kunga sai ahada auran ku". Safina ta fada.
Tas taji abayan ta. "Ina wasa dake ne"? Yaya Faeeq ya tambaya.
"Faeeq!! Bazan yi tolerating din haka ba. Ka tashi ka bar mana parlor, I want to have a girlie moment with my girls, kaga ya dade bamu hadu ba". Hajiya ta fada.
"Bai sai kin fada ba Ummi, daman ina da niyyan tashi, amma naso in koyama bayarbiyar nan hankali. But anyways gwanda in bar ta da halin ta". Yaya Faeeq ya fada. Sai yayi pointing din Nafisa, ya ce "ke kuma lokacin biki, kar ki yi wuf da wani ki gani, zan neman maki tsoho. So it's better ayi da yaro kafun ran Faeeq ya baci. Yaya Faeeq na gama magana, ya bar wajan.
Yana tafiya kaman wanda kafafuwan sa bazasu taba kasa ba, yi yake kaman yana tsoron in suka taba kasa, zasu bata.
Sun dade a gidan su Nabila, dan sai bayan isha, Hajiya tace ma Yaya Faeeq ya mai da su. Nan ma sanda Nafisa ta ita raba fada. Shi Faeeq, baya gajiya da tsokanan ta, ita kuma bata gajiya da bashi amsa, so shi yasa suke prolonging din issue.
"Wallahi Olamide, in kika bani haushi, anan zan sauke ki. Kuma kin san baki son a bun da zai sa dare ya same ki a waje, zanga yanda zaki koma gida". Faeeq ya fada a fusace.
"Ka sauke ni mana, sai me?
Ai ba mutuwa zan yi ba. Inada kudi na da zai kaini har gida". Itama ta fada tana huci.
"Sai ya tsayar da mota, ya fita, ya je side din da take. Daman tana back sit ne, Nafisa kuma na passenger's sit. Kuma anyi hakan ne, saboda kar suyi fada, amma ina abun nasu a cikin jini yake.
Daya tsaya abakin kofar, ya bude, sai ya ce "ki fita".
Kaman jira take, ta yi hanging din jakarta , dan daman tasa jakar saman cinyar ta ne. Tana hanging din jakar, ta fito. Nafisa na ganin haka, ita ma ta fita. Sai ya ce "baki da case Nafy, ki koma ciki. Daman wannan yar rainin hankalin ne".
"Gaskiya bazan iya kallon habibty na haka ba, so duk hukunci daka dauka akan ta, kaman akai na ka dauka. Ka wuce kawai, mun gode, dan na san da kyar in habibty zata kara shiga motan nan". Nafisa ta fada.
"A'a ke ba ruwan ki, ki shiga, kuma ita din ma, nasan zata shigo ai, ba yau muka fara ba". Yaya Faeeq ya fada.
Faeeq da Nafisa annan suna settling matter, ita ko tana can tana neman adaidaita.
Tana samu, tayi ciniki da shi, sai ta ce "habibty kizo na saman mana adaidai ta, kizo mu wuce time na tafiya". Ai ko tana jin haka, ta taho, suka shiga keken, ya wuce dasu.
Shi kuma yaya Faeeq, takaici ya kama shi, bai yi zaton zata samu abun hawa ba, gashi shi yaso ko in zata wuce, ta bar mai Nafisa. Kowa na ganin kaman Olamide ya ke so, but in real sense Nafisa yake so. Me shi zaiyi da yar yarbawa, su da akace suna da masifa, ga fada. Ai gashi ma ajikin Olamide, yarinya sai shegen tsiwa. Allah ya tsare shi, yaje ya aure ta, duk randa yan'borin ta suka tashi, tasa shorts, suyi fada. Gwanda ma Nafisa.
Suna sauka a bakin gate, Olamide ta ciro kudi ta ba shi, sannan suka shiga ciki. Suna shiga, Allah yayi akwai wuta, sai suka kunna fanka, kowanan su ta cire hijabin ta, ta ninke, ta cire bag, suka yi hanging din shi, suka sa takalman su a mazaunin su. Sannan Olamide tayi plugging din ruwa acikin kettle.
Tunda suka shigo, ba wanda ta ce ma wata kala, kowannan su nata harkan gaban sa. Ita dai Nafisa, bata son ta fadi abun da zai bata ma Olamide rai ne, ita kuma madam, sai huci take, tana regretting din zuwan su gidan su Nabila. Ita bawai ta sake masa ne ba, amma ita gaskiya ba zata bari yana zagin ta tayi shuru ba, lokacin da suke 100l, ta na dan jin kunyar sa, bata maida mai magana. Amma yanzu kam she can't take it. Mutumin da ba akan ta zagin ya tsaya ba, ya zage ta, ya zagi yaran ta, kuma abun da bai sani ba is that she is very proud of her tribe, duk da dai bata san garin su ba, amma she is still proud. Kuma ai Allah ya halice mu, yanda Ya halici baki, haka ma fari, ya halice mu in different nations, state, colours, tribes e.t.c, why not mu dauki juna as one, we are all Allah's creation. Amma wasu kam baza su iya ba. Inba racism be, toh tribalism, kuma yana everywhere. In yana ma wasu, suna barin shi, toh ita baza ta bar shi ba. Tana cikin tunani, wayar ta ya fara ringing. Data duba, taga sunan daya fito kan screen, tayi murmushi, ta daga. "Assalamu alaikum Ummi".
"Waalaikumus salaam ya'a. Kun isa gida lafiya"? Hajiya Hajara ta tambaya.
"Lafiya kalau Ummi". Ta amsa.
"Toh Masha Allah. Ina Nafisa"? Hajiya Hajara ta tambaya.
"Gata". Olamide ta fada, ta mika ma Nafisa wayar. Suka gaisa da Nafisa, kafun ta sa masu albarka, suma suka mata godiya, sannan suka kashe wayar.
"Habibty danAllah kiyi hakuri ki daina fushi please".
"Ba fushi nake ba. Kawai dai Ina regretting ne. Da ban san Nabila ba, da bazan hadu da tribalist dinnan ba. I hate his character wallahi. He should even thank his stars, ya girme ni, inba haka ba, daya fi haka shan maganganu a waje na, dana masa tas wallahi" Olamide ta fada.
"Kiyi hakuri kawai, ki dubi relationship din mu da Nabila, ki yafe mai".
"Daman ai saboda Nabila nake ragan masa, inba haka ba, dana dinga bashi amsoshin da zai kasa sa kan sa a pillow". Olamide ta fada.
"Ko ni, bana jin dadin yanda yake maki". Nafisa ta fada.
Suna cikin magana, kettle din ruwan da Mide tayi plugging, ya masu signal. Da sauri Mide ta kashe, ta zuba cikin bokiti, ta kara cika shi da ruwa, ta yi plugging.
Ta dauki bokitin ruwan zafi, ta wuce toilet, tayi wanka, sannan ta fito. Tana fita, Nafisa ta shiga, itama.
```BAYAN SATI DAYA```
Su Olamide kawayan amarya, sai shiri suke, sun dau anko har sun kai dinki, sun raba invitation, sunata shiri, don next week Saturday kam In Sha Allahu Nabila zata zama amarya.
Kuma duk zuwan da suke gidan su Nabila, Olamide bata haduwa da Faeeq, hankalin ta ya kwanta sosai, ta sake sosai a gidan, duk Familyn su Nabila da suka zo, su Olamide sun shiga masu rai, especially Olamide. Wasu macewa suke wai karya take ba bayarbiya bace, wai bata da halin su, kuma bata kama da su. Amma ai kun san ta da baki, ta ce masu wato kowani yare nada kaman sa kenan, kuma ko wani yare na da halin sa, ai ita bata taba sani ba, abun data sani shi ne, Allah ya halince mu duka.
Hajiya Hajara ko sai nuna ta ma kowa take, wai yar ta ce, although ba ita ta haife ta ba, amma yar'ta ce, ita ce yayar Safina.
```WEEK DIN BIKI```
Kawayan amarya ansha lalle, itama amarya, ta sha gyare gyare, Hajiya Hajara da yan'uwan ta, sun gyara ta spiritually, physically, ta mentally, sai kyali ta ke, black skin din ta yayi kyau sosai, Nabila ta dawo kaman ba ita ba, tabi tayi kyau sosai.
Yau Friday, za'ayi kamu, yan matan amarya, sun sha makeup kala kala, da wanda nata yayi fitting din ta, da wanda nata baiyi fitting din ta ba. Nafisa ma ba'a barta a back ba, makeup artist da aka dauka, ta rangada mata makeup itama, tayi kyau sosai, inba kasan ta ba, baza ka gane ta ba. Olamide kuwa anyi anyi da ita a mata makeup, taki, wai su foundations, din da za'a sa mata, zai sa zafi ya kama ta, kuma ita baza ta iya juriyan safi ba. So powder, da wani nude colour lipstick ta sa. Itama tayi kyau daidai gwargwado. Sai shiri ake za'a kamu by 4:00pm.
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
A matsayin sa na aminin ango, tare suke zurga zurgan biki, suje nan suje can. Gidan da za'a sa amarya ma, sanda suka ga gidan was looking it best.
Abdallah ya kai makulli, lokacin da aka zo jere.
In suna tare da Farouk, ya ita tsokanan sa, sai kuma ya shiga land of dreams din sa, ace shi ne ma zai yi auran, daya ji dadi, sosai.
Ranan Friday da safe, suka tafi kano, da shi da ango, da sauran abokanan su. Suka sauka awani hotel, kafun lokaci yayi, su tafi venue din da za'ayi kamun.
Bayan asr, suma suka fara shiri, dakin ya dauka da kamshin turaren maza kala kala. Sunyi kyau sosai, abunka da fararen maza, amma still cikin su, ba'a rasa bakaken ba, suma sun sha kyau sosai.
Basu bar hotel din ba, sai 4 dot, suka kama hanya, suka je venue din event, nan suka samu, wasu kawayan sun zo, amarya da main girls din ta basu zo bako, amma within 5mins, suma suka iso. Suna isa, Nafisa ta fara fita daga cikin motan, tana wani kyali. Abdallah, ya kallie Farouk, ya ce "Guy baka fada mun amarya nada extraordinary beautiful friends haka ba. Just take a look at this one, although dai tayi makeup, kuma kasan I don't go for madeup girls". Yana cikin magan Olamide ta zura kafafun ta ahankali, ta fito. Ai anan bakin shi yayi full stop, yama kasa cewa komai, sanda Farouk yayi taping din shi sau uku, kafun ya ce " subhanallah, which of the favors of your lord would you deny".
*_🔱((Home of Expert and Talented writers, da tambarinmu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'umah))_*
*T.W.A*
*WRITTEN BY ZAYNAB* _(zeexee)_
MARUBUCIYAR
*-RAYUWAR HUSNA*
*-MAHAKURCI MAWADACI (2020)*
```Dedicating this page, to my Moza(Xulley sparks)🤭🤭🤭 and my abokiyar fada🤭🤭💃🏽💃🏽💃🏽. I love you guys overdose🤭🤭🤭🤭.```
1️⃣3️⃣&1️⃣4️⃣
"Which of the favors of your lord would you deny". Abdallah ya fada.
"Non ya akhi". Farouq ya fada.
"I can wait to see my Bila wallahi". Farouq ya kara magana.
"Ni kam I have seen my qalbi, amma ya rage yanda zata zama nawa, don kasan heart dita ce, dole na samu yanda zan daidaita ta". Abdallah ya fada yana rubbing din palms din sa.
"Gaskiya ne, daga ganin yarinya har ka fara maganganu"? Farouq ya tambaya.
"Dole na fara, saboda Allah's creation is sooo beautiful, full of beautiful features. Just take a look at her, batayi wani makeup ba kaman sauran, amma tafi su. Kaga daa bahaushiya nake nama, amma Allah ya kawo mun bafulata a sawwake". Abdallah ya fada.
"Toh Mallam ka dauke ido, only first look is halal. Gaskiya kam, kana da over assurance. Amma idan bai yuwu ba, sai mu fada ma Bila, sai ta taimaka ma rayuwar ka. Kuma to be sincerely speaking, ban taba ganin kana ma mace haka ba, but just looking at her made you this way, what if ta yarda, maybe you will loose a knot". Farouq ya fada.
"Ai naga haka kaima kayi loosing din knot, kaga dole in bi sahu". Abdallah ya fada da wasa.
Olamide ko, data fito daga cikin motan, ta gyara tsuwar ta, Nabila ta fito. Kai sunyi kyau sosai. Daman ankon Olamide da Nafisa, daban ne dana sauran kawayen, kuma style din su daya.
Da Nabila ta fito, Olamide ta ce dan gombe bai iso bane"?
"Ke baki gani ne, ga dan gombe can da wani handsome kusa da shi". Nafisa ta Fada.
Su Abdallah na ganin fitowan Nabila, suka kara sa inda suke. Duk yanmatan da suka wuce, kallon su kawai suke, amma ina ango da abokin ango, anyi nisa.
Nafisa na ganin suna zuwa direction din su, tace "subhanallah, Bilatu, wannan shi ne wanda kika fada mana ko"?
"Ae shi ne, harkin fada a tarkon sa ne"? Nabila ta tambaya.
"A'a, ya mun haske da yawa. Nikam na bayan nan, daya ke bayan angon ki directly, ya shiga mun rai, ala dashi za'ayi wuf". Nafisa ta fada tana dariya.
"Ohhh Asim! Ai shima Doc ne. Yawancin abokan yaya na, Doc ne". Nabila ta fada.
"Habibty, yana ga kin yi shuru ne, ba zaki tofa naki ba"? Nafisa ta tambayi Olamide.
"Toh me zance, duk basu mun ba. Bana imagination akan abun da nasan da kyar ya zama gaskiya. Ai suna jin koni wata yare ce, zasu fara nuna mun tribalism, kuma kunsan bana taking shit. So in other to avoid that, gwanda na auri bayarbe ko dan Suleja, hankali na kwance". Olamide ta fada.
Nafisa na son ta yi magana kenan, su Abdallah suka iso.
Da suka jeru, Olamide da Abdallah suka kasance side by side, Nafisa taso ace ita da Asim suna side by side, unfortunately, yana bayan wanda ke side din ta, kaman tace masa suyi exchange da Asim.
Da kowa ya samu wuri ya zauna, kawayan amarya suka zauna kusa da ita, akan stage. Ai ko Abdallah ya ita satan kallon mide, tun bata sani ba, har suka zo suna ido 4 har sau uku. Na hudu kuma, Mide ta harare shi, ta murguda mai baki, amma ko ajikin shi, instead ya ragu, sai kallon ya karu. She was feeling soo uncomfortable, sai tace ma Nafisa "Habibty, inaga zan tashi anan in koma inda jama'a suke, am feeling uncomfortable". Olamide ta fada tana daure fuska.
"Kai habibty, haka bai dace ba, kinga mune manyan kawaye, ya kamata mu tsaya da ita, wallahi zata ji wani iri inta gan ki a can". Nafisa ta fada.
"Ni kadai nasan abun dake damuna, amma I will be patient. But if I keep feeling this way, gaskiya zan bar wajan nan" Olamide ta fada fuska a daure.
"Ae, ki bari, zan maki coverup a lokacin, but for now ki zauna please".
"Shikenan" Olamide ta amsa.
Bayan some mins, aka fito rawa, Olamide tayi gum kaman bata wajan. Amma Nafisa kuwa ana can Ana cashewa.
Abdallah ma yaki shiga wajan rawa, ya zauna kan kujeran sa kaman wani boss, yana ta dubawa ko zai ganta cikin masu rawa, amma yaga bata wajan, sai yaga Fisa ana cashewa. "Hmm, yarinyar nan akwai busy body. Although nasan na yaba mata, amma bata da natsuwa. Amma ga qalbi na, bata shigo cikin wannan hayaniyan ba, qalbi na natsasiya ce.
Da Olamide ta gaji da kallon masu rawa, ta tashi zata bar gurun, wayan ta yayi ringing, tana duba wanda ya kira, taga Hakeem. Ciki jin dadi da walwala, ta daga, sannan ta fita daga hall din, saboda kara yayi yawa.
Abdallah na juya kan sa, ya gan ta zata fita, ya tashi cikin natsuwa, ya biye mata baya, nan yaji tana waya. Ya aza ko saurayin ta ne take waya da, har heartbreak ya fara kama shi, sanda yaji tana cewa zata dake shi inta dawo, shi yasan bayanda zata ce zata daki saurayin ta. Hakalin sa bai gama kwaciya ba, sai lokacin da yaji tana kiran Fa'iza da autan Mummy, sannan hankalin sa ya kwanta. Yana ta ears dropping, har ta gama waya. Yana jiran yaga ta juya ta shiga hall, sai yaga ta nemi kujera, ta zauna. "Wato qalbi bata son damuwa da hayaniya kaman ni, hmm maybe in mata magana yanzu, because banda time kuma, gobe daurin aure, kuma ana gamawa, zamu kama hanyan Gombe, gwanda kawai na fada mata yanzu".
Sanda yayi addu'a ya tofa ma kan sa, dan according to him, this is a life changing matter.
Da Olamide ta gama waya, ta ce bari ta zauna kafun masu rawa su gama rawan su, sai ta koma. Sai ta nemi wuri ta zauna, ta kunna data, tana WhatsApp. Tana cikin chatting din ta, taji ana mata sallama.
Daya gama addu'a, ya tofa, ya kara cewa "ya Allah, kaga niyya ta akan ta, I don't mind getting married to her in the next two to three months, but Allah you know best, if she is going to be good for me, ya Allah kasa ta yarda dani, in kuma she will not be good for me, ya rab kasa karma ta saurare ni".
Da bismillah, ya fara takawa har inda take, yaga duk hankalin ta na kan wayar hannun ta, sai yayi sallama. A hankali ta dago kai, ta amsa mai.
Olamide na ganin shi ne mai kallon ta a hall, ta fada a zuciyar ta, tace "ai kuwa sai ka fada mun dalilin daya sa ka kure ni da ido, sai kuma na maka lectures, saboda Islamically, only first look is halal, we are meant to lower our gaze, both male an female".
Tana cikin tunani, taji yace "ina iya zama akan wannan kujeran"?
"Ka zauna ma, tunda dai baa kai na zaka zauna ba". Ta fada tana wani bata rai". Tana fadan haka, ta maida hankalin ta kan wayar ta.
"Dan Allah ki dan bani attention din ki, magana mai mahinmanci zan miki". Abdallah ya fada.
"Toh ina sauraran ka". Olamide ta fada,