x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 6 - IN SO CUTANE

  • 15001 words
  • 18000 words
  • Out of 26921 words

Category: Tale Stories

Views 77

09 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
snn idan ya dawo tana zuwa ta mishi sannu da zuwa, bayan haka tana kai mishi abinci duk da ko kallon abincin bayayi hakan baisa ta fasa kai mishi ba tunda shi yake cefanowa, ita dai fatanta watarana ya sauqo komai ya zama labari.
Har tad'an wuce ta dawo, "Akwai abinda kake buqatane?"
Ta tambaya a ladabce.
*Gaisuwa gareki sister Shema'u (Mmn Doctor)Ina yinki tawan.*
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal)*
19.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
This page is specially dedicated to you my brother.
*D'alhat Musa Muhammad Dagauda.(Abu Hanifa.)*
I am very proud of u bro.
*** **** ***
Firgigit yayi ,alamun yayi nisa a tunani.
Ya kalleta kad'an ya kauda kai "Babu."
Yace a tak'aice.
Kamar zata wuce sai kuma ta canza hanya gurin d'an k'aramin fridge d'inta dake cikin falon ta nufa.
Ruwa mai sanyi ta d'auko da plate da d'an karamin glass cup ta kawo ta ajiye kusa dashi snn ta wuce .
Da kallo ya bita snn ya maida kallon kan ruwan da ta ajiye mishi.
Fitowa zata wuce,har yanzu dai mamaki bai barta ba , ba taganshi a falon ba sai ruwan da ta ajiye.
Zuwa tayi ta d'auka ta mayar , ga mamakinta sai taga yasha ruwan.
Murmushi tayi ta tattara tana ci gaba da jinjina al'amarin.
A gurguje ya shiga d'akinshi yayi wanka tare da alwala dan zuwa sallar magrib.
Zuciyarshi fal tunanin aikin da salma ta sa shi.
Ya dai quduri niyyar bata lokaci da kulawa saidai ya rasa ta yadda zai fara.
Sai bayan sallar isha'i ya shigo .
Falonshi ya nufa ya zauna tare da kiran wayar salma.
Yaudai yasan kewarta sai ta kusa illata shi.
Ko gaisawa bai tsaya sunyi ba yace "Da zan iya yau d'innan da fushi zanyi da ke Salma."
"Me kuma nayi Ahmad?"
"Kin fini sanin lafinki ."
"Nifa ban sani ba sanar dani."
"Da kika haramtamin ganinki yau da gangan dole kice baki sani ba."
"Oho, ai har da gobe ma."
Ta fad'a tana dariya duk da dai dauriya takeyi dan ta qara mishi qwarin gwiwa.
"Salma, har ma dad'a jaddada min kikeyi har da gobe ma ko?"
"Eh mana."
"Zamu gani goben idan da qafar ki zan zanzo."
"Assalamu alaikum."
Asiya tayi sallama tare da kutsa kai cikin falon dan sam batayi tsammanin samun shi ciki ba tunda dama ta saba kullum saidai tazo ta ajiye abincin baya nan.
"Wa, alaikumussalam, bismillah ."
Yace snn ya maida hankalinshi ga wayar da yakeyi.
Zai qara magana yaji ta kashe wayar.
Kallon wayar yayi da kyau ya tabbatar dai kashewan tayi ,sai ya sake dialing.
Shiru bata d'auka ,ba har sau uku.
Ajiye wayar yayi yana maida dubanshi kan asiya dake kofar fita.
"Zo ki zuba min abincin."
Taji yace.
Cak ta tsaya tana tunanin ko bata ji da kyau bane.
"Baki ji bane?"
Yanzu kam ta tabbata kunnuwanta sun jiye mata dadai.
Dawowa tayi tayi serving d'inshi , har taje ta kawo ruwan wanke hanu da nasha, yana zaune dafe da kanshi da hanuwanshi biyu.
Salma dai ta bashi aiki, yanzu kuma tunani yake koma zaiyi bayan wnn.
Har ta juya zata tafi ya d'ago ya kalleta.
"Ina zaki kuma?"
To fa, baffa ahmadu kam yau lafiya kuwa.
A tsanake ta dawo ta zauna a k'asa nesa dashi kad'an tayi k'asa da kai.
Gaskiya abin fa da mamaki, yau ya canza mata da yawa, ko dai har ya sauqo ne da wuri haka.
Ko me ya canza mishi ra'ayi?
Bata ida tunani ba taji yace " ke baza kici abincin bane?"
"Yanzu zanje inci."
"Me ya faru da wann an d'in da bazakici anan ba."
😳anya bappa ahmadu ne kuwa, ko canza mata shi akayi.
Hhhh nace ba'a canza miki shi ba asiya, addu'ar kice ta karb'u ,da kuma qoqarin ummi, uwa ta gari mai sanin ya kamata da hangen nesa , da kuma baiwar Allah salma , mai jin maganar iyaye, da d'aukan nasiha ga kuma kishin kai.
"Asiya baza kici abincin ba?"
Adarare ta matso ta zuba abincin tana satar kallonshi, shiko hankalinshi ya maida kan abincin da yake ci.
Gefe ta koma tamkar wata bak'uwa ta zauna taci itama.
Tana gamawa ta tashi ta tattara tana mamakin yadda yaci abincin da yawa.
Shima duk abinda takeyi kallonta yakeyi, yaji dad'in abincinta ba k'arya ,baiyi tsammani zata iya girki kamar haka ba, amma fa shi yasan na Salmanshi sai yafi wnn dad'i.
Tana gama gyara gurin tafita.
Ajiyar zuciya ya sauk'e yana yabawa kokarin da yayi a yau.
Wayar salma yaci gaba da nema yaji ta a kashe ,duk haushi ya gama cika shi, ita ta hana shi zuwa snn ta k'i suyi magana ko ta wayar ma.
Washegari ,tana jiran taji fitowar shi taje ta gaisheshi yadda ta saba, sai taji shi ya shigo .
Gaisheshi tayi tana wani sunne kai, ya amsa yana binta da kallo, kunyarta irinta salma .
Yace aranshi.
"Ke kuma haka akeyi ,jiya kika tafi ba ko jam wala,(mu kwan lafiya)
"Hmmm ."
Tace ,kawai ba magana, sai murmushi da takeyi da tuno lokacin da yace mata hmm zai kasheta.
Yau kuma ko me zai ce mata?
"Hmmm ,ke ma inda dad'i."
Taji yace mata.
Murmushin dai ta kuma yi bata ce mishi komai ba.
"Zan fita to."
"A dawo lafiya, Allah ya bada sa'a."
tace.
Har ya fara tafiya a ranta tace bari dai ta gwada sa'arta.
"Baza ka karya ba zaka fita?"
ta fad'a a d'an tsorace.
Saida ya juya ya kalleta snn ya ce.
*08161594233*
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal)*
20.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
"kin gama abin karin ne?"
A hankali ta sauk'e ajiyar zuciya .
"Na gama."
"To kawo min."
Sauri sauri ta je ta had'a komai a babban tray.
A tunaninta zai koma falonshi, sai kuma ta sameshi a falonta.
"Nan zaki kawo."
Yace ganin tana wucewa.
Yauma zama yayi ya take abinci yayi naqq snn ya sallameta ya tafi, har da tambayarta ko akwai abinda take buk'ata.
Hakama da ya dawo saida yaci abinci ya shirya ya tafi gidansu salma.
"Haka mukayi dakai?"
Abinda ta fara ce mishi kenan bayan sun gaisa.
"Kema haka mukayi da ke?"
"Me nayi ni kuma?"
ta tambaya tana noke kai.
"Me yasa jiya muna magana kika kashemin waya kuma na k'ira kika k'i d'auka."
"Oh ayya lokacin naji kamar amarya na kusa ne shiyasa, kuma kaga bazata ji dad'i ba kuna tare kana magana da wata babu dad'i."
Harara ya banka mata, itako abinma dariya ya bata, ta shiga yi k'asa k'asa.
"Wlh, kika kuma kashe min waya zan fasa bada ratan ,ci gaba zanyi da zuwa kamar yadda na saba."
"Allah ya baka hak'uri, amma maganar gaskiya hakan bai dace ba, dan Allah idan tana kusa ka daina k'irana. Ko ni akaiwa haka bazan ji dad'i ba, kuma irin haka sai ka sa ta rika jin haushina wlh, kuma kaga maganar yawan zuwan nanma da gaske nake ,ka bada ratar atleast kwanaki biyu ko uku kafin kazo, dan itama tasan ka mutuntata."
Saida ya barta ta gama zuba zancenta yace "Idan naqi fa?"
Shiru ta mishi.
Ya kuma cewa "Auntyn asiya nace idan naqifa , me taya kishiya kishi."
Dariya ta d'an yi tace ,"nima sai naqi fitowa kalas."
"Allah, ko, to kalle ni mana ki rika bani amsa, kina magana kina sunkuyar da kai, kalli cikin idona ki fad'a idan da gaske kikeyi ."
Jin tayi shiru ya kuma cewa " ki gwada qin fitowa ki gani idan ban shiga har cikin gidan ba irin ba rannan kema kin san zan iya.
Nifa mamaki ma kike ban yanzu , kwanakin baya har da ciwo kikayi kan kishi amma yanzu ke kike taya kishiyar taki kishi akan kanki.hmm abin har da tsoro mafa ya fara bani , ko dai auren ne yasa kika rage sona salma?"
Kawar da kanta tayi gefe tanaji kamar tayi kuka ,dan ita tasan abinda take ji game da maganar auren nan nashi.
Daurewa tayi tace.
"Kaji tsoron Allah dai ka sauqe haqqin da ya rataya a wuyanka ,kuma kar ka cusa min ra'ayi nikam."
"To naji malama salma , wa'azin ya isa haka."
Ya fad'a yana tunani
a ranshi da yayanshi yasan wacece Salma da bai hanashi aurenta ba.
**** **** ****
Zaune suke cikin falon Ahmad, suna kallon wani indian film d'in da aka sa a bollywood.
Ahmad dai kallo yakeyi amma sam hankalinshi baya ga t.vn.
Tunanin yadda al'amarinshi da Salma zai kasance kawai yakeyi.
Har ga Allah abin ya fara bashi tsoro yanzu, babu abinda yafi d'aga mishi hankali kamar idan ya tuna salma ta kusa gama karatunta amma har yanzu babu alamar yayunshi zasu amince mishi ya aureta, tsoronshi duk ranar da zata ce mishi ya turo magabatanshi.
Ita kuwa asiya kallonnata rabi da rabi ne, tana kallon film, rabin hankalinta kuwa ya karkata ga son gano abinda yakesa Ahmad nisa cikin tunani.
Yawancin lokuta takan ganshi cikin damuwa da tunani mai zurfi, duk da yana kokarin sake mata suyi hira cikin nishad'i, yana bata kulawa daidai gwargwado ,amma ko ba'a fad'a ba tasan yana cikin damuwa.
Kwantar da kanta tayi a kafad'arshi, wanda ya tilasta mishi sauqe ajiyar zuciya , dan ya manta yana tare da mutum cikin falon.
Maida kallonshi yayi kanta snn yace "Ya dai Sal- asiya."
Bata amsa mishi saima kokarin d'aga kanta da takeyi .
Kwantar da kannata dad'ayi yana mai tuhumar zuciyarshi da bakinshi wajen gaza b'oye halin da yake ciki.
A kullum mutuncin yarinyar qaruwa yake a idanunshi sbd hakuri da kuma kawaicinta.
Yasha kiranta da sunan Salma ,duk da dai ba amsawa takeyi ba, amma bata nuna mishi damuwarta ko a fiska ,har ya zamo idan ya kirata da Salma shi da kanshi abin yake bashi kunya.
Asiya bata da matsala, ga haquri ga tsafta ,kullum fes fes zaka ganta daga gidanta har ita kanta.hakan ya bata matsayi mai girma a zuciyar Ahmad, saidai yasan babu abinda zai girgiza kujerar sarautar sarauniyar da ke mulkar zuciyarshi. wato Salma.
K'ok'ari yakeyi kar damuwar da yake ciki ya shafi zamansu , amma ya rasa me yasa zuciyarshi da bakinshi suke nuna gazawarsu.
Kallonta ya kuma yi yaga ta lumshe ido tayi lamo tamkar maijin barci.
"Barci ko?"
Girgiza mishi kai tayi alamar a'a.
A sanyaye tace ina tunanin yaushe zanje inga Adda na ne.
Tausayi ta bashi yanda tayi maganar a sanyaye ,yasan ba wnn kad'ai ke damunta ,amma ya zasuyi dukansu cikin damuwar suke, ya san yama fita damuwa dan a tunaninshi nata mai sauqi.
Yau aurensu watanni hud'u kenan da kwana shida.
Ita kanta tasan zuwa wnn lokaci an samu canji daga ahmad sosae ba kad'an ba.
Tasan haqurinta ya mata rana ya kumayi amfani, shawarwari da naseehar Addanta sun mata amfani sai dai damuwar da take gani a fiskar ahmad wasu lokuta yana d'aga mata hankali., har yakansa taso tasan taqamammen matsalarshi duk da dai jikinta yana bata damuwar bazata wuci a kan yarinyar da yace mata yana so bane.
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
21.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
Kwanto da ita yayi jikinshi gaba d'aya snn yace mata "Yaushe kike so kije ki ganta?"
Da sauri tace "ko yanzu ma."
Hancinta yaja yana murmushi yace "'Yar adda ,yanzu kam dare yayi ai, saidai gobe ko jibi ko gata ko..."
"Kaiiii...😳ta katse shi tana zaro , wnn dogon lissafi? goben dai dan Allah."
Ta fad'a a shagwab'e.
Ajiyar zuciya ya sauqe "Sai goben to in Allah ya kaimu."
"Allah ya kaimu"
tace zuciyarta fal farin ciki.
"Amma fa tare zamuje mu dawo dan ba jimawa zakiyi a can ba."
"Ayya dai."
Ta fad'a da fiskar tausayi.
"To ba ganin su kawai zakiyi ba?"
"Har da Abba fa ,kasan shi ba lallai ne na same shi a gida ba, sai yamma yake dawowa."
"Sai nayi tunani akai idan naga zan iya."
"Zaka iya ma, naga kai d'inma sai yamma kake shigowa."
"To kuma wa zai min girki?"
Shiru tayi ta rasa ma me zata ce mishi.
"Hmmm, baki ji bane?"
"Naji, basai ka siyo mana ba abu na rana d'aya kawai fa."
"ni kuma naki nakeson ci ya kenan?"
Da sauri tace "to zan dafa maka in na dawo."
"Huta abinki ,da wasa nake miki, Allah ya kaimu goben."
"Ameen ."Tace tana jin dad'in gobe zata je gidansu, dan tunda tayi aure bata je ba sai k'annenta ne suke zuwa mata.
Sai kuma gidansu ahmad da taje sau biyu.
** ** **
Tafe suke ita da k'awarta faleela , paper rik'e a hanunta sai jakarta da ta rataya.
Dukansu biyu sanye suke da uniform na sch. Of nursing.
A nitse suke tafiya suna tattaunawa , hakan yasa Salma bata tari napep da wuri ba, har saida suka zo ta inda faleela zata ratse ta yi hanyar gidansu suka d'an tsaya dan su k'arasa tattaunawarsu.
Sallama suka wa juna kowa ta kama hanyarta .
"Sssssss."
Taji ake signal ,kusa da ita.
Ko alama bata nuna taji ba balle ta juya .
"ke 'yan mata."
Juyowa tayi da murmushi d'auke a fiskarta jin muryar yayanta Al-amin.
"Dama kai kake min wnn k'iran 'yan itskan."
Dariya sukayi dukansu sbd yanda ta ambaci iskan ,ta fitar da harafin s d'inne bayan ta danne harshenta da hak'oranta ta fito dashi tsakanin tsiririn wushiryarta.
Kamar yadda qaninsu khalil yakeyi.
Halittarshi ce haka amma ko da yaushe ya ambaci harafin sai sunyi mishi dariya.
"Me kakeyi anan yayanmu?"
"Aiki mana baki gani ne?"
Ya fad'i yana nuna blocks d'in dake tare a kusa dasu ,labourers sai jida sukeyi suna kaiwa wani wajen da wasu ke gini.
Sai a snn ta lura da blocks d'in.
"Yanzu ya yayanmu haka kake d'aukan blocks d'innan masu nauyi."
"Wa ya gaya miki suna da nauyi."
"Da nauyi mana da gani ma ba sai an fad'a ba."
Ta fad'a tare da sunkuyawa tana kokarin d'aga block guda.
"Wasshh."
Tace tana yarfe hannayenta bayan ta ajiye block d'in da ba wani d'agawan kirki tayi ba sai raki .
"Madam karambani ,kin d'auka aikin da ragwayene irinki."
Ya fad'a tare da dungure goshin ta.
'yar dariya tayi tace "Gaskiya fa kuna kokari yayanmu."
"Neman halas kenan ummulu yana da wuya ."
"Aikam ,Allah dai ya biyawa duk mai neman halaliyarsa bukatunshi,Allah ya sanya albarka a sana'ar."
"Amin ummulun ummi ,muje in raka ki ,kinga sunyi nisa a aikinsu sun barni."
Ya qarashe maganar yana nuna ta gefen da yake ginawa ya bari.
"Au ginin kakeyi kenan?"
"Eh, wad'ancan suke kai mana blocks muna ginawa, gidansu oganmu ne muke renovating."
"Allah ya taimaka ."
Tace ,daga nan suka ci gaba da tafiya, har bakin hanya.
_Two days later_
"Ummulu, an bani saqo na manta ba isar ba."
"Mik'o."
Tace tana mik'a mishi tafin hanunta.
Kallonta ya tsaya yi snn suka tuntsure da dariya dukansu biyu.
"Daga an bani saqo sai mik'o, yaushe kika zama haka?"
Dariya ta kuma yi tace
"Nayi tsammanin kud'i aka baka ka bawa baiwar Allah Salma."
Har da wani marairaicewa.
"To ba shi bane sai ki had'iye kwad'ayinki."
"Menene yayanmu."
"Oganmu ne yace in gaisheki."
😳"Oganku?"
*Slm, fans pls a rika haquri damu , masu magana ta pc da masu yi a grps, duk wanda yayi magana ban amsa ba that means ban gani bane, wasu kuma waiting yake nunawa, and masu magana a grps kuma, ba ko wani chat nake iya bi na karanta ba dan grps d'in sunyi min yawa ,idan nace ko wanne sai nabi na karanta to fa bazan samu time na typing ba, idan har kayi magana a grp ba response ka min magana personally in har na gani zan amsa, so bear with me , ina qaunarku kamar yadda kuke qaunata ,na gode.😍😍😍*
[17/12 06:25] Hajara: *πŸ’”πŸ’”IN SO CUTANEπŸ’”πŸ’”*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
23.
πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”πŸ’”
"Zauna kiji salma."
Zaman tayi tana fiskantarshi.
"akwai abinda baki sani ba, ogan nan da kike gani?"
Da sauri tace nakeji dai ban tab'a ganinshi ba ai.
"Sorry, da kike ji to.
Duk mutum mai son karatu burge shi yake yi, yanason mutumin da yasan kanshi.
Tun ranar da ya ganki da uniform, kuma nace ke kanwatace , yaji kin burgeshi"
Katse shi tayi da cewa ,ni d'in ce na burge shi ,ko uniform ko kuma karatun?"
"Duka."yace a taqaice.
"Kuma idan kika sake katse ni ,zaki bar nan da rarrafe."
"Afuwan ya akhy."
Ta fad'a tana rike kunnuwa.
"Yauwa kina ji, ce min yayi ,babu yadda baiyi da qannenshi mata ba su karanci science courses, amma sam sunki ,wai da wuya , tsoro sukeji, baza su iya ba, shi kuma yayi burin a cikin k'annenshi a samu doctor ko nurse , ya musu alk'awarin ko nawa zai iya kashe musu ,amma duk sunki, abin takaicin dukansu yaran gidan su babu wanda ya karanci science."
"To shi me ya hana shi karanta ,tun da yana so?"
Harara ya galla, mata tayi saurin rik'e bakinta , "sorry yayan ummulu, mantuwa nayi."
"Baki ji me nace miki bane? K'annenshi mata yace yakeso su karanci course d'in sbd kishin addini da kuma taimakawa mata 'yan uwansu , ko kema ba hakanne ya saki karatunba?"
Gyad'a kai tayi tare da cewa "hakane."
"To shi yasa da yaga kanwar d'an gidanshi tanayi yaji dad'in abin kuma yaga zai iya bada tashi gudumawar ,kuma ba ke kad'ai yake bawa irin wnn kulawar ba, matasan unguwarsu masu kokarin karatu ma yana taimaka musu,snn ko ni nan da kika gani lokacin da nake makaranta ba k'aramin taimakona yayi ba, yanzu haka shawara yake bani da inje in had'a masters , ina fata kin fahimta?"
"Na kusa dai."
"Tashi ki bar na, tunda yau kuma kwakwalwar ta cushe."
Ya fad'a yana mikewa .
Cikin dariyar kular da shi da tayi tace "Tsaya ina da tambaya."
"Shi wani mataki ya taka a karatun, da shi da matarsa duka."
"mts bana son tambayar ganganci, mutum mai karfafawa wani gwiwa yayi karatu, shi kuma me zai jira yana da hanyar karatun."
"To kuma shine ya tsaya aikin gini ,ko yana wani aikinne?"
"Wai ance miki dole mutum idan yayi karatu mai zurfi sai yayi aikin goverment ne? ina ce iliminshi a kwakwalkwarshi take, kuma da abinda ya karanta zaiyi aiki,.
Shi wnn da kike ji babban contractor ne, yana kuma da companyn kayan aikin gini masu inganci, yana da gidan block na musamman ,gari gari ake bashi contract, har k'asashen waje yake zuwa, duk tafiyar da kika ga nakeyi tare dashi ne , dan ina d'aya daga cikin amintattun yaranshi.
Kuma kin san me ?"
"sai ka fad'a."
"Office yake dashi musamman ,government ta san da zama shi ,snn ya da motoci na d'aukan kayan aiki da blocks ba sai ma an nema a wani waje ba."
Tab'e baki tayi tace.
"Allah ya taimaka to, ka kuma ce mishi na gode."
Dan ita gani take b'ata lokacinshi kawai yakeyi wajen son fahimtar da ita ko waye mai gidanshi.
*** *** ***
Ma sha Allah, gidan ahmad yanzu sai sambarka, komai ya daidaita ,zama suke cikin aminci.
Duk da har yanzu babu abinda ya ragu na soyayyar salma cikin zcyr ahmad, haka kuma bayan kwana biyu yake zuwa gun salmar,
Snn daga gunta ma babu wani canji.
Snn babban karin farin cikinshi kuma a iya zamanshi da Salma bai tab'a ganin ta ko yaji labarin an ganta da wani ba.
hakan bai hana shi bawa asiya kulawa ta musamman ba.
A kullum kokari yakeyi yaga ya danne damuwar shi da kuma soyayyar da yakewa salma a gaban asiya, dan a yanzu tana da matsayi na musamman a zuciyar ahmad.
Babban abin da ya k'ara mata matsayi da k'ima a idonshi shine cikinshi da take d'auke dashi na watanni uku.
Rabo
End Ads