dayake duk a Sanyaye take sai yake ganin kaman yangace take Masa duk yasake sukurkurcewa Wanda ba hakan bane agurinta.
Suna shigowa palon farko itace agaba sbd afia tuni ta shige shikuma Yana gefenta cikin dibbin mamakinta da tsoronta MALEEK suka gani zaune a palon abinda bayayi hannunsa riqeda waya yanayi cikin turanci da yarensa na Amharic Wanda yasa su duka fahimtar da gida yake waya dama mahaifiyarsa sbd Jin yafada sunanta cikin yare.
Dukkaninsu sunsan ko zasu rube agurin bazai dago ya kallesuba musamman ma ita da tana shigowa fararen idanuwansa masu girma acikin nata suka fara sauka tayi saurin sauke Kai zuciyarta na harbawa
Bata tsaya wata wataba ta wuce ciki sum sum tabar Imran a gurin Wanda shikuma ya gyara zaman jiran MALEEK sbd gabatarda kansa amatsayin me neman auren NURU da neman izinin turowa a nema Masa aurenta.
Zaman jiran MALEEK ya dasa tsawon lokaci me tsayi Wanda harya fara sarewa sbd ganin kaman lokacin basa ne MALEEK din bayada Amma bazai sareba haka yayita jira har maleek din yagama.
Barka da dare MALEEK.
Kallo daya MALEEK yayi Masa ya maida kansa kan wayarsa dake sake daukan ringing ya gyada Masa Kai alamar amsawa.
Gyara zama da gyaran murya duk yayi lokaci daya Imran din Yana saka nutsuwa a muryarsa yace"
MALEEK Ina neman izini ne na shigowa neman auren NURU idan an...
Dakatawa yayi daga zancen Yana gyara zamansa sbd ganin kaman MALEEK din baiji abinda yafara fada ba.
Sake bude Baki yayi zaiyi magana MALEEK ya dago ya kallesa da kyau a karon farko da yayi Masa kallon tsaf
Ya bude bakinsa cikin dakakkiyar muryarsa me izza da kamewa yace"
Nayi waya da santiano albeiriteo gobe zasu sauka France jibi zamuyi board meeting na signing contract dinsu
Get yourself ready Kaine zaka kula da contract din har gamawansa.
Yana fadar hakan ya miqe yabar palon Imran yabisa da kallo da idanuwansa dasukai kaman zasu ciko da hawaye,
Shin MALEEK be jisa bane kokuwa zancen ne bai fahimta ba?
Shafa Dan zufan tashin hankalin da fargaban daya tsatsafo Masa yayi duk sanyin AC daya gama gauraya babban Palon Yana girgiza Kai cikin cire negative thoughts yace"
Baiji Mena fadaba gobe zanzo after breakfast nayi Masa bayani daidai.
Miqewa yayi ya fice Yana maida hankalinsa Kuma gurin contract din santiano albeiriteo da MALEEK din ya basa shugabancin handling Wanda bazai taba samun lokacin kansaba tsawon lokaci sbd contact din nada tarin ayyukanda bazasu barka ko lokacin samun nutsuwan bacci me Dadi kayi.,
Tabbas zaizo gobe yakai qarshen maganarsa da NURU agurin maleek kafin aikin yasa yarasa lokaci duk da hakan zai Kira dad dinsa akan maganar.
##MAMUH#
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na bankiππ
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)ππ
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKUππ
0903 234 5899*_Mamuhgee 17_*
*_Turare by awwaba_*
*Assalamu alaikum warahmatullah, shin kinaba amfani da turaren gashi a matsayinki na mace data amsa sunanta idan amsarki aa toga dama tasamu *awwaba scent* *tazomaku* *da turaren fesawa a gashi natural 100% organic *wanda akahada rose water da essential oils tripped action gashi yy kamshi yay kyali kuma moisturiser at *the same time ba anan abun yatsayaba duk wanda yy order zaahada masa da freshener kala hudu ta daki *ta bandaki ta Mopping da turaren wanka a kan kudi 3,000 kacal indai q cikin watan September dinnna ne daganan kuma zasukoma *normal price dinsu, hakanan turarukqn wuta da humra dinmu anyi masu ragi duk me bukata se nememu a 08034236800 ta what's app kokuma ya ziyarci shafinmu a instagram *@turare_by_awwaba mungode*
****************
Washe gari tunda safe yasake dawowa gidan Dan ganawa da maleek Amma sbd rashin sa'a Koda yazo maleek din yafita haka ya juya jiki amace yakoma gida da niyar ya dawo anjima Dan Dole Dole tsakanin yau zuwa gobene damarsa ta qarshe ta ganawa da maleek sbd jibi Ana fara aikin Santiago Babu ranarda zai samu kansa harya samu damar magana dashi.
Ta bangaren NURU itama gabaki daya ta rasa sukuni da walwalarta akan zancen Dan ko abincin kirki tadaina ci kullum saidai tea sbd fargaba da tsoron abinda zai iya kaiwa ya komo
Duk yanda Afia tayi tayi da ita akan abinda yake faruwa takasa Mata bayani dataga kaman ran afian ya baci ne saita fada Mata da Imran nason turowane ita Kuma tana tsoron karatuntane kawai da haka afia ta zaunar da ita tabata wani qwarin gwiwan barin Imran din yayi zancen tahakane zataji idan abin me yiyuwa ne.
Hakan yasa tadan rage damuwar abin cikin ranta tafara jiran tsammani.
IMRAN kuwa Kai yayi mugun daukan zafi sbd duk wata hanyar dazai gana da maleek ta toshe har abin yafara bashi tsoro sai kawai ya yanke shawaran fadawa mahaifinsa Dan shi dakansa ya nema MALEEK din.
Zaune suke a dining suna dinner Kiran FORMER M.AMB JALALUDDEEN yashigo wayarsa yayiwa wayar kallo daya yaci gaba dacin abincinsa a natse harsaida yagama zuwa lokacin yayi Masa Kira kusan hudu sai Ana biyar din ya daga cikin kamewa da ikon sarauta dake yawo cikin jikinsa ya amsa sallamar M JALALUDDEEN suka gaisa a mutunce gaisuwa irinta dattijai manyan mutane kafin M JALALUDDEEN yafara da cewa"
MALEEK nayi kirane akan maganar aure da Imran yakeson yarinyar gurinka wadda yace sunriga sunfahimci juna sosai da ita to.....
Wata nutsatsiyar gyaran murya MALEEK yayi a natse wadda duk wanda yasan mulki da sarauta yasan dakatarwane ga zancen da ake Dan haka M JALALUDDEEN ya dakatar da abinda yake fada
Kai tsaye MALEEK cikin kamewar muryarsa me nuna isarsa yace"
Wannan maganar ba'ayin irinsa a waya.
Hakane tabbas Bata waya bace MALEEK to kabada lokacinda zamuzo sai ayi maganar akai qarshe Inshallah.
Kallon agogo yayi alamar zancen na shiga lokacinsa Dan haka Kai tsaye yace inada tafiya gizah agabana banida lokacin bayarwa idan nasamu time zangani Inshallah.
Daga haka sukai sallama Yana aje wayar AFIA dataji ya ambaci tafiya gizah hankalinta yayi mummunan tashi ta kallesa cikin son tabbatarwa tace"
Dad zakaje delah gizah??
Yana miqewa yace"
Eh Anneti tasamu attack na zuciya yau da safe.
Yana fadar hakan ya wuce gabaki daya.
Bin bayansa tayi da kallo zuciyarta na bugawa tana nanata zancen tafiyar.
Kasa yadda da tafiyar dad dinta zuciyarta tayi dari bisa dari sbd zuwansa zai iya kawo komai na lalacewan faranta da adduar datai shekaru tanayi na ganin dawowar iyayenta tare,
Shin Tata dad zaije delah gizah yanzu bayan zuwansa batareda matarsaba zai bayyanawa duniya cewan sun rabu Wanda hakan daidai yakeda rasa qimarsa da darajarsa hakama Kuma hakan zai jawo kokuma bada damar shigowar wata cikin rayuwar mahaifinsu ko Mata ko negestati.
Dafe kanta dake neman tarwatsewa sbd tsananin tarin damuwa data sawa kanta akan wani irin zazzafan kishi datake jiwa mahaifiyarta Dan haka bazata iya Bari dad yayi tafiyar Nan gizah ba sbd sanin tsananin qarfin iko da dokoki tareda al'adun mulkin irin na delah gizah.
NURU dake cikin Tata damuwar me nauyi tana zaune gefen AFIA din taji yanda takeda sauke ajiyar zuciya alaman Bata cikin kwanciyar hankali ko daya ta bude Baki ahankali cikin kulawa tace"
Kasa waiwayowa tayi takalli NURUn sbd idanuwanta dasukai zuru zuru sbd masifar data sakawa ranta ta kishin mahaifinta ga wata mace
Batareda ta juyoba tace"
Bakomai kawai kaina na ciwo ne shima inaga sbd rashin bacci ne da bansamu nayiba jiyan.
Kafin NURU tayi magana ta miqe ta nufi toilet tashige ta rufo qofa.
Hawaye takeson Yi Amma ta daure tana kallon fuskarta cikin mirror ta rintse ido tana Jin shin mum dinta ta cancanci wannan fadan datake tare Mata kuwa?
Shin idan ta dage ta Hana dad dinta rayuwa da wata mace akan Taya mum dinta kishi tayi adalci a tsakaninsu kuwa bayan mum din itace ta lalata komai tayi watsi dasu ta tafi neman duniya wadda idan ba Allah yasoba har abada bazata samu duniya irinta dad dinsu ba.
Share hawayenta tayi tareda wanke fuskarta ta dauro alwalar azahar datai ta fito tana qoqarin sakewa Dan kawarda tambayoyin NURU akanta.
NURU dake binta da ido ganin babu damuwar komai a kan fuskan AFIA din sai tabar tamabayarta tana sauke numfashi Dan harta fara shiga tunanin kodai maganartane da Imran tazama matsala tunda tasanma kila zuwa yanzu yagama fadawa MALEEK komai.
Farhat ce tashigo daukeda littafi a hannunta tayo gurin NURU ta zauna kan cinyarta tana cewa"
Lewa nakasa gama wannan dubamin kigani.
Sallah Afia ta tayar tana dauke tunaninta daga kansu sbd Sam Babu Wanda zai gane abinda takeji.
Tana idar da sallar tadawo cikinsu suka cigaba da abinda sukeyi da ita Dan tasamu ta fitarda tunani da damuwardake azalzalar ranta.
Har dare tana sintirin yawo tsakanin Palo da 'dakinsu akai akai sbd tanason ganin dad dinta akan ko tafiyarsa delah gizah na Nan.
Har suka kwanta Bata samu ganin dad dinba sbd bai dawoba koya dawo ya wuce sama ya shige Bata saniba gashi tana Kiran Mr Omar Amma wayan Bata shiga haka ta hakura ta kwanta badan taso ba.
Washe gari da safe daga NURU har Farhat sun wuce makaranta ita kadaice Bata tafiba sbd ta sakawa ranta zata zauna harsai tasamu yin magana da dad dinta.
Guraren 11 na safe kuwa saigashi ya sauko qamshinsa na gauraya palon ahankali ahankali sai kyakkyawar fuskarsa dake kame kamar koyaushe
Tai Masa kallon qaunarsa amatsayinsa na mahaifinta datake tsananin kauna da alfahari dashi ta miqe tsaye tana aje laptop din dake kan cinyarta tana amfani da ita ta saki wani siririn murmushi tana qarasawa gurinsa tace"
Good morning dad,barka da fitowa.
Kallon kyakkyawar fuskarta dake yanayi da tasa yayi Yana alfahari da ita sbd juriyarta da iliminta tareda hakurinta ya bude Baki da muryarsa me amon iko yace"
Janyo kujeran dining din tayi ta zauna tana cewa" thank you abal.
Tsit gurin ya dauka suna cin abinci Babu me mgnar sai ita dake cin abincin ahankali sbd son fara kawo zancen tagaji da wasi wasin yin zancen ko kartayi kawai saita kasa dannewan ta aje spoon din hannunta a natse ta kallesa da taushin murya tace"
Dan kallonta yayi tareda sassauta fuskarsa ya gyada Mata Kai.
Sake gyara zama tayi cikin tausasa harshenta da bayyanarda damuwar data Dade da dannewa cikin ranta da biyayyarta ga dad din nata tace"
Dad maganarku da mum zai fito fili idan kaje....shiru ta Dan Yi tana kallon kamewar fuskarsa ta daure taci gaba da cewa"
Idan zancen ya bayyana cewan mum ta tafiyarta tabar...... kallo daya yayi Mata da fararen idanuwansa takasa qarasa sauran zancen ta marairaice fuska tace"
Dad please ko zaka duba kagani kodan sunan mum da naka dazai iya baci.
Tissue ya dauka ya goge bakinsa tareda Miqewa tsaye ya kalleta yace"
Take care princess"ya wuce.
Kasa motsawa tayi kanta na toshewa sbd hakan na nufi zancenta be karbu ba agurin dad dinta sbd hakan da yayi shine rashin amintarsa ga zance idan ankawo Masa.
Miqewa itama tayi tabar gurin Takoma daki ta zauna ta jawo waya ta Nemo numbern mum dinta tafara tunanin takira ko karta Kira,
Fasa Kira tayi tai wurgi da wayar tareda Miqewa tsaye ta sauya Kaya ta fito tashiga mota ta fice daga gidan Dan zuwa dauko NURU datasan yanzu ta Isa gamawa tunda ita yau Bata samu zuwaba.
Tunda suka dawo taketa qoqarin cire damuwarta sbd kada NURU tagane saidai NURUn tana lure da ita saidai batason takura Mata da tambaya sbd batasaniba ko matsalar ta sirrice.
Kwana sukayi ahaka suka Kuma yini ahakan har akai kwana biyu
cikin kwana biyun duk ta Hana kanta sukuni da tunanin al'amarin Wanda take ganin rushewa familynta zaiyi idan wata tashigo cikinsu amatsayin matar dad dinsu ko negestati
Itadaima tafi son iyayenta su shirya koma menene hakan yafi shigowar wata cikinsu.
Ganin dai dagaske AFIA na cikin damuwa me qarfi boye kawai take yasa NURU kallonta bayan sun kwanta tace"
Afia koma menene abindake damunki please ki rage idan bazaki iya ciresaba ko hakura dashiba sbd wannan damuwan naki bamajin dadin ganinki ahaka ko farhat dake qaraman yarinya tafara cewa menene akaiwa AFIA.
Please AFIA kicire koma menene kibarwa Allah a rayuwa dama akwai hakan duk da nasan ke koma menene damuwan ba wani babba bane sbd Babu wani abu najin dadin duniya da Kika rasa Dan Allah ki cire damuwan please baby.
Tunda tafara magana afia ke kallonta sbd wani tunani daya shigota na sha'awar bin dad dinsu gizah Dan koma menene tafison tanacan zatafi samun saukin hanawa kokuma handling maganar rabuwar iyayenta taqi barin ta fita Dan kuwa tasan daga lokacinda maganar ta fita MALEEK na gizah bazai qara awa ashirin da huduba Batareda Matar aure ko negestati ba Dan haka zasu bishi Dan toshe yiyuwar hakan Dan kuwa idan hakan tafaru dad dinta bazai karbi mum dintaba har abada Wanda ita Kuma akan hakan ko kamawa tayi tayi amfani da NURU zatayi Dan Hana wata shigowa rayuwar dad din daidai NURU tayi hkr but she'll have to use her innocence.
Wani numfashi mara karfi ta saki tareda kallon NURUn cikin kauna da kulawa ta riqo hannunta ta rungume tace"
Thank you my NURU" ta rufe idanuwanta ahankali bacci na daukanta.
Washe gari haka ta tashi cikin walwalarta da sakewarta har hakan yasanya NURU da farhat farin ciki sosai har wasan ruwa da basketball sukai yau da yamma a playground Wanda duk abinda sukeyi dad dinsu na gidan dan haka Koda daddare yau taredashi sukai dinner Banda NURU dataqi fitowa tea kawaima Tasha sbd karatun data duqufa dayi Dan gobe tanada zuwa wani court yin wani aikin 4hours dake cikin karatunta.
Acan dining kuwa AFIA ta sanarwa dad dinta sunason binsa Dan Suma su dubo Anneti.
Kallonta yayi kadan tareda maida kallonsa kan farhat dake cewa"
Yes daddy Nima zanje Kuma zamuje da Aunt NURU ma ko AFIA?
Kallon bakin farhat din dako yaushe yake furta sunan NURU ko lewa yayi tareda dauke Kai Yana goge bakinsa yace su zama ready jibi ne tafiyar.
Cikin murna dukkaninsu sukace thank you dad.
Bayan fitarsa NURU tafara wucewa court kafin afia ita Farhat yau Babu zuwa school dinsu.
Sai yamma sosai suka dawo duk su dukansu Koda ta shigo tana waya da Imran da duk yabi ya sukurkurce Mata da cewan amatse yake da MALEEK yabawa su dad dinsa lokacin zuwa.
Murmushi kawai tayi sbd Bata taba tunanin maleek daya Bata ingantacciyar rayuwa tareda 'yayansa zai Bata ingantacciyar rayuwa ta har abada ba ta hanyar bada damar azo neman aurenta Dan tunda haryace idan yadawo zai Basu Daman zuwa ayi magana kenan da yiyuwar barinta tayi aure da rayuwar aure kaman kowaba babban mamakinta data kasa yadda dashi shine yau itace tasamu damar ace MALEEK na Delah gizah guda shine da kansa zai bada aurenta tabbas wannan tunanin idan yafado Mata kanta da tunaninta kasa dauka suke.
Ga tarin dibbin mamakinta tana shigowa Palo Imran suka tarar zaune Yana sako Mata murmushi da wani irin kallon Sonta daya gama yiwa tunaninsa da zuciyarsa mugun kamu saiyakejin kamar bazai iya rayuwa Babu itaba Dan kuwa komai zai iya faruwa dashi idan bai samu NURU ba amatsayin matarsa uwar 'yayan dazai Haifa.
Afia na ganin hakan ta wuce ciki tana Masa dariya da cewa"
Uncle Imran take it easy fa kada ka rasa 6sense dunka akan soyayya mu shiga uku barr IMRAN jalal ya zauce.
Da wata Yar dariyar qarfin hali yabi afia da zancenta idanuwansa suna Jan NURU dake tahowa cikin dogon wando da farar riga sai black scarf daure kanta duk da agajiye take sosai kyawunta ke bayyane tana qarasowa gap dashi ya miqa Mata cup din drink me sanyi da aka kawo Masa Yana cewa"
Have this my love kingaji ko?
Murmushi tasakar Masa takai hannu takarba takai bakinta ta kurba kenan idanuwanta suka sauka cikin na MALEEK dake tsaye da waya a kunnensa yanayi daga Palon ciki take ta qware da qarfi tana sakin tari ta miqawa Imran cup din tarinta na tsananta sosai
Cikin sauri da kulawa ya miqe Yana qoqarin Kai Mata cup din ruwa bakinta Tasha kozata ji sauki sauki sai kawai yaji anriqe cup din ya juyo da sauri sukai ido biyu da Mr Omar dake kallonsa cikin ido Ras ya Dan sake fuskar wata gantalalliyar murmushi tafito Masa yayiwa mum Sarah dayazo da ita kallo daya tayi saurin kallon NURU tana riqota tana Mata sannu tajata sukai ciki
Saida suka shige ya dago ya kalli Imran cikin girmamawar data so kularda Imran yace"
Barr IMRAN idan Babu damuwa zamu iya zuwa palon baqi dake gefen wannan sashen sbd dokokin gidan sun Dan qara tsauri yanzu Babu me sake shigowa sashen MALEEK dagashi sai 'yayansa.
##MAMUH#
**************
Shiru Imran yayi yana bin Mr Omar da ido baice komaiba sbd Kamar bai gama fahimtar me Mr Omar dinba yace Kuma baiyi abinda yace mishi yayin ba, kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya juya ya fice daga Palon Yana fita harabar gidan ya shiga motarshi ya fice Dan Yana buqatan samun iska me kyau Dan yayi refreshing kwakwalsa dayakejin kaman ta toshe baya gane komai.
Mr Omar mabayanshi yabi da wani irin kallo mai ma'anoni da dama, ciki kuwa harda na tausayawa dan ya hango tsantsar soyayyar Nuru a cikin kwayar idonshi wadda yasan abin kamar da wuya Dan kuwa zancen me girma ne dayafi qarfinsu su 'yan qasa qasa Dan kuwa yana da tabbacin aure tsakanin Nuru da Imran ba abune me yiwa ba duk da dai fadan hakan ba huruminsa bane.
Dan
A bangaren Nuru kuwa karfin hali kawai take har lokacin gashi AFIA ta nace Mata akan tafiyar da zasuyi sai anje da ita Wanda takega kaman ta wuce huruminta Binsu delah gizah ziyartar kakarsu uwa sukutum ta MALEEK,
Amma ganin batada zabi na kanta ko ikon kanta Dole ta shirya 'yan kayanta da basuda wani yawa yawancima dogayen riguna ne Dan Bata dauki me wando ko dayaba da zai nuna tasamu dama da