baza'a fadawa kowa ba, mts."
Taja tsaki snn ta kuma cewa "Yauwa yaushe kuma kika taba jin na cewa mutumin nan gentle."
"Wani mutumi?" ta tambaya tamkar bata fahimci abinda take nufi ba.
"Mutumin da kika min sharri dazu a wajenshi, yaushe na ce shi gentle ne."
"Haba, aunty Salma , da bakinki a cikin d'akin nan kika ce mishi gentle with innocent face?"
"Mtss wancan lokaci ,ina miki bayani ne dan ki fahimci abinda yayi bai kamata ba, baki abin magana.
Kamar tana jira tace "tsuliya abin kashi."
Qwafa salma tayi tana cewa "Ba laifinki bane nusai."
"Banda abinki aunty salma ai kunfi dacewa da wnn dinma."
Wani wawan zabura tayi saida ta tsorata nusaiba.
"Da wa din muka fi dacewa?Amma mutuncinki ragagge ne nusaiba. Ahmad din zakiyiwa haka?
Allah ya kawoshi lafiya, dole yasan matsayinshi a gunki. Wlh kin ban mamaki."
Tsakaninta da Allah ranta a b'ace take maganar.
Kusa da kofa nusaiba ta koma snn tace "Tsakani da Allah to meye laifina dan na fad'i ra'ayina, mutumin da ya so ka ya so abinda kakeso ai shine abin so. Bayan haka ma duk wanda yasan dacewa, yaganki yaga gentle yasan kunfi dacewa, ki duba fa skin colour naku ma iri d'aya, shi kuwa ahmad wani fari fauu dashi, idan kuka had'u saiyayi fauu, ki kuma kiyi wata disshhh dake."
ta karishe da dariyar rainin hankali.
"Naji nusaiba, yanzu nasan irin zaman da zanyi da ke, snn da bakisan bamu dace ba sai yanzu kike ganin rashin dacewar, kisani duk wanda yaki ahmad ni yaki, na kuma gode da kiyayyar da kika nuna min,
"Allah ya baki haquri ,niba nufina kenan ba."
Daga nusaiba ta fad'i haka dukansu sukayi shiru.
Saida suka gabatar da sallar ish'ai snn suka bar d'akin, ba mai kula dan uwansa, Fati ko zuba musu ido tayi dan ita bata ma san wanda ake maganar a kanshi ba.
Ko da ahmad yazo, kamo hanun fati salma tayi suka fita tare, nusaiba na kallonsu tana ta dariya qasa qasa.
Saida suka fita tayiwa su ummi tad'in daramar da sukayi da salma snn tace bari taje taga ya salma zatayi.
Tana zuwa wajensu ta washe baki , "Lucky sannu da zuwa , "
"Yawwa kanwarmu da fatar na sameku lafiya."
"Lafiya lau ya Madam."
Ta fad'a tana satar kallon salma."
Shima saida ya saci kallonnata snn yace "tana lafiya."
Salma dai sai zabgawa nusaiba harara takeyi, itako sai janshi da hira takeyi ,harda cewa Allah ya bar mana luckynmu.
"Munafuka."salma tace qasa qasa.
"Aunty kince wani abu ne?"
hararan ta kuma galla mata snn ta d'auke kai.
"Nifa yau ban ganewa aunty salman nan ba.
Cewar ahmad yana maida dubanshi ga salma.
"Ai yaufa bazaka gane mata ba da..."
"Ke nusaiba bar nan."salma ta fada tana muzurai, sbd tsoron kada nusaiba ta fadi wani yazo wajenta , gashi yanzu ma duk a tsarge take.
Dariya nusaiba tayi ta k'ara gaba, tana cewa "lucky, na tafi tunda an koreni."
Ita dai salma jinta takeyi wata iri tamkar ta aikata sab'o haka takeji, duk lokacin da A M G ya fad'o mata sai taji tsinkewar zuciya.
Allah alla take ta shiga gurin al-amin da ya shiga gida yanzu dan tana so suyi magana.
Suna shiga gida ta cewa Fati wuce ciki ni zan shiga gun yayanmu.
Yana jin ta kusa isowa kofarshi yayi saurin kashe wutan d'akin dan ya santa da tsoron duhu.
Tsayawa tayi tana kallon kofar d'akin tana tambayar kanta ta shiga ko kuma ta bari sai da safe.
"Kai ina bazan iya ba yau za'a yita ta qare."
Tace a ranta.
Sau uku tana sallama ,shiru ba amsa, hakan yasa ta kutsa kanta cikin dakin duk da duhun dake ciki.
Lalub'e ta shigayi har ta gane makunnin wutan ta kunna, saiga al-amin kwance bisa katifa ya rufe ido tamkar mai bacci.
"yayanmu ka tashi magana zamuyi ,ni nasan ba bacci kake ba.
jin yayi shiru yasata isa bakin katifar ta duqa ta jijjiga shi da iya qarfinta saida taga ya bud'e ido snn takyale shi.
"Ke meye haka ."yace yana wani hade rai.
"magana zamuyi."
"shine kuma bazaki iya haqura sai gobe ba zaki tasheni a bacci."
"Tunda ka tashi ba sai muyi maganar ba."
Yau ya lura a salmanta take sbd haka ya dad'a hade fiska.
"yauwa, me yasa d'azu baki qarasa ninke min kayana ba? tunda kika shigo sai kizo ki karasa."
Kama kugunta tayi fiska a d'aure tace "Ka ninke kayanka da kanka, naga dai d'azu ninkewa mukeyi ni da nusaiba, ka kirata ka turo min wani k'ato."
Waro idanunshi yayi "waye k'aton salma?"
"Ogan nawa kike cewa k'ato, haba ummulu aiko albarkaci na ya kamata yaci ki mutunta shi."
Kamar zatayi kuka tace "Yayanmu me yasa kake min haka ne, kasan ahmad nakeso kuma shi zan aura, danme zaka hadani da wani? Yaudararshi kakeso nayi, ko ahmad din kakeso na yaudara.?"
"Ko d'aya ni bance ki yaudari kowa ba, amma ina laifin maisonka, ahmad din wani yunkuri yayi game da maganar aurenku? Tun yaushe kika qare karatun in har da gaske yake."
Katse shi tayi da cewa "Wlh da gaske yakeyi, naga wancan karon ba tare da sanina bama ya turo, da na nuna mishi rashin amincewata ne ya dakata, kuma yace sai na yi mishi izini zai sake turowa."
"mtss, to me ya hanaki yi mishi izinin, ko kina tunanin haka za'a yi ta zuba miki ido ga kanwarki zata yi aure ke kuma kina jiran tsammani."
"Yayanmu, kasan ni ahmad nakeso, ka kuma san ra'ayina bana son auren mai kud'i kuma bana son mai mata."
Dariyar takaici al-amin yayi wato bakya son mai mata, shi kuma ahmad d'in 'yar tsana ya ajiye a gidanshi kenan, ko kuma shi d'in ba mai kud'in bane.?"
Wani marairaicewa ta dad'a yi, "Ahmad nefa, shi kasan ko yaya nema ina sonshi."
"Kije ki had'iye shi qarewar so Ummu salma."
Ya fad'a kufule.
"Dakata ma wa yace miki ogana yana da mata? Shi ya fad'a miki yana da mata?
Shiru tayi ta kasa bashi amsa dan itama tasan fad'a kawai tayi.
"Fita salma sai da safe tunda bakisan mai sonki ba."
Juyawa tayi zata fita ranta a b'ace, ya tsai da ita, "Kuma ki sani kafin ya fara zuwa wajenki saida ya nemi izini Wajen malam, kuma yayi na'am dashi, danshi ba wasa ya zoyi ba da gaske yakeyi."
Cikin takaici tabar d'akin a ranta take cewa "to wa yazo wasan?"gaba d'aya haushinsu takeji, daga al-amin, oganshi harma da Nusaiba.
Bai sake zuwa ba har akayi bikin nusaiba aka gama, sai tayi tunanin ko al-amin ya fad'a mishi yanda sukayi ne ya haqura.
Bayan biki taje ta samu Mal. tace mishi zata bi pendonta kaduna, bai hana ta ba ya bata izinin tafiya, sbd haka ta fara shirye shiryen tafiya.
Al-amin kuma yanzu sun koma normal ta daina jin haushinsa.
Ranar da zasu tafi da sassafe al-amin yace su fito zai kaisu tasha.
Sallama suka yiwa kowa,su Hamza suka fitar musu da kayakinsu.
Har sun kai bakin kofa salma ta koma da gudu tana cewa "Bamuyi sallama da auta ba."
D'akinsu Hamza ta shiga ta samu khalil yana bacci.
Tashinshi tayi ya tashi yana murza idanu "aunty yanzu zaku tafi?"
"Eh, yanzu ne, kayi sallah kuwa?"
"nayi da muka dawo daga masallaci ne na kwanta."
Kanshi ta shafa "to na tafi kayi mana addu'a ."
"Allah ya kareku da kariyarsa,Allah ya kaiku lafiya."
"me zan siyo maka."
"Ball da canvas zaki saya min ."
"to khalilu na sai na dawo."
Da sauri ta fice ya bita a baya yana mata bye bye.
Motar ranar da ta gani wanda al-amin yazo dashi.
Tana isa aka bude mata gaba ta shiga da Bismillah, snn ta rufe kofar.
Kamshin da taji ne yasata d'agowa da qarfi....
*Ummu D'alhat ga naki*ππΉ
[17/12 06:25] Hajara: *ππIN SO CUTANEππ*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W.*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
33.
ππππππ
*Dedicated to adda Ummulu (Ummu salma Ahmad Adam) a.k. a Dr U.S.A.*
Wanda ta gani a driver seat yayi matuqar razanata, kallonshi take da mad'aukakin mamaki.
A .M .G.
Ta d'au lokaci tana kallonshi snn ta waiga ta kalli bayanta , wayam ba kowa.
To ina suke.
Kallonshi tasakeyi sukayi 4 eyes, take tayi qasa da kanta.
"Ina kwana Ummu."
Wani kunya taji ya rufeta, cikin sanyin murya tace "Ina kwana."
"Lafiya lau, ya hidimar biki?"
"Alhamdulillah."
Daga nan sukayi shiru, yaja motar sai tasha.tana ta saqe saqe a ranta ,dama wnn bawan Allah ba haqura yayi ba liqimo yayi kenan.
Saida suka isa ta hango al-amin yana jingine da wata mota.
To ina pendon kuma ?
Tace a ranta.
Qarar wayarta taji daga cikin handbag dinta, shi ya katse mata tunaninta.
Wani lafiyayayen murmushi ta saki lokacin da ta fito da wayar, ganin ahmad ne yake kiranta.
Bayan sun gaisa yake ce mata gashi a kofar gidansu, yazo su sake yin Sallama duk da dai jiya sunyi yana so ya kuma ganinta kafin tafi, yasan ko yaya zaiyi bazata tab'a yarda ta shiga motarshi ba, dan tunda suke tare bata tab'a yarda ya kaita wani waje da motarshi ba.
Wani irin tausasa murya tayi tace, "Ayya ahmad mun riga mun wuce."
"Ya kika mun haka salma, naso na qara ganinki kafin ki tafi."
"Nima naso hakan wlh."
Da sauri ya katse ta da "zanzo yanzu kafin ku tashi."
"A'ah, mun kusa tashi, ko kazo ma nasan bazaka samemu ba." itadai tsoronta kada yazo yaga wnn d'an anacen ranshi ya b'aci.
Shiru ya d'anyi snn yace "Zanyi kewarki salma ba kad'an ba."
"nima haka ahmad."
"Ki kula min da kanki, dan Allah banda fita kada samarin kaduna su gane minke su kyasa."
"Ina ,wane su salma ta Ahmad ce shi kad'ai In sha Allah."
"Allah ya yarda, salmata, Allah ya kaiku lafiya, ya tsaremin ke ,zan kira anjima."
"amin na gode sai na jika."
Daga nan ya kashe wayar.
Tunda ta fara magana a waya ya yi baya tare da kwantar da kanshi kan seat, ya lumshe idanunshi.
Har saida ta gama ya bud'esu, snn ya taso.
Tana kokarin maida wayar cikin jakarta ya sa hanu a hankali ya zare wayar.
D'an kalloshi tayi taga hankalinshi na ga wayar, ta tab'e baki tare da kawar da kanta.
Bude kofar take famanyi ta jishi a kulle , hakan yasa ta kuma kalloshi.
"Baki da kirki Ummu."
Yace ba tare da ya kalleta ba.
"fiye da sati baki ganni ba bakiji daga gareni ba amma sam baki nemi sanin halin da nake ciki ba."
Shima kanshi yasan ya fada ne kawai dan neman magana amma yasan bazata nemeshi ba koda shekara tayi bata ganshi ko ji daga gareshi ba.
A nata bangaren kallon mamaki take mishi dan duk a tunaninta ta d'auka zaiyi korafin wayar da tayi da ahmad a gabanshi zaiyi, amma ga mamakinta sai ya dauko wata maganar daban.
Taso ya kawo mata maganar ahmad ko dan ta tabbatar mishi ahmad takeso kuma shi zata aura amma sai taji akasin haka."
"Ummu na shiga wani qauye ne duba wani aiki, qauyen basu da service, shi yasa baki jini ba, amma baki tab'a barin zuciyata ba koda na second d'aya ne.
Da badon Allah yasa na dawo jiya ba saidai na dawo naji kinyi nesa dani, kin tafi ba ko sallama."
Ya dan sauqe ajiyar zuciya.
"Ko da yake dan in biki kaduna ba wani abu mai wuya bane, ai hausawa sunce garin masoyi baya nisa."
Duk surutan da yakeyi salma waje take kallo sam bata yarda ta sake kallonshi ba, ita dai ya cikata da haushi tunda bai fadi abinda ta keso taji ya fada ba.
"Ummu, ummu, ummu."ya jera kiran sunanta, jin bata amsa ba yasa yaci gaba da kiran sunanta.
"ya fara halinnashi na naci d'an anace kawai, sai yayi ta jera sunan mutum a bakinshi ko gajiya bayayayi."tace a ranta.
"Ummu salma." Sai a snn ta kalleshi amma bata amsa ba.
Kurawa juna ido sukayi na dan lokaci, daga bisani ta janye nata.
"Nagode."
Taji ya ce.
Kallonshi ta kumayi da mamakin godiyar da yakeyi.
"Nagode ,dama kwayar idanki nakeson gani dan su zame min abin tunawa a ko da yaushe.
Ta iya yiyuwa ma kallon karshe kikayi min Allah masani."
Da sauri ta kalleshi dan maganar ta dan tsoratata sbd a sanyaye yayi ta.
Suna hada ido ya daga mata gira tare da kashe mata ido, hakan yasa tayi saurin kawar da nata."
Murmushi mai sauti yayi tare da cewa "Ummun Abdul in sha Allah."
"Wannan rana tana cikin ranaku masu muhimmanci a gareni , zaiyi wuya na mance da ita."
Hanunta ta miqa mishi alamar ya bata wayarta.
Tamkar bai ganta ba yaci gaba da danne danne a wayar.
So take ta masifeshi amma bakinta ya mata nauyi.
Haka kawai taga ya mata kwarjini, ya kuma cika mata ido.
"Ummu tsarabar me zaki kawo min?"
Kamar an sata dole tace "Duk abinda kakeso."
Kura mata ido yayi yana murmushi mai qayartarwa , ya ce "duk abinda nakeso kikace?"
Shiru tayi bata amsa ba.
"Ummu tsarabar zuciyarki nakeso ki dawo min da ita, zan samu?"
Ya qarishe maganarshi da cikin wata kasalalliyar murya.
Wani abu taji yana mata yawo ajiki wanda ya tilasta mata takure jikinta waje guda ta kuma rintse idanunta.
Kallonta yayi na dan lokaci kafin ya maida hankalinshi kan wayarta, ya budeta ya cire sim cards dinta ya kuma bude tashi wayar ya musu musanyen simcards snn ya miqa mata tashi wayar .
Saida yace mata "ga wayarki ."snn ta bude idanunta .
Kallon wayar tayi snn tace "waya ta zaka bani."
"itace ai."
Ya fadi ya kuma mika mata wayar.
Ganin taki karb'a yasa hannu ya dauki handbag dinta dake kan cinyarta ya saka wayar ciki.
Jakar tana hanunshi ya bude motar ya fita ,ya zaga ta gefenta ya bud'e mata.
Lokacin da suka fita an fara kiran sunan masu tafiya ,sbd haka ta matsa gurin da taga su ya al-amin, shiko yana biye da ita a baya.
Tana isa al-amin ya washe baki, "Ummuluna kamar mu tafi tare."
Saida ta matso kusa dashi sosae snn a shagwab'e tace "Shine kuka tafi kuka barni ni kad'ai yayanmu."
"Ah, haba dai, yanzu ke kad'ai kika zo?"
Ya fad'a yana waro ido kamar gaske.
"Yayanmu ka qware wajen iya manna wa mutum hauka."
"Me nayi ?to da wa kikazo?"
"Oho, ni ban sanshi ba."
Duk abinda sukeyi pendonsu da A M G suna kallonsu saidai basajin abinda suke cewa, sosae suka burge su dan da ganin yadda take mishi shagwaba kasan akwai shaquwa mai karfi tsakaninsu.
Ita pendonsu tuna mata da yaranta na farin da ta biyun sukayi , haka suke ,basa rabuwa suyi fada su shirya.
Har aka kirasu suna tsaye sai tsokanarta al-amin yakeyi.
Pendo ce ta fara shiga snn ita kuma tazo zata shiga.
"Ki kula kar ki zauna kusa da ko wani qato." taji shi daga bayanta.
Kalloshi tayi kad'an ta kawar da kanta , a zuciyarta tace "Gaka k'ato kake cewa wani kato."
Har ta shiga yana tsaye a gun , saida ta je ta zauna can ta jikin window, seat nasu daya da pendonta, al-amin ne ya zo ya tsaya ta wajen , "Allah ya kiyaye hanya ummulu."
Hanunta ta mika mishi shima ya miko mata suka yi shaking tace "Kamar in fasa yayanmu, wlh zanyi kewarku fiye da tsammaninka, Alla sarki fati na,daga yanzu na fara kewarta."
"Daga baya kenan, saida kika daidaita cikin kujerar mota zaki wani ce min kamar ki fasa, kice dai zakiyi kewar ogana kawai."
Ya karishe da sigar zolaya.
"Hmmm, kace ya bani hand bag dina, indai ba gado na zaiyi tun ban mutu ba."
Dariya al-amin yayi ya zare hanunshi snn yace "wnn tsakaninku ne ,ni na isa na shiga inji kunya?.
Allah ya kaiku lafiya, pendo Allah ya kiyaye hanya."
Ya maida akalar maganarshi gurin pendonsu.
Barin wajen yayi yana jin ba dad'i.
Saida motarsu tazo tashi snn ya leko ya ajiye mata jakar kan kan cinyarta tare da wata leda mai 'yar girma yana cewa "safe journey dear."a hankali kamar mai rad'a.
Snn ya sallami pendo.
Suna tsaye a gun har motarsu ta tashi.
(safe journey salman ahmad.)π
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng