x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 15 - LIFE PARTNER

  • 42001 words
  • 45000 words
  • Out of 73416 words

Category: Love Stories

Views 329

17 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
have time to prepare this kike barina da yunwa Jiddah?" Ta farfara masa ido ta ce "Ai lokacin ina school ne yanzu kuma nayi hutu" daga haka ta mike ta fara serving dinsa, Yusuf ya dan shafa kansa yana kallanta ya ce "Hope haka zakina min a gidana?" Ta juyo tana kallansa sai kuma tayi murmushi ta ce "Accepted" hannunsa ya wanke ya fara cin tuwan yana kallanta, bayan few minutes ya kara kallanta yaga kallansa take, ya danyi murmushi ya ce "Naje wajen kanwarki yau, and u know what?" Nan da nan ta hade rai ta juya kanta gefe, ya ce "Ya akayi Jiddan Yaya?" Ta kara hade rai ta ce "Ni banasan zancen yarinyar" Yusuf ya wara ido yana kallanta ya ce "Really?" Ta daga masa kai, ya ce "To ai watarana tare zamu zauna, dan banda ra'ayin raba muku gida, kinga tun wuri gara ku saba, Fatima bata da matsala, she's kind and nice to stay with" Yana rufe bakinsa taja wani dogon tsaki, ya juyo yana kallanta ya ce "Why the hiss Jiddah?" A fusace ta ce "Then what's my business with her? nina ce banasan kana min maganarta akwai abinda na hada da ita ne" Yusuf ya wanke hannunsa ya dauki phone dinsa dake kan dinning ya ce "Ai kuwa ke kika hada abu da ita, tinda very soon zaku mallaki miji daya" mikewa tayi kamar zata tashi sama ta bar wajen ya bita da kallo. Kwana uku da faruwan haka Yusuf ya kira Abba ya sanar masa maganar auransa da Jiddah, bayan sun gama waya Abba ya sanarwa Ummi, ta nuna 6acin ranta karara a fili saboda bata ta6a tinanin haka ba, fitowa tayi a dakin Abba duk jikinta a mace ta wuce dakinta, Abdul na zaune yana kallo a laptop dinta, ta rife laptop din ya dago yana kallanta ya ce "Nayi sallah fa Ummi" zama tayi bakin gado ta ce "Kiramin Rafi'ah, kai kuma ka wuce" a hankali yace to sannan ya fita a dakin ya rufo mata kofa, fitowanta a wanka kenan tana goge jikinta Abdul ya shigo, ya tsaya bakin kofa ya ce "Anty, Ummi na kiranki" daga haka ya fice a dakin, cikin sauri ta shafa body lotion ta shirya cikin doguwar riga na atampa sannan ta daura dankwalinta ta fita zuwa dakin Umminsu, gently ta tura kofar ta shiga da sallama, Ummi dake zaune ta ce "Come here" sai da kirjinta ya buga ganin yanayin mahaifiyarta, a tsorace ta karasa ta zauna a kan carpet ta ce "I'm here" Ummi ta juyo tana kallanta ta ce "Da gaske ne Yusuf aure zaiyi?" Rafi'ah ta daga mata kai, Ummi ta ce "And that's what u choose for yourself?" Kanta ta sauke kasa bata ce komai ba, Ummi ta ce "Well, kiyi duk abinda kika ga ya dace Rafi'ah, har nawa kike da zaki auri me mata? Don't u see ur mates? Kowa kokari yake idan ya gama secondary school ya samu admission yaci gaba da karatu but ke aure kika sa a gaba" kanta na kasa duk tana sauraron mahaifiyarta, Ummi ta ta6e baki ta ce "Ya miki kyau, idan kinga haka kikeso fine, nidai addu'a shine nawa, kuma duk abinda ya faru dake mine is to say sorry" a hankali ta dago tana kallan Ummi ta ce "I'm sorry" Ummi ta ce "Noo u haven't wronged me Rafi'ah, ina jiye miki gaba ne, shi aure nutsuwa yake bukata da kwanciyar hankali, nasan kuma indai zakije gidan wata to dole ne zakiyi facing challenges, u are too young for that Rafi'ah, bazaki hakura dashi ba idan kika gama Allah ya kawo miki wani kiyi auranki" sai a sannan ta juyo dai dai saitin Ummi ta ce "Dan Allah Ummi kiyita min addu'a, i don't know what is coming over me, ina sanshi Ummi, kuma ita sun dade tare dashi, na miki alkawarin bazan ta6a neman fadan taba idan har Allah yayi shina aura, i promise u this Ummina, addu'ar ki kawai nake bukata" ajiyar zuciya Ummi ta sauke ta ce "Tooo, Allah ya za6a miki duk abinda yafi alkhairi" a hankali ta ce "Ameen" sannan ta mike ta fita Ummi ta bita da kallo.
Shirye~ shirye sosai Umma take na bikin Jiddah, gidansu ma kansa saida aka masa paint from head to toe. Almost everyday Jawad ya kanje ya gaishe da Ummi, wani lokaci ya kawo Mummy su yini, duk da ba'a gida yake kwana ba duk safiya saiya biya ya gaishe da Mummy da Abi kafin ya wuce wajen aiki, ta bangaren Yusuf kuwa tinda ya gama gyaran gidansa Umma ta sa shi a gaba, yau tace ya kawo dubu dari, gobe tace ya kawo dubu hamsin, haka dai kullum, ko kadan kuma baya nuna gajiyawarsa akan hakan, duk abinda suka tambaya ya kam basu, sosai da sosai kuma yake kula da Rafi'ah, baya kwana biyu baije sun gaisa ba, waya kuwa kullum cikin yinta suke hakan kuma na kona raan Jiddah ba kadan ba, idan tayi magana sai yace ai ita kullum suna tare, a haka har biki saura sati daya, a ranar ne kuma Mamin Jawad ta dawo daga Abuja saboda Ikram zata koma school.
Zaune take a gaban mirror tana waya aka bude kofar, tayi still tana kallan wanda zai shigo, ganin Ameera yasa ta sauke ajiyar zuciya dan a tinaninta Ummice, da yanzu ta hau fada, Ameera ta tsaya gabanta ta ce "Matar Doctor Yusuf" Rafi'ah ta danyi murmushi tayi hanging wayar ta ce "Matarsa na gidansu ai" Ameera ta ce "Kema very soon zaki zama ai" Rafi'ah ta sake murmushi ta ce "Daga ina kike" Ameera ta ce "Jiya bakije islamiyya ba, shiyasa nazo naga ko lafiya, kuma dazu nayi ta kiran wayanki baki dauka ba" Rafi'ah ta ce "Ohh, wayan na silent ne, kinsan Doctor used to called much, kuma Ummi fada take tayi wai ina waya da yawa, nikam kawai sai nasa a silent idan ya kira nayi ta wayana, yanzu ma akan idan na gama zan kiraki ne" Ameera ta ta6e baki ta ce "To aikuwa kamar a bakin Ummi" Rafi'ah nata dariya ta ce "Kamar da gaske". Hira sosai sukayi kafin Rafi'ah ta rakata har bakin layi sannan ta dawo gida, tana dawowa ta samu Ummi a parlor ta dawo a aiki, ta zauna tana kallanta ta ce "Sannu da dawowa" Ummi ta ce "Sannu, Anty Halima nata kiranki wai baki dauka ba why?" Rafi'ah ta duba phone dinta aikwa taga 6 missed call dinta, ta ce "I don't know she called" Ummi ta ce "Tinda yau saturday ki shirya Mustapha ya kaiki, batajin dadi ki tayata zama, gobe saiki dawo" dan zaro ido tayi ta ce "Meya sameta?" Ummi ta ce "Zazza6i take, yanzu nayi branching na duba ta" sama Rafi'ah ta wuce ta samu handbag din Ummi me dan girma ta saka kayanta da drugs dinta a ciki sannan ta canza hijabi ta sauko tana kallan Ummi ta ce "To zan tafi sai da safe" Ummi ta ce "Safe, zan kira Abba na fada masa" daga haka ta fita zuwa parking lot.
Mustapha na zaune a balcony din Anty Amina yana kallan idan film a wayarsa, dama nan yake zama indai tana Abuja, Rafi'ah ta karaso kusanshi ta ce "Zaka kaini gidan Mummy yanzu fa" ya mike yana nade tabamarsa ya ce "To Hajiya karama, wallahi wani film nake kalla, yarinyar cikin film din kamar ke, har kama kuke Hajiya" Rafi'ah ta dan juya ido ta ce "Taya za'ai ina Nigeria kace ina kama da Indians" ya ce "Allah kuwa Hajiya, hancinku ma iri daya ne" Rafi'ah ta danyi murmushi ta ce "To zan hadaka da Doctor kuwa" Mustapha ya washe baki yana dariya ya ce "Allah sarki, ai jiya ma daya zo kafin ki fito hira muka sha, ya bani dubu uku, gaskiya kinyi sa'a Hajiya karama, akwaishi da kyauta, gashi fari kaal dan gaye, amma dai bafulatani ne ko?" Rafi'ah na shiga mota ta ce "Sai dai ka tambayeshi idan yazo" Mustapha ya ce "Ai mutumina ne bari ya sake zuwa, anya ba tattarawa zanyi idan anyi aure ba in koma gidanki" Rafi'ah ta ce "Zakawa Abba butulci kenan?" Ya saki murmushi yana jaan motar ya ce "Ai Abba ubane Hajiya karama, tinda nake ban ta6a ganin mutum me fahimta irin Alhaji ba, Allah ya biya shi da gidan Aljannah" a hankali ta ce "Ameen" sannan tayi picking call din Yusuf.
Few minutes ya kaisu gidan Mummy, bayan yayi parking ta masa sallama sannan ta tura gate din gidan ta shiga, a hankali ta sauke kanta ganin Jawad na zaune akan farar kujera dake kan balcony, sai da ta iso dai dai saitinsa ta ce "Ina yini?" Ya ce "Lafiya kalau" daga haka ta shige ciki, Mami na zaune a parlorn da wata kawarta Hajiya Kareema, Rafi'ah ta dan rusuna ta gaishesu, Hajiya kareema ta amsa tana kallanta harta shige part din Mummy, a hankali ta zaro ido ta ce "Wannan yarinyar fa?" Mami ta ta6e baki ta ce "Diyar kanwarta ce, ni wallahi baso ma nake tana zuwamin gida ba, ciwan zuciya ne fa da ita" Hajiya Kareema ta zaro ido ta ce "Ciwan zuciya kuma? 'yar yarinyar nan dako 18 inaga bata cika ba" Mami ta ce "Atooh, ni dai cewa nayi ma ko HIV ne da ita suke boyewa, kiganta fa a bushe sai farar fata, gashi idan ciwan ya tashi saita fita a hayyacinta, batasan ma waye a kanta ba, ni tsorona kar tazo ta ya6a mana wani kalan cutan mu shiga uku, kinga wancen zuwanta ma Ikraam kwana tayi da zazza6i" Haj. Kareema dake sauraron Mami ta ce "Ai gara kuyi nesa da ita" Mami ta ce "To kinga, ina dalili zata dinga min zarya a gida kaalan ta cuci 'ya'yana ta ya6a musu ciwo".
Rafi'ah na zaune gefen Mummy tana matsa mata kafa ta ce "Doctor yace zaizo gaisheki, kuma wai zai kawo maki maganin ciwan kafa, inaga wanda kike shafawa zaki barshi ki gwada wannan" Mummy ta mike zaune ta ce "To Allah ya kawo shi, Yusuf akwai hankali da nutsuwa dan Allah Rafi'ah karki watsa masa kasa a ido, ya soki tsakani da Allah, ki zauna da matarsa zuciya daya, ba ruwanki da kishiyarki ce kiyi iya kokarinki a kanta, i know u are good in caring but pls ki dage kinji Mamana" tana murmushi ta daga kanta ta ce "Insha Allah Mummynah, mezan dafa miki?" Mummy ta ce "Yanzu dai tinda nayi wanka ki hadamin tea, amma lipton kawai da lemon tsami banda sugar" Rafi'ah ta ce "To bari naje" daga haka ta mike ta fito a parlorn Mumny, yanzu kam ba kowa zaune a parlorn Abi, ta wuce kitchen ta dauka mug ta dauraye sannan ta debi ruwan zafi a flask tasa liptopn, tana bude fridge Mami ta shigo, cikin sauri ta ce "Ke dakata" Rafi'ah ta dago kanta tana kallanta, Mami ta rufe fridge din ta ce "Ba kowa ake bari ya bude fridge dinba, ga cututtuka sunyi yawa a duniya, kowa saiya da6a hannunsa a handle din ya bude, irin haka ai sai a dauki cuta" gefe Rafi'ah ta koma tana kallan yadda take goge handle din Fridge din da towel, bayan ta gama ta gefar da towel din ta bude fridge din tana kallan Rafi'ah ta ce "Me zaki dauka?" A hankali ta ce "Leman tsami" Mami ta dauko leman tsami daya ta ajiye mata a kan drawer ta ce "Dama daga yau kina kiyayewa duk abinda kikasan in kin ta6a wani zai ta6a wajen ki barshi kawai, ga mai aiki ki sata tana miko miki" sauke kanta tayi cikin cool voice dinta ta ce "Mami nifa banda wani cutar da za'a dauka" wani kallan rashin mutunci Mami ta mata ta ce "A hakan, ki kalleki fa, to nidai bazance komai ba, amma dai ki kiyaye duk abinda na fada miki, ciwan zuciyar da akace idan mutum yana dashi ka ta6a guminsa kaima saika kwasa fa?" tana rife bakinta ta fice a kitchen din Rafi'ah ta bita da kallon mamaki, kallan leman tsamin ta dinga yi kafin ta dauka ta wanke sannan ta dauki wuka ta yanka shi biyu, tana matsawa cikin tea din wasu hawaye masu zafi suka shiga sakko mata, yanzu har itane za'a ce bazata ta6a waje ba kar ta shafa musu cuta, to cutan me take dashi bayan ciwan zuciya? Shikuma tasan heredity ke kawoshi mostly, dan itama a familyn Abbanta ta gada, Jin kamar footsteps a bayanta yasa tayi saurin goge idanta ta dauka tea spoon, tana juyowa suka hada ido da Jawad, tayi saurin sauke kanta kasa tabi ta gefensa ta fita. Tana kaiwa Mummy tea din wayarta ya hau ringing, ta ciro a jaka sannan ta daga call din, "Ok" kawai tace sannan ta kalli Mummy ta ce "Yazo" Mumny ta ce "To ki shigo dashi parlorn Abi ba sai ya shigo ciki ba" ta ce "To" sannan ta zura hijabinta ta fita, a bakin gate ta sameshi ya jinginu da motarsa hannunsa rike da key, yaci manyan kaya yayi kyau sosai, ta sauke kanta kasa ta ce "U are welcome" ya ce "Thank u Baby, what's wrong with ur eyes?" Ta ce "Daxu abu ya fadamin" ya ce "Ayyah sorry, hope ya fita?" Ta daga masa kai, ya ce "Alhamdulilah", ta dan kalleshi ta ce "Ka shigo ku gaisa" ya ce "Ohk" daga haka ya bude mota ya ciro carton din Malt da leda cike da Apple, yana shigowa gate man ya kar6eshi, da sallama suka shiga parlorn, gate man ya ajiye abubuwan sannan ya fita Yusuf ya zauna kaan carpet yana kallan hoton Jawad dake manne a wall, ba jimawa Mummy ta fito Rafi'ah na biye da ita, tana murmushi ta zauna, ya sauke kansa kasa ya ce "Ina yini Mummy?" Ta ce "Lafiya Yusuf ya aiki kuma" ya ce "Alhamdulillah, ya karfin jiki?" Ta ce "Jiki yayi sauki, Allah ya saka da alkhairi" a hankali ya ce "Ameen" sannan ya ciro maganin ciwon kafan ya ajiye mata a gefe. Sun dan jima kafin Mummy ta shiga ciki, Rafi'ah ta zagayo ta zauna kusa dashi ta ce "Ya Anty Jiddah fa?" ya ce "Tana nan lafiya, yaushe zamuje wajen Ammi ne, ta damu kije mata" a hankali tayi murmushi ta ce "Ko ranar Monday inna dawo a school" ya ce "To Allah ya kaimu" mikewa tayi ta nufi fridge din parlor ta bude ta dauko mirinder da coke sannan ta dora akan tray ta dauki glass cup, tana juyawa Mami ta fito daga part dinta, ta dinga kallanta kafin ta ce "Ke wai wacce irin dabbar yarinya ce, ba ance miki karki sake ta6a mana fridge ba" still tayi waje daya jikinta na rawa, Mami ta kar6a tray din hannunta ta ajiye akan dinning ta ce "Haba, mace kamar mayya, aiko maye yana gane magana wani lokaci" Yusuf dai na zaune yana bin Mami da kallo, Rafi'ah ta koma ta zauna a hankali duk jikinya a mace, ganin sun hada ido da Mami ya ce "Ina yini" ta dalla masa harara, Yusuf ya mike yana kallan Rafi'ah da kanta ke kasa ya ce "Dear, i'm going" daga haka ya nufi kofa, kallan Rafi'ah Mami tayi ta ce "Dama karuwancin naki ba iya gidanku ya tsaya ba harda gidan mutane?" Caak Yusuf ya tsaya jin abinda ta fada, nan da nan hawaye suka shiga sakkowa a idan Rafi'ah, Yusuf ya juyo a hankali yana kallan Mami ya ce "Mama niba mazinaci bane, kuma abinda kika fada saam bai dace ba, saboda baki da shaidar abinda bakinki ya furta" Mami ta ta6e baki ta ce "Idan kai ba mazinaci bane ai ita kowa yasan nata, to tinda tare na ganku ai zance duk kanwar ja ce" Yusuf ya dinga kallan Mami with much surprise ya ce "Mama!!!", bude kofar akai Jawad yayi sallama, Mami ta saki kuka ta zauna akan kujerar dinning, Jawad ya karasa kusanta da sauri ya riko hannunta ya ce "What's wrong Mami?" Ta dago fuskarta hawaye sha6e sha6e ta ce "Wallahi wannan bawan Allan ne Jawad ya cimun mutunci, daga gani ma shaye~shaye yake, saboda kawai nace bako baka gaisuwa ne" nan da nan Jawad ya mike ya daga hannu yayi kaan Yusuf, Rafi'ah ta fashe da kuka, dai dai nan Mummy ta fito a part dinta da sauri har kamar zata fadi...

[7/29, 2:12 PM] My Imaan: *_...شريك حياتي..._*
_{MY LIFE PARTNER}_

*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
_We are here to Educate, Motivate and Entertain our Readers._

_By FATIMA ✍🏻_

_32_

Rike hannunsa Yusuf yayi yana kallan eyeball dinsa da sukai jaa ya ce "How there you?" Jawad ya kwace hannunsa ya cakumi wuyansa yana huci, salati Mummy ta saki tana kallansu ta ce "Na shiga uku, Jawad me nake gani haka?" ganin Mummy yasa Yusuf baiyi attempting ta6a shi ba, Mummy ta janye Jawad gefe tana kallansa ta ce "Maiya faru ne Ahmad?" Juyawa yayi ransa a 6ace ya shige dakinsa, dan shima indai a gaban Mummy ne he can't do anything, Mummy ta kalli Rafi'ah dake kuka sosai sannan ta ce "Ikon Allah, me yake faruwa ne haka?" ganin hankalinta ya tashi yasa Yusuf ya gyara wuyan rigarsa yana kallanta with a little smile ya ce "Ba komai fa Mummy, Allah ya kara sauki" daga haka ya juya ya bude kofar parlorn ya fita. Mami ta dago kanta tana dariya kasa~kasa ta shige part dinta Mummy ta bita da kallo, saam ita kanta ya kulle, she is totally disturb to know what's happening, kama hannun Rafi'ah tayi suka shiga part dinta, Mummy ta ce "Ki rifemin baki ki fadamin meya faru?" Goge hawayenta ta shigayi sannan ta bata labarin abinda ya faru tin zuwanta kitchen da zata hada tea
End Ads