x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 7 - IN SO CUTANE

  • 18001 words
  • 21000 words
  • Out of 26921 words

Category: Tale Stories

Views 73

09 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
kenan.
*** *** ***
Sati biyu da dawowar salis aka sa lokacin bikinsu.
Shirye shirye suka shigayi , tare da salma da pendonsu kanwar mamansu,sai fati, suka shiga kasuwa sukayi wa nusaiba sayayyan kayan kitchen masu kyau, dadai k'arfinsu.
Tun ana saura wata guda biki pendonsu da take kaduna ta iso ,nan ta fara gyara amarya yadda ya kamata.
Cikin kwanakin kuma Salma ta k'are karatunta bayan taci wuya ,har rama tayi.
Farin cikin ta ya gaza b'oyuwa, ba ma ita kad'ai hatta malam da ummi da sauran 'yan uwanta sunyi farin cikin kamalla karatun nan nata ,sai da fatan samun sakamako mai kyau.
Alk'awari ta d'aukarwa kanta ,duk lokacin da Allah ya sa ta k'are makarantar lafiya zata shirya walima , dan nuna tsan tsan farin cikinta da godiya ga Allah da ya bata ikon yin karatun.
Hakan ko a kayi ta fara shirye shiryen walimah ,tare taimakon ,malam, ummi, da al-amin.
Nusaiba taso ta haqura su had'a walimar da na bikinta ,tace sam, bazaiyiyu ba, walimarta daban na bikin nusaiba daban.
*Gaisuwata gareku.*
*Rakiya yakubu.*
&
*Habiba Muhammad.*
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
'
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
24.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
*Ina kike uwa ma bada mama, wnn shafin naki ne, uwa hana kukan talauci, uwarmu abar alfaharinmu, HAJIYA FA'IZA ALIYU BASHIR (Aunty)*
*Allah ya bada tsawon rai mai amfani.*
*Ina alfahari dake mamana.*
Yau suka tashi da shirye shiryen walima , gida ya cika da dangin Malam da na ummi, duk sunzo taya Salma murnar k'are karatunta.
Yadda aka tsara da yamma za'ayi walimar .
Wanka ta fito tana gyara fiskarta bayan ta gama shafa mai.
Fati ko tana fitar mata da sabon kayan da al-amin ya d'inka mata na fitar walima.
Nusaiba ce ta shigo tana mika mata wayarta da take ringing .
"Wayene?"
Ta tambaya tana kallonta.
Mik'a mata wayar tayi tana mita k'asa k'asa "Kullum mutum ya bata waya sai tambaya wayene, tamkar bata san sarkin nacin ne yake kiranta ba."
Bata kulata ba ta karb'a ta kara a kunnenta ita kuma ta juya ta tafi.
"Assalamu alaikum, Ahmad an wuni lfy?"
"Wa alaikumussalam, amma bazan amsa gaisuwar ba."
"Me ya faru."
"Tambayata ma kike me ya faru? Salma yanzu kina ganin kin kyauta kenan?"
"Me nayi ahmad?"
"Ina ko zaki san abinda kikayi tunda yanzu bani da wani matsayi a gunki, fii sabiilillahi a ce zakiyi walima na qare makarantar ki baki sanar min ba , me kike nufi?"
Jimm tayi ta ma rasa abinda zata ce dashi.
"Dole ki rasa ta cewa tunda kinsan baki da gaskiya."
"To ahmad me zan ce maka, naga walimar na mata ne , ko zaka turo amarya ta taya ni murna ne?"
'Yar karamar tsaki yaja ,a kufule kuma yace ,"Idan na mata ne kuma bani da matsayin da za'a sanar dani kenan, da ba don na k'ira nusaiba ta d'auka ba har ayi a gama ban sani ba dan ban kai matsayin ba ko?"
"Allah ya baka haquri ni ba haka nake nufi ba."
"To yayane in ba haka ba?"
Kamar zatayi kuka tace "Ni dai kayi haquri."
Katse wayar yayi yana maijin haushi abinda tayi mishi.
Wato taki sanar dashi ne dan kada ya ce zai d'auki nauyin wani abu.
Mttss yaja tsaki, yasan hakan halinta ne ,tunda suke da ita bata tab'a rokanshi abu ba , snn koshi ya bata ma sai yayi da gaske take karb'a ,wani lokacin sai ya bawa kannenta sukai mata.
Duk da hakan yana qara mata daraja a wajenshi amma yaji haushin abinda tayi mishi ba kad'an ba kuwa .
Saida ta gama shiri tayi d'as da ita kamar wata sabuwar amarya .
Ta cewa fati ta kirawo mata nusaiba.
Suna cikin magana nusaibar ta shigo , itama wankan ta yiyo .
Harara salma ta galla mata, ita ko ta d'auke kanta tamkar bata ganta ba.
"Nusaiba me yasa kika fad'awa ahmad maganar walimar nan?"
Kallonta takeyi baki sake, daga bisani tace "Wai kina nufin dama baki sanar dashi ba ?No wonder yake tambayar ya yaji hayaniya , ashe bai san da maganar ba , amma dai baki kyauta ba wlh."
Har ta d'auki mai zata shafa ta sake juyowa takalli salma "Ina fata ya nuna miki b'acin ranshi kuma kema ya b'ata miki naki ran, wlh nima kin ban haushi aunty, meye abin b'oyewa a gurin abin farin cikin? Wlh in nice shi zai fara sani."
"ke ya isheni haka masifaffiya, yarinya kamar an d'auko hayarki kimin lecture?"
"Allah ya baki haquri aunty, kinyi kyau fa kamar yau za'a kaiki gidan lucky."
Ta fad'a tana washe baki da son basar da zancen dan taga aunty nata har ra fara hawa.
Kafin ta yi magana suka jiyo sallamar friends na salma , suna shigowa suka had'a baki wajen fad'in "Wooww ,sister salma ,kinga yadda kika fito?"
Murmushi tayi tana mika musu hanu d'aya bayan d'aya suna shaking, snn suka zazzauna aka fara chapter.
"Allah ya nuna mana bikinki sister, wnn had'uwa haka ?"
Faleela ta fad'a , dukkansu cikin farin ciki suke ,kowa ta cab'a ado na gani na fad'a.
Wata cikinsu tace wlh nima nanda kwana biyu zakuzo nawa walimar, ina komawa zan fara shiri."
Kwashewa dauka sukayi da dariya "Ke da kika ce sai party, yaushe kika canza shawara?"
Cewar d'aya daga cikinsu.
"na fasa ,nima walimar zanyi ."
Fati ce ta shigo tana ce musu su fito an gama had'uwa su ake jira ,har malaman da zasuyi wa'azi sun iso.
Fitowa sukayi sai zuba k'amshi sukeyi.
Kanwar mamarsu ta kaduna ita tazo ta rike hanun salma tana cewa "Ma shaa Allah 'yata kinyi kyau."
Shadda ta saka zani da riga da d'ankwali purple colour yasha aiki , d'aurin steps tayi a kanta wanda ya dad'a fito da kyaun fiskarta sai gyalenta fari da ta yafa , takalminta silver colour sai purse da agogon hanunta , sarka da 'yan kunne ,abun hanu zobuna duka silver colour.
Simple make up tayi wa fiskarta ,daga powder, kajal sai janbaki colourn kayanta.
Canopies biyu aka kafa cikin gidan kasancewar akwai babban fili a gidan.
Sai da ta fara zuwa ta kwashi gaisuwa gun manyan malaman da aka gayyata domin gabatar da lecture.
*Hajiya Faiza Aliyu Bashir.*(Aunty)
*Hajiya Aishatu (Malama Tasalla.)*
*Malama Mamuji*
Sune manyan malaman da aka gayyata domin gabatar da wa'azi a wnn rana ta farin ciki ga k'awata Salma.
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal)*
25.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
*Wannan shafi kyauta ce gareku Qungiyar Khairul Umma, at large ban rage ko d'aya ba.*
*Allah ya biyaku.*
Wad'annan manyan mata masu daraja malamai ne daga qungiyar mata musulmai na Jalingo ,dake jahar Taraba .
*KHAIRUL UMMATI*
Qungiyace ta musamman wacce take bada muhimmiyar gudumawa ga musulunci da musulmai.
Aiki suke tukuru wajen ganin sun d'aukaka kalmar Allah, ba dare ba rana.
Suna sadauqar da lokacinsu, qarfinsu, da dukiyoyinsu wajen d'aukaka kalmar Allah.
Lunguna, saquna, qauyuka ,suke shiga dan yin da'awa.
Suna musuluntar da wad'anda ba musulmai cikin hikima, baseera, da ilmin da Allah ya hore musu.
Suna kuma d'aukan nauyin wanda ya musulunta 'yan uwa da dangi suka k'ishi sanadiyyar shiga addinin musulunci.
Karatu ,ci ,sha, sutura ,muhalli, wnn duk basa gazawa wajen d'aukewa masu buqata.
Ruwa da iska, zafi da sanyi , zafin rana, akwai da babu duk ba sa hana su tsayawa tsayin daka wajen ganin sun yiwa addini hidima.
Allah ka sakawa wad'annan bayi naka da alkhairi , ka biya musu buqatunsu na duniya da lahira, ka qara musu lfy, ka basu ikon cika qudurin su na alkhairi.
Ka kare su da kariyarka ,kama karesu daga sharrin dare da rana, mutum da aljan.
Ka kare su daga sharrin dukkan abin qi.
Ka kara d'aukakasu.
Ka basu ikon ida nufinsu na alkhairi.
*Ameen*
Malama Tasalla ita ta bud'e taro da addu'a tare da karatun alqur'ani mai girma.
Daga nan Hajiya Fa'iza ta fara gabatar da lecture akan muhimmancin ilimin 'ya mace.
Muhimmancin karatun likitanci ga 'ya mace a wnn zamani da muke ciki, wanda ma'aikatan asibitoci suke d'aukan ran musulmi ba a bakin komai ba , ake wulakanta musulmai, a tozarta su ,ana musu kallon banza da raini, ana ganinsu basu san komai ba, more especially mata masu ciki in anzo wajen haihuwa.
Tayi magana akan likitoci musulmai da suke biyewa colleagues nasu wad'anda ba musulmai ba wajen kin taimakawa da tausayawa ga 'yan uwansu musulmai.
Sai kaga an kawo mace mai nakuda ,tana fama, ace idan ba kud'i baza'a karb'e taba.
Ko da kud'in ma baza ta samu isasshen kulawa ba tunda musulmace kuma ba a ga maiko a tattare da ita ba.
Su kuma 'yan uwan namu musulman sai su nuna halin ko in kula ga lamari.
Shin tsoro ne ko kuma qangarewar zuciyace.
Wata ma kina gani musulmace 'yar uwarki, sai arne ko arniya ta tsaya kanta tana bata kalmar "JESUS."
Instead ke ki bata kalmar shahada.
Allah ya tsare.
Wani abin takaicin zaka ga mace tana fama ,wai dan ta d'auki lokaci bata haihu ba dan kar ta b'ata musu lokaci sai a nemi mijinta ko 'yan uwanta ace su sa hanu za'ayi mata tiyata bazata iya haihuwa da kanta ba, ke kuma 'yar uwa musulma kina gani kin yi shiru baza ki taimaka da baiwar da Allah ya baki ba.
Nasan ba duka aka taru aka zama d'aya ba ,amma masu taimakon basu da yawa.
*Sister Jamila Usman Nyaja (Mmn Al-Mustafa)* kina kokartawa, kina bawa mata kulawa ta musamman naji daga bakin mutane da dama .
Allah ya saka miki da mafificin alkhairi.
Nurses kuji tsoron Allah, ku tausayawa 'yan uwanku musulmai ,ku taimaka musu da iliminku, Lokacinku da kuma aljihunku inda hali.
Akwai lada mai tarin yawa cikin wnn aiki naku,.
Nan dai Hajiya Fa'iza ta rika kwad'aita musu lada da kuma falalar dake cikin wnn aikin.
Har Salma da sauran colleagues d'inta suna jin zasu iya bada kowace irin gudumawa ta fannin wnn karatu da sukayi.
Gaba d'aya sun kwad'aitu da falalar da ke cikin wnn aiki.
Karshe ta bawa iyaye shawara da k'arfafawa yaransu gwiwa dan su rika karanta science courses sbd mu samu wadatuwar likitoci musulmai.
Daga nan Malama Mamuji ta karb'i wa'azin inda ita kuma tayi fad'akarwar akan mata ma'aikatan gwamnati da suji tsoron Allah , su rik'e mutuncinsu da mutuncin aurensu.
Su kame kansu aduk inda suka tsinci kansu.
Su guji cin amanar Allah, da ta mazajensu.
Snn ta zayyano d'imbin azabar da tab'ewa da ke jiran duk mace mara tsoron Allah, mai cin amana , mai munafurci da annamimanci.
Wayyo Allah , kuzo kuga yanda guri yayi tsit, tsoron Allah ya Shiga zuqatan mahalarta wannan taro .
Kuzo kuga idanuna yadda nake zaro su ,ina bin aminai na da kallo, Maryam Mazad, Amina Sale Muri, Lubabatu kyauta, Salamatu Ibrahim Bawa, Ummul kulthum Aliyu Bashir, Nafisa D'ahiru,Hajara Aliyu, Sister Jamila, Sadiya sale, Jamila Mu'azu, Maryam Adamu lanko,Sadiya Ibrahim, ga kuma swt sister Halima Auwal, Ga Nafeesat (Mrs Bashir Bello.) Kai ,muna da yawa fa.
Sai zura gula gulan idanunsu sukeyi, anji maganar lahira.
Malama mamuji badai iya sa tsoro ba, idan tana wa'azi sai kaji kanka na juyawa, kwakwalwarka na amsa quwwa, tsigar jikinka na tashi, ka rika jin wani zuuuuuu irin kana gangarawa lahirannan.Lol.
Allah kasa mufi qarfin zuqatanmu.
Ana cikin wa'azi sai ganin almajirai akayi suna shigowa da kwalayen juices da snacks.
Mikewa salma tayi tana rarraba ido , can ta hango Nusaiba ,zaune tayi zugum jiki a sanyaye, alamar wa'azi ya shigeta.
Cikin sanyin jiki ta ...
Na gaji wlh☹
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal)*
26.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
*Wnn shafi kyautace gareki Hauwa .S. Zaria, nagode da qauna Allah ya bar zumunci.*🌹
Cikin sanyin jiki ta fara ratsa mutanen har ta isa wajen nusaiba ta kamo hanunta.
Saida suka fito sarari snn suka tsaya.
Lokacin nusaiba ta lura da kayan da ake shigowa dasu, ta tambayi salma daga ina.
Itama tace bata sani ba, dalilin da ya sata nemo ta kenan.
Kafin su qare maganarsu almajiran har sun gama sun fita.
Sbd haka nusaiba taja hanun Salma tana cewa "Zo muje mu duba."
Suna fita suka ga wucewar motar ahmad, sai almajirai a gefe da suke rabon kud'i.
"Ahmad ne wlh."
Salma tace tana nuna motar.
Kafin nusaiba tayi magana sai ga wata bak'ar mota mai tinted glass tazo ta parker kusa dasu, sai sheqi takeyi.
Babu ta yadda zasuga na ciki, sai na cikin ne yake kallon su.
Kamo hanun nusaiba salma tayi tana cewa ,"Mu koma to, tsayuwar me mukeyi.
Har sun kusa kofa suka ji ya al-amin na k'iransu .
A tare suka juyo ,suka saki murmushi a tare.
"Yayanmu nayi missing d'inka yau wlh."cewar nusaiba.
"Ke kikayi missing d'inshi ko ni, tunda garin Allah ya waye ban sashi a ido ba ,inajin ma tun asuba ya bar gidan."
Salma tace.
"'yan matan ummi kunga yadda kuka yi kyau kuwa, ku tsaya na muku hoto."
Al-amin ya fad'a lokacin da ya iso dab dasu ,ya ajiye k'atuwar ledar dake hanunshi, yana kuma fiddo wayarshi daga aljihu.
D'aukansu hotuna yayi tayi wani su biyu, ya musu d'add'aya snn sukayi tare dashi.
Saida suka gama snn ya d'auko ledar da ya ajiye ya mik'awa nusaiba yace "Ku k'ara ku rabawa bak'i."
Karb'a Nusaiba tayi tana cewa "Me kuma muka samu? Na lura sai wani ji da aunty salmannan kukeyi dukanku, wlh kukayi wasa nima sai na zuciya nayi karatun." tana fad'a tana bud'e ledar.
Dariya dukansu sukayi snn Salma tace"ki zuciyan mana muma haka muka fiso."
Snn ta juya ga ya al-amin."Yayanmu wancan bai isa ba har sai ka dad'o wani?"
"Wnn dabanne sai na dawo ana jirana."
Yace tare da barin wurin , suna kallonshi ya shige cikin mota.
Kallon juna sukayi kafin nusaiba tace "Wnn kuma motar waye?"
"Allah masani." Salma ta bata amsa.
Fitar da abinda yake ciki nusaiba tayi , hand bags ne masu kyau da k'wari diff.colours.
"Woow , duba aunty Salma ,hand bags d'innan sunyi kyau."
Cewar nusaiba.
Karb'a tayi tana dubawa.
*Congratulations Ummu Salma.*
*May Almighty Allah bless ur knowledge.*
*Curtesy.....A.M.G.*
K'ara girman idonta tayi tana kallo snn nunawa nusaiba.
"Duba kigani."
"Waye shi?"
Nusaiba ta tambaya.
"Ina zan sani."
Salma ta bata amsa.
Rik'e ledan sukayi a tare suka shiga gida, nan suka tarar an k'are wa'azi , malama Tasalla tana addu'ar rufewa.
Fati suka tarar har ta fara rabon take away.
Robobi ,mafici, cups ,da aka manna musu stickers, suka shiga rabawa, tare da bags d'in.
Haka taro ya watse cikin farin ciki, sai fatan alkhairi ake mata.
Da dare suna had'e dukansu a tsakar gida ,duka yaran gidan suna had'e har da Malam, kamar yadda ya saba zama cikin iyalanshi idan d'alibanshi basu zo ba ,hira suke cikin raha, duk suna cikin nishad'i.
Al-amin ne ya shigo da sallama, dukansu suka maida hankalinsu kanshi suna amsa sallamar.
Kusa da Mal. Yazo ya zauna ya gaisheshi snn ya gaida ummi da kanwarta, kannenshi suka mishi sannu da zuwa.
"Hamza zo ka tayani d'aukan wasu kaya a d'akina.
Cewar Ya al-amin, bayan ya mike yana zura takalmanshi.
Ba tare da b'ata lokaci ba sai gasu sun dawo d'auke da kaya.
Kayanya shiga fiffitarwa nan kusa da Mal.
Saida ya gama fitarwa yace "Salma ga sak'onki."
"Wnn fa daga ina ?"
Mal. Ya tambaya yana kallon kayan.
"Oganmu a gurin aikine ya bani na kawo mata."
Wani zabura salma tayi har ta tsorata pendonsu dake zaune kusa da ita.
Kamar wacce aka hankad'a ta isa gaban al-amin ta zauna tamkar wacce zatasa shi ya maida maganar da ya gama fitarwa yanzu.
Hanunshi ta kamo ta rike ,bakinta na motsi ta kasa magana sai kallon shi takeyi.
"Yayanmu."
Tace still idanunta cikin nashi, ta rasa me zata ce mishi, ta rasa ta ina zata fara,
Girgiza mishi kai ta farayi alamar maganar ki fitowa.
Kawar da idonshi yayi tare da zame hanunshi daga cikin nata, kallon da take mishin ne yaji shi wani iri ,kallon yayi kama kwarai da na tuhuma, snn kwayar idanunta kamar suna nuna tamkar akwai wata laifi da ya aikata mata.
*Mom Afrah🌹*
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W.*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljala)*
27.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
*Wnn shafi nakine Hajiya Aisha (Hausa novels books, na gode da kulawa Allah ya bar zaumunci.*
*** *** ***
Kallonsu kowa yakeyi cike dason jin k'arin bayan.
Lura da hakanne yasa ya al-amin ya fara nuna musu kayan da d'add'aya.
Sphygmomanometer, na auna B.P. weigheing scale,na gwada nauyi. thermomether, na gwada temprture, first aid box da duk wani abin buqata, sai kuma qaton text book na research.
Bin kayan da kallo salma takeyi zuciyarta na bugawa, a yau kam bata yarda da cewa kyautatawace haka kawai ba kamar yadda yayanta yake fad'a mata, a yau zuciyarta ta fara raya mata wani abin daban.
Tana gama wnn tunanin taji hrt d'inta ya buga da k'arfi har sai da ta kamo yatsun hanunshi guda biyu ta matse da k'arfi.
"Ya haka Salma?"
Ya fad'a qasa qasa tamkar baya so a jishi.
"Ya al-amin."
"Ya dai?"
Kamar nusaiba tasan abin da ke zcyr salma ta matso tace "Yayanmu hand bags na d'azu kuma daga ina?"
Saida ya d'auke kanshi daga kallonsu, sbd kaucewa kallon kurillar da salma ke mishi, yace "Duka shi ya bayar."
Kallo su salma tayi taga duk hankulansu na kan kayan snn tace , "Me yasa kake karb'an mishi kayanshi?"
Ba tare da ya kalleta yace "Sbd ba kyau maida hanun kyauta."
"Ka tabbata tsakani da Allah yake wnn abin?"
"To da tsakaninshi da dake ne? dan mutum yayi kyauta sai a tuhumeshi? Na d'azu taya murna ne ,yanzu kuma gudunmawa ne dan ki taimakawa al'umma, ko ba daga yanzu karatunnaki zai fara amfani ba? Kuma ko bai saya miki ba ina da niyyar saya miki idan aka biyani kud'in aiki na?"
Duk maganar da sukeyi a hankali sukeyi.
Sai a snn ta d'an samu relief amma hankalinta bai gama kwanciya ba.
Su kuwa sai yaba kayan suke suna sa mishi albarka , Su Hamza har da cewa tazo ta gwada B.Pn su , Fati da nusaiba kuma sukace ta gwada weight d'insu.
Ita dai binsu takeyi da kallo tana kissima abubuwa da dama a ranta.
Kallonta ta maida kan Mal. taga shi hankalinshi yana kan labarin da kanwar mamansu take bashi.
Su nusaiba ne dai suke ta jujjuya kayan kowa na fad'an albarkacin bakinshi, daga qarshe fati ta tattara ta shigar d'akin Ummi.
Har aka watse hiran Salma dai jikinta a sanyaye yake.
Sai washegari su Ummi suka matsa mata da ta mishi godiya, ba dan ranta ya soba ta nufi d'akin al-amin.
Maganar ma kamar shaketa akeyi tacewa wa al-amin ya qira oganshi ta mishi godiya.
"Zan dai baki nambarshi ki qira shi."
Yace mata .
Cikin nuna gajiyawa da zancen tace bani da kud'i a wayata, in kaima baka dashi, sai in baka saqo kace mishi na gode."
Mika mata wayar yayi yana cewa "Gashi kirashi."
B'ata fuska tayi tace "in ce mishi wacece?"
"Ummu salma "yace a taqaice.
"Nikam karb'a ka fad'a mishi saika bani in mishi godiyar."ta karishe kamar zata sa kuka, bakinnan a cune.
Karb'a yayi, yayi dialing nambar , saida ya d'auka suka gaisa snn yace mishi Ummu salma ce keson magana dashi."
Miqa mata wayar yayi ta qara a kunne.
"Assalamu alaikum."
Tace a sanyaye.
"Wa alaikumussalam."
"jin tayi shiru ya sashi cewa Ummu ya kike ya mutanen gida."
"Lfy, ina yini?"
"Lfy lau Ummu ya hidima?"
"Alhamdulillah."
Tace snn tayi saurin cewa "Ya al-amin ya kawo min saqo ,na gode Allah ya qara bud'i."
"Amin, Amin, nima
End Ads