x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 18 - KAMAL NE

  • 51001 words
  • 54000 words
  • Out of 58900 words

Category: Romance Story +18

Views 140

18 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
fuskarta da kirjinta, zuwa shafaffan cikinta. Wata irin raunaniyar ajiyar zuciya Mubina ta sauke da karfi... Ta zabura jikinta na wani irin kyarrrrrma, ta fara ƙoƙarin bude idanunta wanda suka mata mugun nauyi, ga zafi tana girgiza kanta da karfi, amman ta kasa buɗe idanun kurma ihuuu tayi da karfi" Wayyo Allah na!! Umpah bana gani wlh bana gani umpah ƙishi nake ji ka bani ruwa." ta faɗa tana kecewa da kuka jikinta na karkarwa gag-gag. Kamal ya rankwafa yay mata rumfa da kirjinsa ya sanya tattausan hannunsa ya riƙo kafadunta, ya tallafo kanta ya sanya hannunsa ɗaya saman zara-zara gashin idanunta wanda suke kwance luf ya shafa, ya shiga hura mata iskar bakinsa ya meƙa hannunsa ɗaya ya janyo botteI ɗin water ɗin ya riƙota sosai jikinsa ya kafa mata bottel ɗin a ɗan karamin bakinta, da sauri ta fara haɗiyar ruwan ta dora hannunta saman nashi tana shan ruwan sosai. Kamal ganin batada niyar dena shan ruwan ya janye robar ruwan daga bakinta. Ta sauke ajiyar zuciya ta nitsa kanta kirjinsa tana maida numfashi, kuma sai tayi wata irin zabura, ya riƙeta gam itako se ƙoƙarin fizgewa take. Bakinsa ya kai dab da kunnenta Cikin ƙasa da murya yace"ke! maras kunya nutsu kisan da wa kike tare ko yanzu na sake tsinka maki lafiyayyun mari wlh , karamar ƴar rainin hankali." ya faɗa yana shafa idanunta da suke a rufe ruf, jikinta se rawar sanyin yake. Inajin murya a dodon kunnena sai naji wani irin mugun tsoron sa ya shigeni nan take ban taɓa tunanin zan ji tsoron mutum ba haka... Amman yau naji mugun tsoron sa fiye da kome... Sbd ni kadai nasan azabar da naji lkcn da ya tsinkamin marin karshe... Shiru nayi jikina na karkarwa ina jin wani irin sanyi yana shiga jikina se rawar sanyi nake na kasa kwakwaran motsi... Kamal ganin Mubina tayi shiru ta fasa hauka sai rawar sanyi take, yasa yaji mugun tausayin ta ya darsu a zuciyarsa. Jikinsa ya shigar da ita sosai yana shafa gashin kanta. Can ƙasan makoshi yay mata magana dab da kunnenta yace"kina jin sanyi ko?" ya faɗa yana shafa lallausan gashin kanta. Cike da tsoro na ɗaga masa kaina ina nitsa kaina cikin kirjinsa ina rawar sanyi. Murya sa naji yace"Am sorry my kanwar nine na mareki har kika suma ko?" tsintar kaina nayi da girgiza kaina ina kara ɓoye kaina kirjinsa, dan Allah ya gani bana son ko kallan fuskar shi ji nake banida makiyi a yanzu da ya wuce shi se dai a sannu zan rama cikin ruwan sanyi ta bayan gida, dan a yanzu bazan iya masa rashin kunya ba ya ɗarsa min tsoron! sa a zuciyata... Amon muryasa naji cikin kunnena yana cewa"Ok to waye ya mare ki idan ba Kamal ba?" ban iya bashi amsa ba hawayen baƙin cikin tunawa a tsakiyar makaranta yaci mutunci na! hawanye takai ci ke sauka kan fuskata... Ji nayi yana mgn cikin tsawa"Ke!! Maida hawayen ki yanzu nan." ya faɗa yana zaro handkerchief me wani irin daddaɗan ƙamshin sa me sanyaya zuciya, naji saman fuskata yana goge min hawayen. Shiru nayi nayi lamo jikinsa ina sauke raunaniyar ajiyar zuciya da karfin gaske, ina shaƙar daddaɗan ƙamshin sa. Hannunsa naji saman fatar idona yana shafawa yace"Oya buɗe idanunki maza." ya faɗa yana shafa gashin idona. Ƙoƙarin buɗe idanuwana da suka min nauyi na fara yi, amamn na kasa buɗewa... Muryasa na tsinto tsakiya kunnena ya kirani *Mubeena*" da sauri bakina yana rawa nace "Sir... na... Ka... sa... bu... ɗe... idon... na...wa" na fada ina hawaye. Kamal jin abinda Mubina ta faɗa gaban sa ya yake ya faɗi jikinsa na rawa ya ɗago da kanta ya riƙe fuskarta da hannu biyu ya kai bakinsa saman idanunta kawai sai ya fara lasar idanun nata ya shiga tsotsa a hankali yana shafa lallaunsa gashin kanta. Wani irin abu na fara ji na tsirgamin jikina tin daga ɗan yatsana zuwa tsakiyar kaina, nayi saurin ƙamƙameshi ina girgiza kaina nace"Sir ina jin zafi zan iya buɗe idanuna yanzu bari na gwada kaji Sir."na faɗa ina tusa hannuwana tsakiyar sumar kansa mai taushin gaske ina sauke ajiyar zuciya, ina ƙamƙameshi sosai jin yadda yake tsotsar min fatar idanuna, idan ya tsotsi na dama ya saki ya tsotsi na hagum. Kuka na sakar masa da karfi ina dukan kirjinsa. Kamal bakinsa ya janye daga idanun Mubina yana murmushi ya tallafo kanta murya can ƙasan makoshi yace" Ok *Mubee* oya buɗe idanun naki na gani kinsa gabana faduwa wlh." yafaɗa yana shafa fuskana yana huramin iskar bakinsa saman idona. Bakina na zumburo gaba, na fara ƙoƙarin buɗe idanuna amman sam na kasa kirjinsa an fada ina girgiza shi na kece da kuka nace"Sir Kamal wlh bana gani na kasa buɗe idanuna sam..." Kamal da sauri ya rufe mata baki jikinsa ya fara kyarrrma yace"Pls Mubeena ki rufa min asiri wlh buɗewa zaiyi , me zance ma Umpah da wani ido zan kalle su haba Mubee buɗe kinji."ya faɗa yana ɗaga min fatar idanuna na kara sakin kuka da karfi. Kamal yace" Ok yi hakuri yi shiru muje hospital ko?kai na ɗaga masa na tura kaina kirjinsa ina sauke ajiyar zuciya. Hannunsa naji tsakiyar bayana ya zagaye bayana ya dora kansa wuyana, yana gogamin habarsa a dede setin keyata, yana sauke ajiyar zuciya ajere a jere, naji bakinsa cikin gashin kaina, yana cewa"Mubeena ki daina min irin wannan wasan nasan lafiyar ki kalau dan ki rama ne, to pls kiyi hakuri na tuba me kike so yanzu na baki ko na saya maki ki hakura , muje na saya maki na kawo ki gida da kaina har gaban umpah da Mamu cikin ƙoshin lafiya yanzu zan maki ko meye amman pls bari min wasan ido kinji My Mubee kanwata?" ya faɗa yana bubbuga bayana, ya maido bakin sa dab da wuyana numfashinsa na sauka a wuyana ina jiyo bugon zuciyarsa da karfi tana bugawa... Duka na kai masa kirjinsa na saki kuka nace"Wlh Sir Kangiwa bana gani wayyo umpah kazo ya kasheni..." da sauri Kamal ya dora hannunsa saman bakinta yana murzawa a hankali, ta lafe luf jikinsa. Kamla yace"Innalillahi wa'inna ialaihir raji'un!! Mubeena muje hospital ko?" kai na ɗaga masa ina zubar da hawaye. Kamal ya goge min hawayen fuskata, ya kwantar dani saman kujera yace"Ok bari na shiga na ɗauko maki hijab nayi alwalla kinji Mubee." ya faɗa yana shafa fuska. Kai na ɗaga masa ina zumburo ɗan karamin bakina. Kiss ya rankwafa ya manna mani a agoshi ya buɗe motar ya fito ya murza key daga waje dan sam zuciyarsa bata yadda ba cewar idanunta sun ƙi buɗewa, kawai dai wahala take son bashi. Murmushi ya saki ya tura hannunsa tsakiya sumar kansa ya shafi tattausar sumar kansa, jiya yi ana kiran sallah la'asar. Anutsu ya nufi ciki yana ƙarƙaɗa makullan motarsa. Garba ya nufo Kamal da gudu yana washe baki yace"Yallaɓai barka da zuwa kaga namijin duniya , ɗa ɗaya tilo wajan Abubakar Kan Giwa Mai Nasara..." Kamal yace"Garba a yanzu dai ka barni na sami nutsu ina cikin wata yar matsala wacce idan ta girma zanji kunya a idanun duniya na makanta...." ko me ya tuna yay saurin cewa"Bari na nutsu sai kamin kiraranin Ok." yana faɗin haka yay cikin gida. Garba yayi dariya yace" to wa ya tabo mana Oga kuma?" kofar parlon ya danna ɗan madanin ya shege da sallama. Samha ta tarbe sa tana dariya tace"Yaya Kamal gwara da Allah ya kawoka zo na zuba maka kunun alkama da nama Zakiyya da kaina , wlh yayi dadi." ta faɗa tana dariya. Ummah ta kurba ta ajiye cup ɗin hannunta tana dariya tace"Kamaluddin ya naga kana gama fuska naga ai kana son kunun ko baka jin yunwar yamma?" Hafsat tace "my son ya dai kai dawa wai?" Kamal ya saki hannun Samha ya kara sa wajan Hafsat yace"Wlh momy an ɓata min raina ne amman nima naga abin bai kai ya ɓata min raiba, amman wlh ya ɓaci gashi kamar zan shiga cikin wata ƴar matsala , pls idan kunyi Sallah yanzu ku sani a cikin Addu'a kada Allah yasa wannan abun ya zama gaskiya, momy yaushe kika zo ne ina yini bari naje na dawo , Zakiyya saura ki shanye kunun nan kiga yanda zamuyi uwar ci ina Ummah tane?" ya faɗa yana haurawa saman bene. Ummah tace" gata nan kuwa tana bacci ai yanzu zan tasheta na mata wanka , Ai Addu'a kullum cikin yinta muke ɗan albarka babu abinda zai sameka na sharri se alkhairi." ummah ta faɗa tana miƙewa. tace" Zakiyya tashi maza tinda kin koshi aje asha ruwan zafi." Hafsat tace"lallai fa kam Samha ya dai anyi shiru yayanki zai sha yace ransa ne a ɓace wai." Hafsat ta faɗa tana kallon Ummah. Ummah tace"Kamaluddin kenan ya huce ai shida abokan kasuwanci ai su kullum burin su su kuntata ma wanda zai sauƙaƙa kayansa cikin sauƙi domin talakawa suji dadi , to basa so." Zakiyya ta miƙe tace" Allah ya fisu." Hafsat ma ta miƙe domin ɗauro alwalla se su Ameer kawai suna wasa, dan ganin yanayin fuskar uncle Kamal ta hana su bishi sama.
Kamal yana hawa sama bedroom ɗin Samha ya shiga ya sato hijab dogo har ƙasa ya saka cikin leda ti kun ya fito ya wuce bangaran sa se da yayi wanka saboda yadda yake kin zafi ya ɗauro alwalla ya fito, ya shirya ya saka wani yadi ruwan ƙasa me shegen kyau ƙaramin ɗinki ne mai masifar kyau ya fesa sansanyan turare ya kwashi wayoyinsa da makullan motarsa ya fice...

Yana fitowa parlo ba kowa se su Ameer da gudu ya fice dan karsu riƙe shi. Yana zuwa ya boɗe motar tana nan yanda ya barta, se dai tana rizgar kuka tana kiran umpah. Kamal ya shigo ya zauna ya ciro hijab ɗin a leda ya kamota ya saka mata yay ma motar key ya nufi get. Yana fita daga gidan, jin taki daina kukan ya janyota jikinsa bai yi magana ba ya shiga bubbuga bayanta da hannunsa ɗaya ɗayan yana driving, jin ta tsagaita kukan ta lafe jikinsa tana sauke ajiyar zuciya, yasa ya ɗan kara mannata jikinsa ya cire hannunsa daga bayanta, ya ɗauki wayarsa ya shiga neman layin Sageer. Bugo ɗaya Sageer ya ɗaga tare da sallama. Kamal ya sauke ajiyar zuciya da karfi yace"Sageer pls ina son ganinka yanzu da fatan kana hospital?" daga can Sageer ya bushe da dariya yace"Kangiwa ango me zan samu? Gani fa cikin makaranta..." Kamal yaja tsaki yace"To kazo hospital ɗinku yanzu yanzu mu hadu mu dubata." yana faɗin haka ya tsinke kiran, ya maida hankalin sa kan driving. Mubina ta fashe masa da kuka tin karfi. Kamal yace"Ya Salam me ye to kuma? don Allah kibar zuciyata ta huta haka haba ina dalili, ba hospital ɗin zamu ba ko idon ya buɗe ne? Mubina ta girgiza kai tana kara shigewa jikinsa tana sauke ajiyar zuciya. Hannunsa ya sanya yana buga bayanta...
Kai tsaye hospital ɗin da Sageer yake Kamal ya nufa. kusan tare suka iso da Sageer dan yana cewa su hadu su dubata yaji gaban sa ya faɗi. gashi yana kiran Mubina ba'a ɗauka, ya fito a guje ya shiga mota ya nufi hosfital ɗin. Kamal na parking Sageer na parking......


*Labarin nan na kudi ne kan farashi me sauƙi, book 1&2 zaku same shi akan 200N kacal, ga mutanan mu na Niger zaku biya 400F, ba tsauwalawa hakan ta faru ne saboda masoyana na asali, karfa ku sake ayi baku wannna salon na daban ne, wannan karon bana cewa kome kune zaku faɗa insha Allahu, duk me bukatar siya zaku tuntuɓeni ta wannan*
*Lambobin👉🏻+22796515805/ +22792589446, karku manta nera 200 kacal zaku karanta book 1&2 ,Real ladingo na maraba da masoyanta har kullum💃🏻💃🏻💃🏻*

*💖😭KAMAL NE😭💖*

*Book 1*



NA

*Real ladingo*
*Sweet Baby💋*

Ƴar Mutan Niger🤙🏻



```Aslm masoyan Littafin Kamal ne... Dubun gaisuwa da fatan Alkhairi a gareku, nasan dayawa zasu shiga ruɗanin abinda zai faru a cikin wannan pagen... so abinda nake so daku 🙏🏻don Allah kar wacce ta bini pc dan ƙorafi ko shawara ko gyara nace a mafarki abin ya kasance, wlh bazan saurare kuba! Dan haka na tsara labarina kuma ina dalilina na yin hakan, dan haka don girman Allah tin wuri idan kinsa zaki saya domin ki dameni da jaje ko korafi, to na yafe ki riƙe kuɗin ki na riƙe book ɗina, se kuma ku wanda kuka biya kudi, don girman Allah kada ku cazamin kai ko isheni da korafi, kuyi hakuri ku biyo ni muje cikin labarin Kamal ne... Bayan wuya se dadi kuma mutum baya tsallake ƙaddarasa...````


*Daga yau pagen kyauta ya kare.*


*Bismillahir Rahamanir Raheem*



*Ƙarhen😅👉🏻 Free Page😉*


```Page biyu ne na haɗa```` 👉🏻 🅿️2️⃣1️⃣

Kamal yana gama parking ya fara ƙoƙarin janye Mubina daga jikinsa, ta wani tunzuro baki gaba ta saƙala hannunta wuyan shi, tana gujin kuka alamun bata so ya cireta daga jikinsa. Kamal ya zuba mata tsumammun idanunsa, ya fara mgn me cike da rauni yace"Mubeena mun iso hospital ɗin fa tsaya mana na sauka na kamaki mu shiga ciki ok." ya faɗa yana ɓanɓareta daga jikinsa, ya buɗe motar ya zuro kyakyawar ƙafarsa waje, ya hango Sageer na nufo gun motar sa, karasa fitowa yayi ya rankwafo ya kama hannun Mubina yace"Oya tashi muje" Mubina ta kwakwaɓe fusa tana shirin kuka tace"Allah Sir se ka ɗaukeni ni bazan iya tafiya ba bana gani salon na faɗa rami..." Kamal yace"Wane irin rami kuma? Ai ina riƙe da hannunki oya tashi muje." Mubina ta ɓangare baki ta saki kuka tana jijiga kanta tana diddira ƙafafunta... Kamal yace"Ok yi shiru bari na ɗauke ki shi kenan ko...?" Mubina ta ɗaga kanta. Kamal ya sunkuya ya cicciɓeta ya fito da ita ya rungumeta kirjinsa, ya fara ƙoƙarin rufe motar, Sageer ya iso gurin a guje ganin Mubina ce. Yana isowa yace"Subahanallahi me ya sami babyn my one kawota muje to" ya faɗa yana ƙoƙarin amsarta a hannun Kamal. Kamal ya kauce yana kallon Sageer fuskar shi ba walwala, yace"kuji ni da mutum kaine ka kawota ne zaka wani amsheta muharamarka ce?" ya faɗa yana ƙara manneta a kirjinsa. Sageer ya zaro idanu yace"Babban yaya harda gori? To afuwa muje."ya faɗa cikin yanayin damuwa. Mubina kuwa jin murya Sageer ta saƙala hannunta wuyan Kamal ta ƙamƙameshi ta fara magana dab da hancin sa, har tsinin hancin su na haduwa na gugar na juna, hucin numfashin su ya haɗe waje ɗaya, tana mgn a sangarce"my one Sir ne ya mareni bana gani..." Kamal yay saurin saka tattasan hannunsa saman bakinta ya rufe mata baki, suka nufi ciki. Jama'ah se kallon Kamal da Mubina suke yanda suka yi wani irin kyau suka dace da juna.

Suna shiga Sageer ya kai su wani room me kayan gwaje-gwaje komai akwai a ciki. Ya kalli Kamal yace"Wai Kangiwa me ya sami babyn tawa ne?" Kamal ya nufi gun gadan ya kwantar da Mubina yana jona mata wata na'ura, tako saki kuka ta riƙe hannunsa gam, Kamal ya riƙe hannunta gam ya zuba mata lumsassun idanunsa yace"To meye kuma? ba dub ki zamuyi ba pls daina kukan kinji kanwas." ya faɗa yana shafa fuskarta. Mubina ta damƙe hannunsa a cikin nata tace"Sir ni de my one zai duba ni bana so kai ka duba ni ko nayi ta kukan." ta faɗa tana ɓare baki zata saki kukan, Kamal yace"Ok shiru bari ya duba ki" ya faɗa yana sakin hannunta, ya juyo ya kalli Sageer yana tsaye dab dashi duk ya zama wani iri... Kamal yace" Abokina ka dubata da kyau karka biya sangarta ta pls." Sageer yace "Ok wai da gaske bata gani ne?" Kamal yace"ka dai jona mata na'urorin se mu tabbatar." ya faɗa yana lumshe tsumammun idanun da ya buɗe kofar ya fice. Direct masallaci Kamal ya nufa dan yayi sallah. Sageer ya jona mata na'ura a kanta ya haska mata wani abu a idonta, kamar fitila me hasken gaske gaban sa na faduwa yace"Babyna wlh ko da hakan ta kasan ce ina sonki ina kaunar ki , banga halin da zaki shiga bana na rabu dake zan kasance dake har abdan insha Allah , baby." ya faɗa yana cigaba da aikinsa kusan 1 hour. Kamal kuwa yana nan kofar room se kai komo yake gaban sa na bugun uku-uku kar abin ya zama gaske ina zai shiga da kayan kunya? Tabbas da yaji kunya ba karama ba.!! Se kiran sa ake a waya yaki ɗagawa, dan baya da nutsuwa.
Sageer ya sauke nauyaiyiyar ajiyar zucuya, ya cire ma Mubina na'ura da ya ɗaura mata ya zauna kusanta ya ɗagota ya zaunar da yace"Me yasa kika yi karyar idanu baby haba baby me ma wai ya faru ne?" Mubina ta buɗe idanunta tar ta dorasu kan Sageer tace"My one don Allah kamin alfarma karka cema Kangiwa ina gani so nake na rama abinda yamin cikin ruwan sanyi , nasa yaji kunyar da bai taɓa jiba a duniya na bashi wahala ya kasa sukuni ya rasa nutsuwar sa da kwanciyar hankalin sa..."Sageer yay saurin rufe mata baki da hannunsa yace"haba baby mijin yayarki ne fa to meye ya maki ma faɗa min naji idan ya cancanci hukuncin sai mu masa?" Mubina nan ta kwashe kome ta faɗama Sageer yanda abin ya faru... Ta dora da cewa "my one ka yarda ko da sati ɗaya ne na rama kaji." ta faɗa a shagwaɓe tana narai-narai da idanunta. Sageer ya riƙe hannunta, ya ƙura mata idanu yana girgiza mata kai yace"No baby ina sonki bazan so abinda zai cutar dake ba ko na rasaki , kina ɗaukan abin wasa zai iya zama gaske dan Allah babu ruwansa..." ta sakar masa kuka tana riƙe hannunsa tace"pls my one ka temakamin na ƙuntatama Kangiwa pls..."Sageer yace"ke ni fa ba ɗan iska bane najawo abinda nine zan kwana a ciki... Ta yaya zan ɗauki wuka na dabama kaina...? Ko baki san za'a iya cewa a fasa auran sa da Amrah ya aure ki tinda shine ya nakasa ki ba..." Mubina ta zaro shanyayyun idanuta wanda suka rine waje tana kallon Sageer tana turo baki. Sageer yace"eh wlh da
End Ads