tanan ne ko a delah gizah be?
Fadamun da sauri amed inason sani ne idan a delah gizah za'a Kai.
Kallo biyu yake Mata,
Kallon Sonta da kallon yasan manufarta akansa Dan haka cutar cuta za'ayi yasani Sarai sbd yace gizah zasu take taredashi ta yanda idan an isa zatasan yanda zatai ta watsar dashi ko negestati ta zama acan din ta yarda shikuma Yana sane Sarai ba gizah din dazashi hakama yasan wannan tambayar datake Masa Dan taji idan Wanda za'a kaiwa negestati a gizah ne tsaf zata samu abal dinta tace abadata Amma yasan yanda zaiyi da ita ko taqi ko taso ita din tashi ce shi daya.
Bata fuska yayi kalar tausayi ya riqota Yana cewa"
Padima shiyasa bazan iya Bari abadaki ba sbd anan delah ne za'a bada Kuma qarin cikin abin a yanda naji abeela za'a kaiwa qila mutuminda shine kusan babba acikin jikokin delah ya tsufa ko me zaiyi da mace yanzu?,
Padima bazanso kije rayuwarki ta gurbata ba Zaki samu arziki da mulki Amma baida amfani sbd bazaki more rayuwarki yanda kikeda buri ba gwara muyi aure mutafi gizah acan nasan rayuwa zatai Mana dadi.
Jin Wanda za'a bawa negestati din yasake daga hankalinta tafara girgiza Kai tana cewa"
Badai ni padima yonas ba,
Sam rayuwata bazata mutu ba agurin bautawa tsohoba duk ya zugemin kyau da quruciyaba,
Padima darajata ta wuce Nan wlh bazan yardaba saidai NURU koma meryam za'a bada abada nidai wlh bazan yardaba.
Juyawa tayi ta nufi hanyar gida cikin tsananin tashin hankali batareda ko takansa tasake biba,
Duk rashin hankalinta da girman kanta bazata iya bijirewa iyayenta ba saidai zata fada musu bataso idan sun nace bazata iya musu taurin kaiba saidai
Abu biyune tasani matuqar aka bada ita negestati to rayuwarsu kaf tana cikin hadari sbd duk Wanda aka kaiwa ita ya kwana da ita zaijita ba budurwa ba Wanda hakan babban laifine hukunta kisa itada iyayenta duka idan sunada jini acikin delah wadda ta taba zama negestati shine zata roqar musu sassauci baza'a kashesu ba saidai za'a koresu daga qasar gabaki daya to gashi basuda Yar uwa ko daya delah dama burinta ta auri amed sukoma gizah inda tasan kyawunta saisa kaitsaye tasamu Dan sarauta bayan tasan yanda tayi ta rabu da amed yanzu ga wannan babbar maganar ta bullo yau ita wazata fito tafadawa kada abadata sbd ita din ba budurwa bace.
Koda ta isa gida har wani murdawar tashin hankali cikinta keyi tayi danasanin bawa amed kanta yafiso cikin kwando dari Dan kuwa Sarai tasan masifar hakan a addinance dakuma al'adance.
Tana shiga gida dakinsu tayi da sauri ta ajiye kayan hannunta tafito ta zari buta ta nufi bayi tana kaucewa kallon inda abal da amminsu ke zaune suna binta da ido.
Koda tashiga bayin kasa yin komaima tayi tafito tana qoqarin sakewa tazo gurinsu abal din ganin su NURU sun dawo ta zauna anacin gasasshen dankalin dasukeci da ita.
Kallon NURU abal dinsu yayi hakanan yake sakejin hankalinsa yafi kwanciya da zuwan NURU sbd ita din tafi cancanta duk da baisan waye za'a kaiwa ita ba Amma dai yasan delah basuda tarihi mara kyau Dan haka duk Wanda za'a kaiwa baida fargaba ko shamaki.
Padima yakalla yasake kalla zuciyarsa nasake tabbatar Masa da kamar kaita wani kuskure ne koba komai yafison yabarta ta aura Wanda take Dan burintane ita Kuma NURU bada ita ba'a shiga haqqintaba sbd batada wani buri sai wanda su iyayenta suka yanke akanta.
Ajiyar zuciya ya sauke tareda kallonsu cikin nutsuwa yafara koro musu bayani komai tareda dorawa da cewa"
Padima kiyi hkr da wannan al'amari daza'a Kira da qaddararre sbd tabbas kowane uba zaiso ganin ya aurar da dukkanin 'yayan da Allah ya azurtashi dasu,
Naso ganin hakan Nima kamar kowane uba saidai Allah be nufa zanga na dukkanin 'yayana ba saidai biyu daga ciki Dan haka padima Ina Baki hkr dakuma umartaki dakiyi biyayya wa Ni mahaifinki dakuma al'ada da dole ki karbi wannan qaddarar dan haka saiki nutsu Zaki daina fita daga gobe sbd za'a fara Miki wanka da siracin sabuwar Madara za'a fara kawowa daga DELAH.
Tsit sukayi dukkaninsu kamar ruwa ya cinyesu musamman padima da jikinta yadauki mazari tafara hada zufan tashin hankali Wanda yasa umminsa shiga tunani me firgitarwa kafin wani yayi magana padimar ta bude Baki murya na rawa tace"
Kutashi kuje kuyi tunani inshallah Zakiyi farin ciki da hakan ba dama gidan arziki da mulki kikeso ba Inshallah zakiji Dadi.
Cikowa idanuwanta ke neman yi ta girgiza Kai tana cewa"
Ammi ba hakan bane ni...Ni..
Kuje nace padima.
Kamata NURU da jikinta yagama sanyi tayi Dan ita gabaki dayama ta firgice dajin abinda yake faruwa sbd ita ko delah akace za'a saitaji duk ta firgice bare ace itace zata shiga delah ta zama jininsu Sam firgici ma tunanin hakan yasata shiyasa tausayin padima yashigeta me tsanani duk da tasan padima ita zata iya duk da idan tashiga ita din ba komai bace Amma dai gwara ita zata iya.
Suna shiga daki padima ta zube kan shimfida tana sake shiga tashin hankali wlh Bata shirya mutuwaba,batason mutuwa Ina zata saka kanta dole ta samo mafita.
Duk irin lallashi da kulawarda NURU ke Mata cikin tsananin tausayawa Sam Bata fahimta sbd hankalinta baya jikinta.
Abu biyu da biyu ga zama negestatin tsoho mara amfani,ga tsoron agano ta taba kwanciya da wani Kuma ta shiga delah ga tsoron hukuncin hakan duk saitaji tana neman haukacewa wlh bazata iyaba Gwara abada NURU Dan ita tunda duniya Bata dametaba zata iya rayuwa da tsoho ko baida amfani itadai ba ruwanta can su qarata.
Har gari ya waye Bata rintsa ba sbd tsananin tashin hankali Koda ta fito da safe babu Wanda bai fahimci Bata hayyacintaba duk ta firgice gashi tanason ganin amed suyi magana Kamar me ba halin fita Dan idan Bata samu magana dashiba komai lalacewa zaiyi.
Da maraice saiga manyan bayin delah kusan guda goma sha biyu sunkawo tarin kayan wankan Madara daza'a fara Mata washe gari tana ganin hakan hankalinta yasake tashi jama'ar gari kuwa suna gani suka tabbatar aka fara zarya gidan tayasu ammy murnar samun yancin abal da murnar shigar 'yarsu delah.
Kwanaki goma sun shude da fara gyaran Negestati padima Amma Sam hankalinta a hargitse take takai yanxu ko rintsawa Bata iyayi tun abin na wasa tadawo ko abinci Bata iyaci take tafara wata irin rama da duhun tashin hankali daganan sai kukan dare Wanda yayi masifar daga hankalin NURU da duk duniya taqi jinin ganin damuwa akan fuskar iyayenta da 'yan uwanta ta tashi cikin tsakiyar dare tareda lalubar qaramar fitila ta kunna taga padima zaune hannunta riqeda wuqa tana faman wani irin kuka da sauri ta qaraso ta fixge wuqar cikin tashin hankali da tsoro jikinta yadau rawa sbd ita qaramin abu ke firgitata tace"
Padima me Zakiyi da wannan tafada ta wurgi da wuqar cikin tsananin tsoro.
Sabon kuka padima tasake tana qwacewa tace"
Mutuwa zanyi tunda ko ban kashe kaina yanxuba naje delah mutuwa zanyi.
#MAMUH#
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐๐
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐๐
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐๐
0903 234 5899*_UBAYD MALEEK_*
_(Royalty versus love)_
*_Mamuhgee_*
*4*
Cikin tsoro da rawar murya NURU tace"
Padima kidena cewa mutuwa kina bani tsoro sosai kidaina kuka menene Dan Allah ki dena kina bani tsoro.
Ganin yanda NURU duk ta firgice cikin tsananin tsoro yasa tadan sassauta tayi tunanin amfani da tsoron NURU sbd dama can ita abu kadan yake Bata tsoro saita sake marairaice fuska tana faso wani kukan tace"
NURU idan Banga amed mukai magana ba akwai babbar matsala wlh komai zai lalace zamu rasa komai da iyayenmu duk mutuwa zamuyi.
Zaro manyan fararen idanuwanta NURU tayi jikinta na daukar rawa tana sake padiman takasa magana tana neman yin baya ta fita a rude padima ta riqota da qarfi tana cewa"
NURU wlh dagaske nake idan bangansa munyi magana ba komai zaifaru Dan Allah kimin hanya naganshi idan nadawo zan fada Miki komai Amma wlh rayuwata na cikin hadari danasu abal ma..
Kasa fahimtarta NURU tayi sbd firgici sai rawa da jikinta keyi ganin hakan yasa padiman taja wani qaramin tsakin takaici tareda girgizata da qarfi ta jawota ta direta zaune tafara shafa bayanta tana hura Mata iska tana kiranta ahankali ahankali hartafara nutsuwa tana dawowa hayyacinta saidata rarrasheta tadawo hankalinta tsaf tukuna ta janyota ta kwantarda kanta kan cinyarta tafara Sabin hawayen samun yaddar NURUn tasake fada Mata abinda tafada Mata da farko NURUn daketa ajiyar zuciyar ta qanqame padima cikin tausaya Mata murya amatuqar sanyaye tace"
Padima idan kikaga amed din shine zesa bazaki kashe kanki ba ko?
Eh NURU bazan kashe kainaba Ni sbd ma kune nakeson ganinsa na nema mafita.
Haka ta lallaba NURU taringa marairaice Mata da kuka hartayi nasarar cika tunanin NURU da tausayinta akan alamarin shiyasa washe gari da za'aje wankan ruwan Madara saita lullube fuskarta taje amaimakon padima bayan tayi Mata hanya sunyi sauyin kaya ta fitar da ita gidan masu wankan dasuka ganta saisuka tambaya tace ai yanzu ita za'a ringawa ba padima ba dayake bayin qasane gabaki daya saisuka yarda sbd manyan bayi basa fitowa delah bare akawo musu irin wannan.
Dama Shima NURU taje ta sanar dashi padima zata fito tanason ganinsa shiyasa yaje inda suke haduwa Yana jiranta danshima a mugun qage yake da ganinta Dan wlh Shima be shirya mutuwaba tunda yasamu labarin ita aka bayar yasan qaryarsa taqare kashesa zaayi duk ranarda akaji shine yafara kwanciya da ita.
Kamar munafuka haka take tafiya tana waiwaye tana boye fuska harta iso Yana ganinta da gudu ya qaraso yakama hannunta suka nufi can nesa da gidajensu cikin wani lambu bayan bishiyar ayaba ya rungumeta Yana cewa"
_Ya Allah Padima nafekushi_
(Ya Allah padima Nayi kewarki sosai)
Riqota yayi da sauri Shima cikin firgicin yake yace"
Padima ki nutsu musamo mafita Nima angaya Miki na shirya karban wannan hukuncin ne?
Bazan iyaba nikaina mafitar nake nema.
Zamewa tayi qasa tayi zaman dirshan tana cewa"
Amed kayi gaggawar samo mafita kokuma kawai mu gudu.
Mu gudu muje Ina padima?
Idan muka gudu burirrikanmu fa damuka Dade muna....
Cikin masifar tashin hankali ta katsesa da cewa"
Burin banza tunda Saida rayuwa zamu cika burin,
Ni kaga kawai musan abinyi wlh na cikin masifa wannan wane irin balai ne nasaka kaina aciki amed ka cuceni...
Wani kallon takaici da baqin ciki tai Masa tana cewa"
Sun San da NURUn suka badani sbd tunanin ita wawuyace batada wayo Ni bansan inda zansaka kainaba zuciyata fashewa zatayi....
Da sauri ya durqusa gabanta cikin Dan samun sa'ida yace"
Muyi amfani da sanyin halinta kiyi Mata wayo ki gurbata Mata tunani da tsananin tausayinki ki Bata tsoro da rayuwar iyayenku da kanta zata bada kanta.
Dakatawa tayi da kukan datake ta dago idanuwanta dasuka gama kunbura sukai jajir ta kallesa tana qoqarin karban abinda yafada din cikin nazarin maganar tace"
Kumafa hakane..
Batada wayo zan iya sata ta bada kanta da kanta.
Meyasa banyi tunanin hakanba tun farko?
Meyasa na tsaya Bata lokacina cikin tsoro da tunanin zan mutu bayan inada NURU.
Riqosa tayi da sauri cikin tsananin farin ciki tace"
Amed kashirya komai zai tafi yanda mukeso zanji da NURU sauran aikin idan mukazo tareda ita saikayi naka.
Rungumeta yayi Yana cewa"
Karki damu tunda munada wadda zata shiga tarkon mukuma mu fita kuka yaqare sai Dadi da rayuwar delah gizah dake jiranmu.
Shafarta yashiga yi Yana lallashinta da qara Bata shawarwarin yanda zasuyi hardai suka samu suka sake biyan buqatarsu agurin Saida duhu yadan yi yarakota har bayan gidansu ta zagaya tashige yakoma cikin farin ciki.
Itama cikin farin cikin tadawo gidan ta tararda NURU a daki tana jiranta cikin firgici da tsoron rashin ganin dawowarta kan lokaci tana ganinta ta taso da sauri cikin tsoro ta rungumeta tana sauke ajiyar zuciyar ganinta tace"
Padima kinbani tsoron rashin dawowarki kan lokaci.
Murmushin jin Dadi padiman tasaki tana rungume NURUn tace"
Wallahi Bet'ami afek'irihalewi NURU.
(Wallahi Ina tsananin sonki NURU)
Ajiyar zuciya kawai NURU ta sauke suka qarasa komawa ciki suka zauna ta marairaice fuska tana Shirin fara hawaye NURU ta katseta da cewa"
Padima karkiyi kuka Dan Allah tunda kingansa kinsamo mafitar matsalarki ko?
Girgiza Mata Kai padima tayi tana tsoyayo hawaye tace"
NURU banason mutuwa,
Banason abal da ammi suma su tafi su barku dagake se meryam qilama duka tafiya zamuyi mubar DUNIYAR bansan yazanyiba duk nice na janyo shiyasa nakeson na kashe kaina nahuta kowama ya huta.
Da sauri NURU ta girgiza Mata Kai tana cewa"
Padima bazan iya Bari ki kashe kankiba gwara mu mutu gabaki dayan koma menene yafi Mana sauqi bazamu iya juran rashin 'daya daga cikin ahalinmu ba kidaina fadar hakan muna tsananin sonki bazaki mutuba yanzu inshallah.
Jan numfashin kuka tayi murya na fita daqyar tace"
NURU kinsan menene yake faruwa ga duk negestati dinda aka Kai aka tararda batada budurci tabawa wani??
Ras Ras qirjin NURUn yayi wani mummunan bugawa harsaida jikinta ya nuna hakan sbd rawar daya Dan dauka ta kalli padima da fararen idanuwanta cikin rashin fahimta tace"
Meya kawo wannan tambayar padima?
Sunkuyar dakai tayi tana tsoyayo hawaye tace"
NURU nida amed mun.....
Wani mummunan tarine ya qware NURU idanuwanta suka firfito tafara tarin cikin azaba da tashin hankali tun tana shafa Mata baya hardai dole suka fito daidai fitowar amminsu Nan sukai kanta akaita Bata ruwa Ana fesa amata Amma sosai ta sarqu idanuwanta sunyi jajir sbd azaba cikin fada ammi tace"
Menene ya sarketa padima?
Ammi kawai zaune take saita fara tari shikenan ne kawai.
Fitowa abal yayi daukeda sabuwar madarar raqumi yabata yakuma fesa Mata take abin yafada Mata tafara fidda numfashi daqyar tana rufe idanuwanta cikin galabaituwa.
Padima ta tayata ta watsa ruwa takaita daki itama tadawo tayi wankan tazo tayi sallah saikuma takejin kunyar NURU din Amma Kuma tunda dai amfani takeson yi da ita dole zata fada Mata hakan.
Kwanciya dukkaninsu sukayi babu ko me dogon motsi sbd tunanin da kowa keyi musamman NURU dake cikin tashin hankalin jin masifar dazata samu ahalinsu.
Washe gari ma NURU ce taje wankan ruwan madaran haka zalika takasa sake tankawa padima maganar dasukai din sbd har lokacin shock din maganar Bata saketaba.
Padima ganin ankwana biyu NURU taki cewa komai gashi zuwa lokacin kowa ya shaida NURUn Bata cikin hayyacinta tana cikin tsananin tsoro da tashin hankali saidai anyi tambayar duniya taqi fada sai kuka.
Hankalin iyayensu yatashi sosai musamman da itama padima suka lura duk a firgice take ta bangare daya wankan haryanxu basuda masaniyar idan anzo NURU akewa sai gidan yakoma Kamar gidan da akai muguwar mutuwa sbd gabaki daya kowa baya cikin nutsuwa anyi anyi NURU tafada abindake damunta taqi fada sbd gabaki daya tsoro da firgicin abinda zaisamesu yasa ta kasa dawowa hayyacinta tsoron fadama takeji.
Yau dai padima da takaici da baqin ciki ya isheta sbd saura kwana goma sha biyu cikar wa'adin cikin tsakar dare ta tashi ta sake dauko wuqa yauma tadawo ta zauna tsakar dakin tareda fashewa da kuka yanda NURU zataji Dan dama tasan ba bacci takeba saigashi tana bude ido taga padiman ta daga wuqa zata sokawa kanta da gudu ta zaburo ta riqeta cikin tashin hankali tace"
Padima.
Qwace wuqar ta hau Yi padiman ta riqe cikin tsananin kuka take cewa"
Kibarni NURU gwara na mutu sai kowa ya huta matsalarmu da tsoronmu zai qare idan na kashe kaina shikenan Babu Wanda zaisan abinda nayi bare rayuwar abal da ammi tashiga hadari duk laifinane Dana Bari harnazo yanxu ban Kai qarshen matsalarba gashinan kema nasaki a damuwa bazan iya ganinki cikin damuwa da qunciba NURU sbd Ina tsananin sonki 'yar uwata.
Cikin hawaye NURU tace"
Bazaki iya ganinaba cikin qunci kike tunanin Ni zan iya ganin kin kashe kanki.
Zamewa tayi ta zube qasa tana rusa wani sabon kuka tace"
NURU komai ya lalace a rayuwata
Mutuwata itace salama agareku sbd matsalar ta wuce yanda kike tunani NURU cikine Dani yanxu haka...
Kingani ko gashinan kina neman sumewa sbd jin wannan muguwar masifa gwara na mutu kowa ya huta NURU kibarni kawai....
Kokuwa suka hau Yi akan saita dauki wuqar NURU na riqeta cikin tashin hankali take gabaki daya hankalinta yakasa dauka wai padima harta San bawa wani kanta,mutuncin,qimarta hadda ciki.
Zubewa tayi qasa tareda rushewa da wani irin kuka Wanda yasa padiman itama zubewa tana sakin nata kukan.
Kwana sukayi kuka Koda gari ya waye kowacce fuskarta da idanuwanta sunyi suntum ai Nan hankalin abal da ammi yatashi musamman dasukai tambayar duniya kowacce tayi shiru har Saida abal din ya harzuka yace aqyalesu koma menene idan sunji uwar Bari sunzo dakansu sufada itadai ammi hankalinta bai kwantaba taringa lallabarsu Amma ba wata mgn saima Kamar zurfafa da NURU keyi da tunani.
Jan padima NURU keyi Kamar wata qaramar yarinya harsuka isa inda tacewa amed su hadu suna zuwa kuwa Yana gurin NURU ta jefesa da kallon qyanqyami da baqin ciki take zuciyarta ta gaurayu da tsanarsa saidai Babu yanda ta iya tunda dole cikin biyu daya za'ayi dole shine zataji idan zai auri 'yar uwarta daya lalatawa rayuwa.
Wani abu ta hadiye me Kama da dutsi ta zuba Masa manyan fararen idanuwanta dasuka kusa gigitashi ya dauke Kai da sauri sbd wlh kallon cikin qwayar idanuwanta kawai na iya sumar dashi da duk wani ma'abocin begenta.
Ka yadda da Kaine kawai kasan padima amatsayin 'ya mace?
Da sauri ya gyada Kai Yana satar kallon padiman dake Masa wani kallo.
Sake jeho Masa qata tambayar tayi da cewa"
Kasan cewa tanada juna biyu yanzu haka a jikinta Wanda yake nakane?
Nasani Kuma ashirye nake da aurenta kafinma kowa yasan da akwai cikin Amma Kuma sbd zata zama negestati wannan al'amari yazama mafi hadari ga rayuwarmu mu duka hadda ta iyayenmu,
Wlh inason padima sosai itama tana Sona NURU Amma yanzu tsautsayi daya gitta mukai wannan abin yasa yazama Kamar wata mummunar qaddararmu da iyayenmu da basujib Basu ganiba..