Da mamaki abdallah ke kallonta,Yana tunanin wane irin sin abin duniya ne da mom Wai?" Ko jira agama mgn batayi.
Dagowa yyi jin Abba yace Amma fa akwai matsala sbd mai girma president yace in yadawo dg k'asar India da 3 weeks za'ayi bikin bud'e campanin atime din angama ginasa to zaiyi kusan 2 weeks acan,shine nike ganin yarinyar nan zeenat d kikeso ya aura ,ayi auran ta ida karatun acan gdnsa ,sbd bazaiyu wu ayi bikin bud'e campanin bashida aureba ,Kuma na amsa yanada aure be kamata yallabai yaga nakasance me mgn 2 ba .
Yaka gani my son?"
Had'e rai mom tayi tace ai zeenat sai taga karatu zai aureta sbd haka acikin 5weeks Zan nema Masa AURE maana In zabar Masa wacce zai aura ,auren wucin gadi, byn Yan watanni sai yarabu d matar.
Abba yace haba ya....ah ah kaga kayi shiru kawai ayimasa AUREN WATA SHIDDA da lokaci yyi yarabu da ita,in Kuma kafison aganka me mgn biyu to.
Shiru Abba yyi Yana tunanin wannan maganar, yyinda uban gayyar bece uffanba saima ya fice dg parlourn....
Share pls
BY
MMN FAREESA
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐บ AUREN WATA SHIDDA๐บ
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
Story & written by
mmn fareesa
Dedicate to all my fans๐ฅฐ๐ฅฐ๐๐ปโค
ana mugun tare ,naga comments had'e da fatan alkhairi agareni a grps daban daban nagode sosai๐๐ป
p10
"""Ransa bbu dad'i ya isa part nasa" kwanciya yyi Yana tunanin wane irin haline da mom ?"
Tsaki yaja yafi ak'irga , yyinda yakudiri niyar bazai cewa mom komai ba gameda auren datakeso tamasa ,Kuma shima abban bazai Masa mgn ba ,inhar sun tursasa to zai amince amma duk wacce aka aura Masa wlh zata raina kanta agunsa...
Yo inbacin abin mom koni da kaina sai in bud'e campanin da gumina ba sai wani yabudeminba , yafad'a afili had'e da tashi ya wuce bath room...
Washe gari byn Abdallah yagama Shirin yyi break fast sannan yabar riyanatu na gyara Gurin ya nufi part din iyayansa Dan gaidasu.
Tab'e baki riyanatu tayi byn ya fita sbd ganin yadda yaketa cika Yana batsewa,amma ta lura yau Yana cikin damuwa,dan fuskar nan tasa murtuk take tamkar besan miye dariya ba...
apart d'in mom yafara zuwa ya gaida ita ,ta amsa cikin kulawa , sannan ta ce my son kayi hakuri pls kaji wlh zeenat tayi nadamar abinda ta maka Kuma anjima zatazo tabaka hakuri.ina umartarka daka nuna mata ka amince sbd yarinyar nan tana sonka ai yakamata ka Mata uziri sbd fa Kai take kishi ,shiyasa tayi hakan....amma mom Kuma sbd rashin hankali d wayo had'e da sakarci sai ta zargemu ni wlh banison.....ya isa haka kada kace komai..
Sannan mgnar auren da zaa maka yakake gani?"dan gsky banison wannan campanin yawuce ka....haba mom niwlh banison kina haka ko be budemunba inada kud'i kin sani,Abba ma haka zai iya bud'e mun can....ah ah my son wayace maka ana maida hannun kyauta ni na rigada na tsaba maka wacce zaka aura byn wata shidda ku rabu kaga baza a zargekaba da auri saki. Tunda mahaifinka yyi subutar bakiyace kanada aure be kamata Kuma aji ba haka bane gsky...
Shiru yyi Yana sauraronta " can yace nifa mom banida wani zab'i saidai daza a fasa auren harda na zeenat d'in to zanfi kowa farin ciki wlh...,,,,,
Hmmmm baza a fasaba kuwa nagaya maka mungama mgn da abbanka ko"
Tashi yyi hade da cewa to mom , yafad'a fuska bbu walwala... murmushi mom tayi tace na zauna nayi tunanin da wa Zan hadaka ?"sai na tuna da mai aikinka RIYANATU.....
Whattttttttt?" Mikike nufi mom?"
Zauna kaji Mana my son inmaka bayani sbd inada hujjojin yin haka zaifi"
Zama yyi had'e da tsareta d ido"ahankali tace kaga dai da farko iyayenta talakawa be Kuma ba nan garin sukeba ada ,amma yaxun sundawo da zama anan inaso kuyi AUREN WATA SHIDDA da ita akuma sirri nafiso dg mu iyayenka sai Kai d ita kawai zaku sani sai zeenat shima sbd kada ta tashi hankalintane.
Munyi mgn da dad naka gobe zai tura alh bukar yaga mamanta suyi mgn akan suna neman aurenta Nanda sati3 zuwa 4 zaayi auren.
In har sun amince to zasu siya ma ,mamanta gd subata jari ta Kuma saka amata binkice akanka kasan aure' dole Saida binkice in ma tana shakkun bada y'ar tata.
Saidai baaxa a fadi AUREN contract bane zaa dai nuna kana bukatar auren d wuri ita Kuma yarinyar Zan tsorata ta akan dole ta amince in iyayenta suka tambayi tana sonka , sannan Zan Mata alkawarin mai da ita boko sbd harira ta fad'a mun dg JSCE ta tsaya....
Shiru Abdallah yyi yanajin dogon sharhin mom harta Kai aya azancenta"
Tamkar zai fashe sbd bacin rai ,sbd ganin Wai kamarshi zaa tsorata wata can akan tace tana sonsa Wai ta auresa ,Kuma Wai duk arasama wadda zaa ce a aura Masa sai wannan vileger girl d'in k'aramar yarinya mittsss yaja tsaki afili....
Shiru tayi tana mamakin halinsa, sannan ta ce yanxun kaje gun abbanka ka gaidashi sannan ka koma part naka ka turomun wannan yarinyar....
To"yafad'a atakaice, sannan ya fice dg parlourn.
Koda ya shige part d'in abban,samunsa yyi zai fito ya shirya da alama fita zaiyi,fadawa jikinsa yyi tamkar yaro yasaki kuka.,,,
Da sauri Abba yace yah Salam"
My son gayamun damuwarka kaji ?"
Ahankali yace gsky Abba Ni banson auren nan Dan ALLAH ku barni... ajiyar zuciya Abba yyi hade da cewa to shikenan tunda kafison in kunyata agaban babban mutum irin yallabai yadauki mahaifinka mak'aryaci Abdallah na fasa yimaka auren...bazanso sakaka adamuwaba" saidai matsalar mominka da k'yar zata....Abba na amince kayi hakuri Dan ALLAH insha ALLAH zankasance mai biyayya agareku.
Murmushi Abba yyi yace yauwa yaron Abba ko kaifa ,ka daure sbd nasan Kai jarimine insha ALLAH inaji ajikina akwai wani babban al'a mari mai kyau ko akasin haka da zai faru nan gaba , sannan wannan auren na sirrine bazayi shagaliba sbd gudun kada agane sai yanzun zakayi aure nafison aganka d matar ranar bikin bud'e campanin insha ALLAH sbd baniso mai girma president yaji lbarin bikin ,inhar sun amince iyayanta zasu baka ita,to da'a d'aura aure washe gari ta tare bbu wata bidia ko al'ada daza ayi.
Sannan apart naka dake gdn nan zaku zauna,ka fahimta?"
ak'agare Abdallah yace eh sbd yadda yakejin zafin maganar auren.... sannan yajanye jikinsa dg na Abba had'e da cewa to Abba sai kadawo, yafad'a had'e da saurin varin Gurin...
Azuciye ya isa part nasa,yasami riyanatu zaune kan carpet tana kallon indiyan firm a receiver"ke kije inji mom.....batamasan ya shigowa b.
Atsawace yace keee eeee!wawiyar inace?" anamiki mgn, atsorace ta juyo sukayi 4 eyes wata uwar harara ya aiko mata da ita had'e da Jan doguwar tsuka,yace kije momna kiranki , sannan kada ki koma yimun kallo a parlou"kinji ko bakijiba?" Yafad'a atsawace....
Jiki na kirma tace naji, had'e da saurin fita t nufi part d'in mom...
Zaune tasami mom itada aminiyar hjy ikilima wato mahaifiyar zeenat, sallama riyanatu tayi gabanta na mugun faduwa sbd tana mugun jin tsoron mom had'e da shakkarta.
Sama d qasa suka kalleta hjy ikilima ta tabe baki .sannan mom taja tsaki hade da hararan riyanatu dake gaidasu tace ki rik'e gaisuwarki.
Tuni mom ta Fara mgn kamar haka ,dalilin kiranki shine inason saki wani aiki mai hadari saidai zanmki GARGADI 2 na farko kiyi shiru kada ki fadawa kowa na biyu dole ki amince ko kuwa duniyar ta gagareki Zama....zaro ido riyanatu tayi cikinta yyi k'ara k'uuuuuuuuuuu tuni xufa tafara keto Mata.... murmushn samun nassara mom tayi sannan ta zayyane wa riyanatu k'udirinta akan son ta auri Abdallah Kuma AUREN WATA SHIDDA....
Cikin tsoro riyanatu tace Dan ALLAH hjy kirufamun asiri wlh tsoronsa nake ......rufemin baki ai na Masa mgn bbu abinda zai Miki sbd shi mgn Bata sha Masa kaiba saiki kiyaye kada kimasa kuskure akwai dalili shiyasa Zaki auresa inba hakaba ai ke ko darajar matar direbansa Baki kaiba.
daga k'arshe gobe zaa je gdnku gun ummanki neman aurenki inta amince ta fad'a musu suje gun iyayanki maza abasu aurenki.
Cikin tsoro riyanatu tace Amma Dan ALLAH kada kimun komai sannan da way shidda yyi zai sakeni?"
Harararta mom tayi tace eh bbu ragi bbu k'ari ,saiki tafi ko!kin wani kama kallonku d k'wala kwalan idanunki....
Jiki asanyaye Riyanatu ta fice ta na mamakin meke Shirin faruwa d rayuwarsu itada ummanta be?"
Tasan in bata amsaba to komai mom zata iya yimata sbd tunda taji maganarsu rannan ta yarda hjy batada Imani.
Da haka ta koma part d'in Abdallah,tasamu bayan nan,haka ta zauna tana tunani har 12 tayi,saiga wani yyi knock ta bud'e nan yasanar da ita shine zai rik'a koya Mata turanci .
Babu musu ta bisa alambun gdn yafara koyar da ita.
Cikin ikon ALLAH kafin su tashi riyanatu ta iya wasu abubuwa,shi kansa malamin yyi mamakin k'wak'walwarta....
Byn sun tashi dg islamiya ta koma gd ,duk jikinta asanyaye Fatima na lura da ita,harta tambayeta Amma sai tace bbu koma.
***********
Washe gari Gurin karfe 2:30pm su umma na zaune atsakar gd suna fira yyinda mutane na zuwa siyan abinci...wani yaro yashigo yace Wai ance ana son mgn da umman riyanatu inji wani mutum....
Da mamaki zuwaira tace to kace tana zuwa.
Byn fitar yaron ,umma tacewa mama zuwaira tayi hkri ita bazata b sbd batasan kowa agarinba.
Murmushi zuwaira tayi sannan ta saaka hijab ta fice waje.....tafi minti12 sannan ta dawo tana murmushi ta kalli umma tace kisaka hijab naki muje soro bara na shimfad'a ta barma bak'i mukayi sunxo mgn da kene akan dansu nason riyanatu....
Umma tace....
Share pls
BY
MMN FAREESA
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
Umma tace anya kuwa da gaskene?"
Murmushi zuwaira tayi tace muje Dan ALLAH!ta fad'a had'e da daukar tabarma ta nufi soro....
Umma ma tasaka hijab tabi bayanta ranta fal da tunani"
sallama tayi had'e da Zama kusada zuwaira" byn gama gaisawa,alh bukar yyi gyaran murya had'e da cewa to nasandai zakuyi mamakin ganina a wannan lokaci,suna Alh Abubakar da'aki sani da alh buka .nasan kunsan ALH KABIR GIRMA ko?"suka d'aga Kai" sannan yacigaba da cewa ni amininsane yaturoni akan neman iziniku akan zaya turo a nema ma D'ansa auren y'ar ku,wato RIYANATU dake ma D'ansa aiki,wato ABDALLAH dg nan suka Fara soyayya d juna ....
Cikin mamaki umma tace oh D'an yau kenan dama ba aiki takemasa ba soyayya suke?"
Murmushi alh bukar yyi hade da cewa kunsan halin Yara insunason Abu to shine ai Abdallah ya matsa ayimusu aure saita cigaba da karatunta acan insha ALLAH,amma yanxun miye amsar ku?" Umma tayi ajiyar zuciya had'e da cewa da farko dai sai naji ta bakinta intana sonsa sannan muyi binkice akansa d iyayensa tukum saina turaku gun dangin mahaifinta dake k'auyen...
Tashi alh bukar yyi hade da yimusu godiya sannan ya ajiye musu rafa guda ta 1K ya fice Yana cewa ah ah su karb'a sbd jin umma na cewa yabar kud'insa...
byn fitar sa,su umma suka shiga cikin gd"mama zuwaira nata murmushi tace oh ikon ALLAH Ashe alkhairi ne ya maidoku garin nan,ai dama matar mutum kabarinsa ALLAH yasa hakan shiyafi alkhairi.
Umma tace ameen, Amma nifa gsky inajin tsoron ta auresa mufa talakawane gara dai ta auri talaka daidai mu. Kuma bamusan halinsaba....ah ah bintu addua yaka Mata kiyi, maganar hali Kuma gsky dukda ba Wai hudda nikedasu ba to Alh Kabir girma Yana mutunci sosai akwai temakon talakawa wlh ga yadda naji ,Kuma shi Abdallah bama nan yyi karatu ba ,bedade d dawowaba ,Amma inbaki yardaba bara nasaka harira dake hudd'a su dakuma salisu mak'ocinmu dake dreban gdn su Miki binkice akansu..
Ajiyar zuciya umma tayi tace ai bama wannan ba ,sai tazo naji abakinta tukum kinsan Dan yau ,kahaifesa baka haifi halinsaba.
Zuwaira tace hakane tana dariya , yyinda Fatima dake sauraronsu tanad'aki taita murmushi tana tuna yau zata tsokani Riyanatu....
*********
Zaune yake a lambun gdn kan resting cheir. gabansa center table ne da choke d cup akai da riyanatu ta aje Masa"
Idonsa alumshe yaje sai girgiza Kai yake,Yana jiran zuwan Hafiz sbd yakirasa akan yazo yanxun yanason ganinsa...
Yyi zurfi atunani yaji andafa kafad'arsa "da sauri yabude idanunsa dake jajir ya aza akan fuskar Hafiz"tamkar bayason mgn yace pls kazauna friend"
zama Hafiz yyi had'e da cewa lfy dai ko AK?"
cikin damuwa yasanar da shi maganar AUREN WATA SHIDDA da mom ke son tamasa Kuma Wai wannan vileger girl d'in ta zab'a Masa.....hhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhhh...look mlm ba dariya nakiraka kamunba ,shawara zaka bani pls"cewar AK cikin jin haushin Hafiz daketa Masa dariyar.kallonsa Hafiz yyi ido cikin ido yace gsky kaji dad'i wlh... mittsss kaifa d'aniska ne ,Ina maka wani zance Kai kanamun wani"murmushi Hafiz yyi had'e da cewa hmmm to Wai miye abin damuwa anan ai gara RIYANATU akan zeenat gsky Ina maka murna sbd yarinyar ta had'u wlh ๐ฏ% inbacin daka rigani aida nike Shirin yin ta biyu da ita ni wlh dama tuni naga kunyi mugun marching da ita harfa kama na ga kunayi da ita,sbd.....STOP IT kanada matsala wlh kaxo kanamun surutan banza, bacin bashi na kiraka kamunba...wlh zaka jamata wlh ....
Sorry abokina Ni gsky banison kayi auren contract,amma kayi biyayya gasu Abba amma insha ALLAH wannan auren zai Zama alkhairi ,Kuma insha ALLAH baza ka auri zeenat ba.
Tsaki abdallah yaja had'e da cewa suduka bbu choice dina aciki kinsu .....hmmm haba mutumin kadafa ka kamu kazo kana mun y'ar murya nashawo maka kanta , Hafiz yafad'a cikin tsokana....wani purch Abdallah yakawo Masa yyi saurin kaucewa Yana dariya had'e da cewa k'ila mu angwance tare k'ila ma na rigaka sbd ni gsky bbu d,aga k'afa in my feedo ta shigo hannu na yadda nike amatse....tsaki abdallah yaja had'e da cewa banxa Dan akuya... murmushi Hafiz yyi had'e da cewa eh naji kaikuma me zaa kiraka sbd gara ni da Kai....kayimun shiru ga wannan yarinyar nan karma kaja ta kamun raini wlh na fasa bakinta yafad'a in a serious tone...
Riyanatu na k'arasowa,ta sunkuyar dakanta k'asa sannan tace yallabai ko akwai aikin da zanyi maka lokacin islamiya yakusa?"
inkin tanka Abdallah yatanka saima yarufe ido had'e jingina jikin sa d kujerar yamata banza.,,,
dagowa tayi ganin yashareta tace Yaya hafis Ina wuni?"
Murmushi Hafiz yyi yace lfy qlau ,Ashe kina islamiya?"
Eh tafad'a"atakaice.
Kallon AK hafis yyi hade da cewa friend kayi mgn pls kabarta tsaye "kada Kuma ta tafi tayi laifi..
Yakusan second 52 , sannan ya tsina fuska cikin husky voice ya dubeta had'e makamata harara sannan yace ban hanaki kirana da yallabai ba saikace kina gaban d'an sanda mittsss,Wai miyasa inbaki sani surutuba,bakijin dad'i?"
"Ahankali tace kayi hakuri lokaci na tafiya me zanyi?"
Banza yyi da ita"
Hafiy dake kallon su yace riyanatu kitafi abinki kinji...
Juyawa tayi had'e da tafiya.....RIYANNNNNNN cak ta tsaya sbd jin muryar Abdallah ta daki dodon kunnanta , had'e da mamakin jin yafad'i sunanta dukda yarage wasu haruffan aciki,Kuma yau ce ranar daya Fara Kiran sunanta.,sai Kuma taji sunan yyi mugun Mata dad'i amma Bata nuna ba.
Ahankali tace tadawo baya had'e da cewa gani,yadauki wasu second kafin yace ki had'a mun ruwan wanka,saiki tafi....
"To tace had'e da tafiya"
Byn tafiyita Hafiz yabugi kafad'ar Abdallah yace gsky mutumin kana lokaci fa wannan kasaita haka ,kumafa sunan da ka kirata dashi yyi daidai dama haka ake kiranta wlh RIYAN nice name.... Ya isa parrot Kanata zuba kamar ruwa na kirata ne sbd bazan iya kiran sunan har k'arsheba sbd yyimun tsawo sunan...
Murmushi Hafiz yyi had'e da girgiza Kai suka cigaba d fira wacce afirar Hafiz ne yafi mgn.,,,,,,
Riyanatu ce zaune gaban umma "
Umma tace dama Ashe ba aiki kikeba soyayya kuke da yaron nan dama?"
Wani mugun faduwa gaban riyanatu yyi ,cikin dauriya ta kak'aro murmushi ta sunkuyar dakanta k'asa..
Tunani take wato Ashe harma anzo neman auren kenan?"tunda gashi har umma na Mata maganar, lallai hjy abin tsoroce ita yanxun to yanxun daukar suna soyayya da Abdallah ake Mata wannan mai girman kan tsiyar d izza...kin yi shiru bakiyi mgn ba, iyayensa sun Aiko suna son abasu damar suje su nema Masa aurenki.
Kifad'amun gsky kina sonsa ko kuwa?" Cewar umma tana kallon riyanatu...
Shiru tayi tana mamaki da wannan tsaka mai wuya datake aciki"
BY
MMN FAREESA
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
๐บAUREN WATA SHIDDA๐บ
๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ๐พ
Story & written by
mmn fareesa
Masumin mgn a pc ko agrps bbu reply kuyi hakuri pls &pls dakuma rashin jin posting d'ina inada uzuri....
p12
"Ahankali tace eh umma"ta fad'a tana murmushn dole had'e rufe fuskarta Wai taji kunya....
dariya umma tayi hade da cewa ALLAH yatabbatar Mana d alkhairi.sannan cike da jin kunya riyanatu ta tashi t fice..
Aranan ba'a kwanaba umma ta Kira Inna mariya tasanar da ita had'e da neman shawarar ta" takuma amince cikin farin ciki had'e da musu fatan alkhairi bbu bata lokaci umma ta bukaci Inna mariya ta sanar da baffa sule(k'anin baban riyanatu)zuwan bak'in yakuma fad'i yaushe zasu zo?"
sannan sukayi sallama akan duk yadda sukayi zata saka gali yakira su umma tamasu baya ni...
Zaune yake a cikin mota dawowarsa kenan dg wani park,kasancewar da kansa yyi driving bbu Wanda yabisa, ya d'ora kansa bisa sitiyarin na motor yyi zurfi atunani.... k'amshin turarenta da motsin bud'e motar datayi yasakashi dawowa tunaninsa"hiiii baby!
d'agowa yyi ransa bbu dad'i fuska a had'e yadubeta ya juya Kai , azuciyarsa yyi tsaki sbd ganin irin kayan dake jikinta... ahankali tace yakk?
lfy!ya amsa atakaice"haba baby duk kawani daure fuska bbu faraa kasan banason haka ko?"look zeet kinsan halina banason surutu da yawan mgn so pls ya isa"murmushi tayi tace hakane baby amma yakamata kaji meke tafe dani,kasan inasonka sosai am ma Kai ko irin zuwa fira guna bakason yi miyasa ?"cikin k'osawa yace hakan baya cikin tsarina"
Yanzun gsky yakamata kaje gdnmu ayi mgn asan da Kai dna kammala skul muyi AURE....ki sanar