallo mai rikita wanda ake mawa, "yaushe mace ta samu damar da zata furta masa haka, yaushe mace ta samu zarran kallon ƙwayar idonsa harta furta masa haka, mace ita ce wacce yafi tsana a rayuwarsa, Abinda ya ɗauki Mace maƙaryaciya maci Amana muguwa kuma Azzaluma, makira, mace ce mafarin tarwatsa masa dukkan wani farin ciki, shi yasa bama zai taɓa bawa mace damar da zata furta masa koda kalma ɗaya bace" ya furta a zuciyarsa yana sake bin Maheer da kallon tsana
tun da yake bin ta da kallon jikinta yai sanyi wani kalar tsoronsa da shakkarsa ta shigeta,ba tare daya tanka Mata ba ya miƙe yana tattara Laptop ɗinsa ya shige bedroom,da kallo ta bisa tana miƙewa itama fuskarta tayi jawur ɗan sai ta nutsuwarta tayi tana fita,kai tsaye wajen Mom ta nufa tana shiga Falon ta faɗa cinyar Mom tana fashewa da wani kalar sabon kukan, "Maheer mi ya faru" Mom ta tambaya hankalinta a tashe
"Mom wallahi ba zan iya jurewa ba,Yah BObbi har yanzu bai damu dani ba,yanzu haka da naje wulaƙanci yai man" Maheer ta faɗa kamar zuciyarta zata faɗo ƙasa dan takaici da baƙin ciki
"duk magana da nasihar da nayi Wa Bobbi bai ji ba, kiyi haƙuri Ƴata kiyi shiru Ni da kaina zan jawo hankalin Mijinki" Mom ta faɗa
shiru tayi tana share hawaye "Amma Mom ai nasan ita waccan ba haka yake mata ba nice kawai baya ƙauna"
kallonta Mom tayi tana furta "haba ita ɗin banza ita da ƴan aikin gidan nan ma sun fita gata da ƴanci kisha kuruminki ke ɗaya tal a wajen Bobbi babu kamarki Ni da kaina zan jawo maki hankalin mijinki
sannan ita waccan na mayar da ita kwandon shara a gidan can dan har Abada bazan taɓa barin Bobbi saninta ba, Dan na mayar da ita cikin Ƴan Aiki ba zaki taɓa gane cewar Matar Bobbi bace"
girgiza kanta Maheer tayi "Amma Mom kina ganin kin kyauta abinda kuka aikata itama fa Ƴa ce kamar ni"
kallonta Mom tayi tana faɗin "Maheer ba zaki gane ba, nasan kin ga wacce na aika maki a ɗazun kizo kici Abinci, kinga kalarta kinga surarta wane Namiji ne zai ga wannan bai sota ba? bana son BObbi ya ganta ne ballantana harya faɗa tarkon sonta,gashi kin san ɗiyan talakawa da iya Asirce _Asirce"
gaban Maheer ne ya faɗi jin cewar Muneebba ce Matar Bobbi, "Duk da haka Mom baki kyauta ba dan Allah ki cire ta a jerin ƴan aiki ni wallahi tun a ganina da ita na farko naji ta kwanta min a rai sannan zubinta da yanayinta ya bani tausai"
kamar Mom ta rufe Maheer da duka haka take ji dan takaici "wallahi Maheer baki da hankali har yanzu baki hankali ba aka gaya miki ita kishiya abar tausayi ce to wallahi janza hali tun wuri"
girgiza kai kawai Maheer tayi ta san da cewar tabbas Mom sunyi nisa ba zasu gane ba, hakan ya sakata miƙewa ta haura Up stairs, da kallo Mom ta bita kawai
A haka rayuwar taci gaba da tafiya ba wani sauyi sannan a hankali Maheer ta din ga jawo Muneebba a jikinta, haka ɓangaren Zaidu kullum da baƙin ƙudiri akan Muneebba ya shiryawa Muneebba tarko kala_kala amma Allah na tseratad da ita,
Tsaye take ɗakin Zaidu hankalinta duk ba'a kwance, ba dan babu yadda ta iya tun da Mom ce ta sakata gyaran ɗakin Zaidu, a hanzarce ta fara gudun karya zo ya sameta, tana kammalawa ta fito daga bedroom ɗin sai dai turus tai ta tsaya gabanta na tsananta faɗuwa ganin yadda Zaidu ya rufe ƙofar Falon key ɗin a hannunsa yana wasa dashi, wani yawu ta haɗiye tana tunkaro ƙofar da nufin buɗewa, hannu ta saka ta buɗe amma taji ƙofar ƙyam da ita a rufe, juyowa tayi tana faɗin "dan Allah ka taimaka ka buɗe"
Murmushin gefen baki ya saki yana dubanta sama da kasa kafin ya taso yazo daf da ita har numfashnsu na haɗuwa ,Hijab ɗin dake jikinta ya cire "wow" ya furta lokacin da idanuwansa sukai arangama da manyan Boobs ɗin ta wanda suke cike tab a riga, ƙanƙame jikinta tayi tana rufewa, hawaye na biyo kuncinta,tana girgiza masa kai bakinta na rawa saboda tashin hankali " Kada ka keta man haddi ka dubi girman Allah ka ƙyaleni"
shafa gefen bakinsa yai yana cire ƴar singlet din dake jikinsa ya rage daga shi sai Boxer, rufe idonta tayi tana kiran sunan Allah,jawota jikinsa yai yana ƙara ƙare mata, kallo yadda ko ina na jikinta ke cike ,wani yawu ya haɗiye yana kai hannunsa kan Manyan mazaunanta ya fara shafawa yana lumshe idanu,so take ta kufce amma ta kasa saboda riƙon da yai mata ba na wasa bane,"kaji tsoron Allah ka daina taɓa jikin da ba naka ba, ka dubi girman Allah ka ƙyaleni, kada ka keta man haddi, kada kaci mutuncina ta haramtacciyar hanyar nan,"
"tabbas yau zanci mutuncinki sannan naci mutuncin Auren dake kanki, tun da shi mijin naki yaki yai abinda ya dace bari Ni nayi" ya faɗa yana kai hannunsa kan Boobs ɗin ta, wani ƙarfi taji yazo mata ta turesa tana ja da baya jikinta na kyarma tare da kare jikinta
tunkarota ya sake yi a karo na biyu yana neman zare Boxer ɗin dake jikinsa, idanunta ta sake rufewa kam tana jiran tsammani sai dai shirun da taji ne ya sakata buɗe idanunta tana kallon inda yake waya kara a kunnensa,"ok" ya furta yana sauke wayar a kunnensa tare da jan dogon tsaki, kallonta yayi yana furta "kin tsallake target ɗina da yawa amma ki sani next target ɗina ba zaki taɓa tsallakesa ba"
Yana gama faɗar hakan ya wuce bedroom, wani kalar Ajiyar zuciya ta saki tana ɗaukar Hijab ɗin ta ta zira sannan ta ɗauki key ɗin daya ajiye ta bude kofar tana fita da sauri,
Tun daga lokacin dukkan wani dukkan wata hanya da zata haɗata da Zaidu take a kauce mata
Maheer tsaye take tana fito da wasu ƙwayoyin magunguna waɗan da na tada Sha'awa ne sosai hakan ya sakata tanadar su dan yau so take shirinta yayi akan Bobbi, Dan ta Gaji da zaman haƙurin da take koda yaushe matsananciyar Sha'awa na damunta, kai tsaye ɗakin Bobbi ta nufa key ɗin data ɗauka tun tuni ta saka tana buɗewa a hankali, murmushi ta saki tana nufar Freezer ta buɗe ajiyar zuciya ta saki gani lemo ɗaya ne ya rage A Freezer ,ɗaukar lemon tayi tana zuba ƙwayar maganin ciki ta jijjiga shi sannan ta mayar tana ajiyewa , tare da fatan Allah ya sa haƙarta ta cimma ruwa, dan ta tabbatar zai sha kuma yanzu lokacin dawowarsa ne daya zo shi zai fara sha, tun da komai sai da ta tsaya ta fara karantarsa kafin ta aiwatar,
da sauri ta bar Falon tana rufewa ta nufi nata Part din, koda ta shiga wanka ta shiga
*Bobbi*
Tsit ɗakin yake sunyi shiru yayin da Bobbi ya gama magana,jiki a sanyaye ɗaya daga cikin mutane huɗun dake zaune ya kalli Bobbi yana furta "Amma Sir rayukan mu tabbatas suna cikin haɗari, wanda na tabbatar suka gane muna cikin ƙungiyar su da wata manufa to tabbas dukkammu sai munyi ta rayuwarmu, sannan ina ganin da haɗari basu damar da kayi akan su samu nasarar Sace Mailbox ɗin da keda sirrikan Company ka,"
Murmushi mai tarin Ma'anoni Bobbi ya saki yana furta "Yes na basu dama ne domin ina son mu fara buga wasan game ɗin dasu ne tun a yanzu, kamar yacce a baya suka dinga buga wasan Game damu har suka ɗauki rayuwar ɗan Uwansa, ta wannan hanyar ce kaɗai zan iya masu tarkon da zan kama su, sannan hanyoyin dana faɗa muku tasu kaɗai nake son kubi, kada wanda ya kuskura yai kuskure Akan abin da na faɗa muku kubi komai a tsari,kamar yadda suke da tsare_tsare muma haka muke da, namu tsarin,fatan kun fahimta? Sannan ku fara shiri tun a yanzu"
"Ok sir " suka furta dukkansu sannan suna ƙara jinjina girman Aikin da za suyi wanda yake dab da rasa rayukansu, wala su suyi nasara wala kuma ai nasara a kansu, zuciyar kowa da abinda yake saƙawa har suka gama zaman Meeting ɗin
shi kanshi Bobbi yana ƙara jinjina girman aikin dake tunkarosa, wan da tabbas ya san idan yayi sake bashi ba harna kusa dashi sai an cutar,dafe kanshi yayi ƙwalwarsa na sake tariyo masa abubuwan da suka wuce a baya,a duk lokacin daya shiga tunanuka irin wannan yana son ya keɓe shi kaɗai, amma yau yaji yana da buƙatar tunkarar gidan nasu,kai tsaye can yace a nufa dashi,koda yaje ta Falon Mom ya bi ya wuce iya gaisar da ita kawai yai ya haura Up stairs ɗin, da kallo ta bisa kafin ta miƙe ta shiga kichen da kanta ta haɗo masa Abinci sannan ta fito tana neman wanda zai kai masa, kamar daga sama sai ga Muneebba ta shigo domin shiga kichen tayi musu sabon girki, kanta a ƙasa ta gaisar da ita wani mugun kallo ta watsa mata tana taɓe baki kafin tace "ke zo ɗauki Abincin nan ki kaiwa Bobbi sannan idan zaki shiga ki rufe fuskarki karki bari yaga fuskarki" da to ta amsa zuciyarta na bugawa dan ko kaɗan bata buƙatar shiga ɗakin Bobbi
Tun lokacin da Bobbi ya shiga Kai tsaye Freezer ɗin Falon ya nufa yana buɗewa ruwa ya fara ɗauka ya sha, sannan ya ɗauki lemo ɗaya daya rage cikin ɗaya daga cikin kujerun Falon ya samu yana zama,buɗewa yai yana ɗaga kai yana sha,lumshe idanuwansa yayi yana jin wani abu na daban na ziyartarsa, miƙewa yai da nufin tashi ya shiga bedroom ɗin amma sai dai cak yaja ya tsaya sakamakon abinda yaji, nan take jikinsa ya fara rawa wata zufa na fara yanko masa,
Zama yai yana sauke wahalallen numfashi, a dai_dai Lokacin ne kuma Muneebba ta fara Nocking jin shiru ya sakata tura ɗakin fuskarta lulluɓe da niƙabin da Mom ta sakata sanya wa, ta gefen ido Bobbi yaga tsayuwar mace nan take wata muguwar sha'awa ta dirar masa, hankalinsa ya fara gushewa, "fi.......ki rufe man ɗakin " ya faɗa a rarrabe ba zaka gane ma abinda yake faɗa ba
bata ji abinda yace ba illa kawai ta rufe ɗakin, zuciyarta na dukan uku_ukku ta rufe ɗakin tana dawowa gabansa ta tsaya tare da zazzare idanu alamun tsoro sun bayyana a gareta,
Bobbi kuwa ganin mace a gabansa ya saka hankalinsa gushewa babu abinda yake gani da so sai son kasancewa da ita hakan ya sakasa tashi kamar wani tsohon zaki yana jawo Muneebba wata uwar ƙara ta saki bai bari ta ida ƙara sawa ba, ya cire niƙabin dake kanta yana haɗe bakinsu waje guda a zafafe, wani kalar tsosa ta fitar hayyaci