zai wargaza mana tsari , yanzu fa sam bakya karatu kamar da."
Ta karashe maganar tana satar kallon Ummi.
"Adda magana ."
Cewar Fati ,tana hararar Nusaiba.
Itama Salma Hararar ta zabga mata snn tace "To maganad'isu ,yaushe kikaga banyi karatu ba, naga lokacin da nake karatun duk kunyi nisa a bacci."
"A da kenan, yanzu kam ina zaki barmu muyi bacci mai nisa yanzu yanzu karar waya a ishe mu kuma da kashe murya."
"Taraba state broadcasting service (T.S.B.S.)"
Cewar Fati.
Nusaiba ta amsa da "A a kin manta T.T.V. ne Taraba television."
"Kin shiga uku da gulma Nusaiba ,dan tsabar gulma har wani ina hana ku bacci ,Sa idonki dai ya hanaki kada ki min sharri."
Gyara zama tayi ta fara magana seriously "Aunty ki ture batun wasa, wlh ba gulma ko sa ido ,abinda na lura dashi nake fad'a nifa gani nake kamar Lucky bai damu da karatunki ba ,idan ya damu k'arfafa miki gwiwa ya kamata yayi ,amma kullum shike hana ki karatun ,anya wnn idan a gidanshi kike zai barki kiyi karatunma?"
"Kai Adda Nusai kamar wacce aka aiko?"
Cewar Faty.
Zare mata ido tayi "Ke ban hana ki kirana da Nusai d'innan ba, ki kirani da full name d'ina 'yar rainin hankali, kuma daga fad'ar gaskiya sai ace an aiko ni, nifa so nake auntynmu ta fito da result mai kyau amma wnn d'an wailawan yana so ya kawo mana cikas."
Ummi har yanzu bata kallesu ba balle tayi magana amma tana sauraron duk abinda suke cewa.
Itako Salma kogin tunani ta fad'a ,maganar Nusaiba fa gaskiya ce ,tunda take tare dashi bai tab'a kawo mata maganar karatunta ba ,bai tab'a tambayarta burinta idan ta gama karatu ba ,kuma ko ya kirata tace mishi tana karatu bai tab'a ce mata Allah ya bada sa'a ko ya taimaka ba, shi dai kullum maganarshi ta amince ya turo manyanshi, kuma bayaso a d'au lokaci ba'ayi bikinsu ba.
To me hakan yake nufi.
Fati ce ta matso kusa da Nusaiba tace a hankali "Munji mama Nusai, zamu gyara, uwarsu matar ubansu."
D'aga hanu tayi zata d'aka mata duka ta goce ta sake binta sai ta arce tayi cikin d'akinsu tana dariya.
Kan gado ta fad'a tana dariya tana d'agawa Nusaiba hanayenta tare da cewa "Na tuba bazan kara ba Mama Nusai."
Dariyar har kamar shaketa yakeyi .
Lallai yau fati ana jin raha.
Itama kanta Nusaiba dariya abin ya bata sai ta fad'a kusa da fati itama tana darawa.
Tsagaita dariyar Fati tayi snn tace.
"Fisabilillahi me yasa kikawa auntynmu haka, kinga bata ji dad'in abin ba wlh, nasan gaskiya kika fad'a amma dakin yi mata magana tsakaninku Ummi bata wajen."
"Hmm baza ki gane bane Fati aunty tana yiwa mutuminnan matsananciyar soyayyar da ba lallai bane da saurareni ta fahimci abinda nake nufi.
Da gan gan na mata haka ,ko ba komai nasan Ummi zata mata magana kuma in shaa Allah zata saurareta ta gyara."
"Allah ya sa to."
Fati tace.
A can waje kuma su fati na barin wajen Ummi ta d'ago ta kalli Salma.
"Ummusalma."
Kusan a firgice ta d'ago "Na'am Ummi."
*Mmn Abdul & Noorain*
[17/12 06:24] Hajara: *ππIN SO CUTANEππ*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Aunty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
8.
ππππππ
*Gaisuwa da fatan alkhairi masoya a duk inda kuke, ina kaunarku fiye da yadda kuke qaunata*
*Gaisuwar ban girma gareki ummu D'alhat, Allah ya bar zumunci.*
*Maryam A.I Gital*
Kina raina ,Allah ya qara miki lafiya da basira.
*Ciwo lokaci guda yake shiga ,amma sauqi sai a hankali, Alhamdulillah, na samu sauqi 'yan uwa saidai fatar Allah yasa ciwon ya tafi gaba d'aya.*
*Naji jiki wollah.*
"Nasan Nusaiba bazata yi miki k'arya ido da ido ba, kai ko a bayan idanki ma banyi tsammanin haka ba , abinda nusaiba ta fad'a yana kan hanya ,muddin kika biyewa Ahmad ya hanaki karatu baki kyautawa mal.ba.
Mal. Ya yarda zakiyi kuma zaki iya shi yasa ya tsaya tsayin daka na ganin kin yi karatunnan domin cikar burinki.
Duk da cewa tun farko aure yaso ya miki kika nuna ke karatun kikeso kuma ya biye miki.
Kina tunanin zai ji dad'i idan lokaci guda kika watsar da wahalar dayayi na ganin kin cika burin ki."
Kanta a duke tace "kiyi hakuri Ummi bazan k'ara ba."
"Baza mu takura ki ba Salma idan auren kike so yanxu ki sanar damu dan baza mu tauyeki ba kinga sai in sanar da Mal. a fad'awa Ahmad d'in ya fito."
Girgiza kanta ta shigayi "A'a Ummi wallahi sai na k'are karatun."
"Ni dai na gaya miki kika ci gaba da biye mishi kina wasa da karatun matakin da zamu d'auka kenan."
"In shaa Allah daga yauma an dena Ummi kiyi hakuri."
Fati ce ta iso ta karb'i shinkafan da suka gyara tana kallon auntyn tasu da gefen ido ,dan son gane wani yanayi take ciki.
Saida ta wanke lallenta snn ta bar wurin , tana isa kofar d'akinsu ta samu nusaiba zaune daga gefe tana kankare k'umbunanta .
Kurr nusaiba ta kureta da ido ,itako tayi kamar bata ganta saima d'an murmushi da tayi ta wuce ta .
Saida tazo ta bayanta snn ta talle keyar ta tare da cewa "wani irin kallo ne haka kamar baki da gaskiya.
Ajiyar zuciya ta sauke dan duk a zatonta auntyn tayi fushi da itane.
"Sorry my aunty ,ciwon sub'ul da baka ne ya kamani d'azu a gaban ummi."
"Allah ya shirye ki uwar 'yan magana , Mama nusai."
Ta karashe maganar tana murmushi dan tasan ta tsokano ta.
Cuno baki nusaiba tayi "Allah zanci kaniyar Fati."
"Nawa dai zaki ci tunda ni na fad'a."
"Wane ni swt aunty ita dai da ta fara kirana da sunan."
Haka suka ci gaba da rahansu tamkar babu abinda ya faru.
Kamar yadda ta alkawarta haka ko akayi bayan yazo sun sha firarsu zai tafi yake ce mata sai tajishi anjima idan ya kirata.
"Yauwa Ahmad dama akwai wata maganar da nakeso muyi da kai."
Dawowa yayi ya zauna "Ina jin ki sweety na."
Sai da ta d'an murmusa kafin ta fara magana.
"Dan Allah Ahmad kiran daren nan nakeso ka d'an rage dan yana shiga lokacin karatuna ,bana samu nayi karatu kamar da wlh."
Tunda ta fara magana ya kafe ta da ido har ta gama .
"Karatu dai, karatu dai."
Yace a ranshi.
"kayi shiru Ahmad."
"Salman dai."
Yace mata fiskarshi d'auke da murmushi ,dan ya lura duk lokacin da aka ce mishi Salman sai tayi ta mishi kallon mamaki.
"Wai ni me yasa ake ce maka Salman ."
"To meye sunan idan ba Salman ba."
"Ahmad nasanka dashi nidai."
"A da kenan, tunda Ahmad ya had'u da Salma ya zama Salman, ina fata kin fahimta."
"Lallaima Ahmad, to ni bansan wani Salman ba Ahmad na sani."
"Daga yau na soke Ahmad d'in Salman zaki kirani."
'yar dariya tayi "Cabb, ni Ahmad na sani kuma shi zan kira ban san wani salman ba ehe."
Ta karashe maganar harda d'an murgud'a bakinta.
Ciza lower lip dinshi yayi yana binta da kallo tallabe da hab'a fiskarshi d'auke da murmushi.
"Baka ce komai ba Ahmad."
Tuni fara'ar fiskarshi ta d'auke ,shi da yayi tsammanin ya shashantar da maganar ashe bata manta ba.
"To me kike so ince tunda rowar muryarki kike so kimin."
Marairaicewa tayi tare da cewa "Ba haka bane Ahmad ,hiran yana tsawo yana affecting karatuna, har an gane a gida bana karatu kamar da, kuma kaga ina cikin shekaran karshe ne na gamawa, ya kamata in maida hankali sosai ko dan na samu sakamako mai kyau domin cikar burina."
Tsura mata ido yayi na d'an lokaci yana nazarin kalamanta ,daga baya yace "Menene burin naki ."
"Na zama nurse of course ,naga ina taimakawa 'yan uwana da sauran al'umma idan rashin lafiya ta samesu."
"Akwai matsala ."
Yace a ranshi, dan yasan da wuya iyayenshi su amince da hakan.
"Salma me zai hana ki amince ayi aurenmu idan yaso ki kammala karatun a gidana."
Shiru tayi nad'an lokaci tana tuno maganar Nusaiba.
"Wnn idan kina gidanshi zai barki kiyi karatun ma?"
Tunowa da hakan da tayi yasa ta fara girgiza kai.
"Gaskiya Ahmad ,A'a, ka bari dai na kare karatun idan yaso ayi komai kafin na fara aiki."
Shiru yayi yana tunanin yaya danginshi zasu d'auki wnn al'amari su da sukewa karatun boko fassara ta daban musamman ga mace.
Zai jarraba sa'arsa ya gani idan har ya aureta koma me za'ayi ayi ,idan su zasu janye ra'ayinsu falillahil hamdu , idan kuma itan ce zata hakura da cikar burinta ,duk dai wnn sai ta shigo gidanshi .
*Mmn Abdul&Noorain*
[17/12 06:24] Hajara: *ππIN SO CUTANEππ*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
9.
ππππππ
*In dedication to my swt sisto Haleema Auwal (Mmn Aysha.)*
Jin shirunshi yayi yawa ne ,ya sata shiga damuwa, dan yanzu ta dad'a tabbatar da maganar nusaiba ,Ahmad baya son karatunta ,idan ta sake ta shiga gidanshi kuma tayi ban kwana da cikar burinta.
Hakan yasa ta mike a sanyaye ta mishi sallama tun bai amsa ba dan yayi nisa a tunani ,tayi gaba abinta.
Shiganta d'akinsu ta zauna ta jinginu da bango , a ranta take cewa "Lallai nusaiba ta hango mini abinda na gagara hangowa kaina, yanzu idan yace bazanyi aikin ba hakura da aikin zanyi koko dashi zan hakura.
Tana tuna yadda za ta hakura dashi taji gabanta ya bada damm, juya kanta ta shigayi ,"bazan iya ba ,duka biyu ina so."
Ta fad'a a bayyane.
Shi kuwa Ahmad kanshi ne yad'au caji, tunani yake yi lallai idan yayi sake Salma zata guje shi akan karatunta dan ya lura ba karamin kwallafa ranta tayi akai ba ,ina mafita.
Mafita d'ayace ,itace yayi wa tufkar hanci tun abu baiyyi nisa ba ,saboda haka sai ya yanke shawarar yayi abinda zuciyarshi ta raya mishi .
Zuwa yayi ya samu yayanshi ya bashi labarin ya samu yarinyar da yakeso ya aura snn yana so aje anema mishi auranta, amma bai fad'a mishi akan tana karatu.
Yayanshi yayi farin ciki kwarai ,dama burin shi kenan yaga d'an autansu ya ajiye iyali.
Saboda haka sai ya nemi sauran 'yan uwanshi ya sanar dasu snn suka sa ranar da zasu je dan su nema mishi aurenta.
Kamar yadda suka tsara ko haka sukayi , sunje nemawa Ahmad aure gidansu Salma ba tare da saninta ba ,duk da a wurinsu suna tunanin saida suka fahimci juna kafin Ahmad ya tunkare su da maganar.
Shi kuma Ahmad a tunaninshi so da yardar dake tsakaninshi da Salma bazai bari ta watsa mishi k'asa a ido ba koda za'a tambayeta ra'ayinta game da aurenshi.
Sun samu tarba ta mutunci da karamci daga wajen Mal. Inda bayan gaishe gaishe suka gabatar da bukatar su ta nenawa k'aninsu auren Salma.
Snn idan zai yiyu suna bukatar a gama komai cikin k'ankanin lokaci.
Duk da Mal.yaji mamakin abin amma bai nuna musu ko a fiska ba, ya dai ce musu zai ji ta bakin yarinya dan basu sanar dashi wani abu makamancin haka ba daga cikin gidan.
Snn bai b'oye musu ba ya sanar dasu salma tana karatu da kuma irin karatun da takeyi.
Nan suka shiga kallo kallo kowa da abinda yake sak'awa a ransa.
Sallama da godiya suka mishi suka kama hanyar komawa gida .
Ahmad da yakasa zaune ya kasa tsaye yana jira yaji irin amsar da zai samu daga garesu .
Ganin shigowarsu yasashi binsu yana musu sannu da dawowa.
Daga yanayin fiskokinsu ya gano akwai matsala.
Babu walwala a fiskar ko d'aya daga cikin su ukun.
Ganin yadda ya tasa su gaba yake binsu da kallo cikin rashin sukuni yasa babban yayansu wanda yake tare dashi ya fara magana cikin zafin rai.
"Ahmadu me ya had'a ka da 'yar boko? Wato bidi'a kakeso ka kawo mana cikin zuri'a ko? Ina kai ina auren likita ,kullum tana yawon zuwa asibiti bata da lokacin ka, duk 'yan matan garinnan ka rasa wacce zaka aura sai wacce ta tsofe tana yawon karatun boko.
Ka bani mamaki Ahmadu ,kai da kake namiji ma bakayi karatun boko mai zurfi ba sai mace?
To ba'a zuri'armu ba saidai idan zaka canza dangi, baza mu lamunci wnn aikin kafurcinba."
Ya karashe maganar yana huci.
Suko sauran 'yan uwan sai gyad'a kai sukeyi irin d'an uwansu is absolutely right d'innan.
D'ayan yayannashi ya cab'e zancen da cewa "Kasan duk dangin mu ba'a tab'a irin haka ba kuma akanka baza'a fara ba, gwara ma ka canza shawara ."
D'ayan ko da tausayin Ahmad duk yabi ya cika shi ganin yadda lokaci guda kamanninshi suka canza ,jijiyoyin kanshi suka tashi burd'um2 ,cikin sassauta murya yace.
" Nidai shawarar da zan baka ,kayi hakuri ka daure ka cire yarinyar a ranka dan kasan aurenta ba mai yiyuwa bane, ka nemi wata ka aura."
Babban yayan ya amshe da "Kada ma yayi hakuri in ya ga dama ,aurene dai bazai aureta ba, saidai in bana numfashi, idan ma aurenne akwai yanmata da yawa masu mutunci ,ko ni nan zan zab'a maka mace mai hankali nagartacciya wacce tasan darajar aure mai yawon banza ba."
Sai a snn ya samu bakin magana "Wai shin auren 'yar bokon haramunne?"
"Laa ilaaha illallahu ,muhammadarrasuulullahi salallahu alaihi wa sallam."
Suka had'a baki wajen fad'a.
Kadin d'ayan wannashi yace.
"kaga abinda muke gudu kam ko, zama da ire irensu babu abunda yake k'arawa mutum sai rashin kunya , yanzu akan auren farin kake sa' in sa damu .
Daga yanzu ma kenan inaga in ta shigo gidanka ,Kai Allah ya raba mu da auren 'yan boko, ko da yake ba laifin ka bane ,biye maka da akayi tun farko kayi karatun bokon shi ya baka damar yin abinda ranka keso."
Babban yayansu sune ya katse shi da cewa "Umaru ka daina b'ata bakinka ,ni nan zanyi maganin fitsararre ,aure zan mishi da 'yar mutunci ko yaki ko yaso, cikin kwanan nan zamuje nema mishi auren, idan ya ga dama kada ya hakura wnn matsalarshi ce."
*Mmn Abdul &Noorain*
[17/12 06:24] Hajara: *ππIN SO CUTANEππ*
*Fasaha Online writers*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal.)*
10.
ππππππ
*A friend in need is a friend indeed.*
Maryam Mazad.
*kina nan manne cikin raina a ko da yaushe.*
Tsabar bakin ciki da takaici barin gurin Ahmad yayi, danji yayi kamar ya naushi bakin yayannashi.
"Ji min mutum kamar wani ubana wai aure zaimin ,kamar wata mace."
Abinda ya fad'a kenan lokacin da fita daga gidan.
Salma kuwa tana can bata san wainar da ake toyawa ba, saida gari ya waye taje gaisheda malam yake tambayarta ko ita tace Ahmad ya turo iyayenshi.
Take taji wata muguwar fad'uwar gaba ta mata dirar mik'iya.
Dafe kirjinta tayi tana juya kai idanun ta taff kwalla, maganar ma ta gagareta.
Ganin halin da ta shiga lokaci guda yasa malam yace ta tashi taje kawai dama ya tambaya ne don yaji ta bakinta.
A sanyaye ta tashi ta tafi tana jin zuciyarta na dokawa.
A b'angaren malam kuma dama yayi tunanin bata da masaniya akan hakan dan inda ta sani ko yaya zata sanar da Ummi, saboda haka ya kudurta indai bata so ,hakuri kawai zai basu idan suka dawo.
Yaraf ta zauna a bakin gado hawaye na gangarowa daga idanunta .
Abinda Ahmad zai mata kenan, ya turo iyayenshi ba tare da izininta ba.?
Ya yakeso iyayenta su d'auki al'amarin."
Ita har kunyarsu ma ta fara ji ,gani take kamar zasu ce da saninta suka zo, ba abinda yafi damunta kamar idan ta tuna maganar da sukayi da ummi kwanaki uku da suka shige.
Lallai Ahmad ya mata bazata.
Ko me Mal. Yace musu sai Allah.
Tana cikin tunanin ta tsinkayo nusaiba na cewa "Lafiya aunty kike kuka?"
Shafo hawayen fiskarta tayi tana kallo kamar wacce taga bakon abu, ta kuma gagara yiwa Nusaiba magana.
Ganin haka yasa nusaiba fita ,tare da kiran ummi.
Tare suka shigo da Al-amin da ya shigo gaisheda Ummi ya ci karo da labarin Salma tana kuka.
"Kukan me kikeyi salma, Me ya sameki da sassafennan?"
Ummi ta tambaya tana zama kusa da ita.
"Cikin kuka tace Ummi Ahmad ya turo iyayenshi gun mal. ba tare da sanina ba."
"Au dama bake kika ce ya turo ba?"
"Ummii."
Tace da saurin baki tana zaro idanu.
"Taya zan yanke wnn hukunci ba tare da saninku ba, wlh ni ban san zai turo ba ."
Ta fad'a muryarta na rawa tare da karin hawaye akan fiskarta.
"Toh kukan me kikeyi ba kinasonshi ba ,meye dan ya turo."
Da sauri ta sake cewa "A'a ummi ban shirya ba wlh , na fad'a mishi sai na kare karatuna, Ummi yanzu me Mal. Yace musu."
"Ina zan sani ni kuma yanzu dai zasi dawo su ji amsa kuma amsar tana gareki in eh, eh in a'a kuma sai asan yadda za'ayi."
Ajiyar zuciya ta sauke tana share hawaye, tare da bin ummin dake fita da kallo.
Mayar das kallonta tayi kan su fati da nusaiba .
Suna had'a ido ta harare ta "kallon fa ?"
Dariya tayi taja hanun fati sukayi waje tana cewa "Fati mu fita kar a huce haushin lucky akanmu."
"Ina kwana ya al-amin."
Salma ta fad'a murya k'asaΒ² .
Murmushi yayi "Ummulu har an gama kukan?"
Kwafa tayi snn tace "Haushi ya bani yayanmu idan banyi kukan ba bazan ji dadai bane."
"Banda abinki meye abin kuka a ciki, dan ya turo ba sai a gama komai a jira idan kin kare karatun musha biki ba?"
"Hmm yayanmu baza ka gane bane ."
"To ganar dani"
Ya fad'a tare da zama kan katifa.
Gyara zama tayi ta zayyane mishi komai har da yadda ahmad yake basar da zancen karatunta in ta mishi.
Shiru yayi na d'an lokaci snn yace "Nidai shawarar da zan baki anan itace ,ki dage da addu'a ,ki roki Allah zab'in alkhairi , idan Ahmad alkhairi ne a gareki Allah ya tabbatar idan kuma sab'anin haka ne ,Allah ya musanya miki mafi alkhairi."
A ranta tace in Allah ya yarda ma alkhairi ne.
A fili kuma tace "Amin na gode yayanmu."
Amma kuma can k'asan ranta da gaske haushin abinda Ahmad ya mata takeji.
Hakan yasa ko da ya kirata kin d'auka tayi ,duk nacinshi haka ya hak'ura ya kyaleta.
Ko da tagama shirin makaranta ta fita ma ta ganshi sarai tayi kamar bata ganshi ba tayi saurin taran napep
ta shiga ta tafi.
Toh Ahmad ka b'allo ma kanka ruwa ,da wanne zakaji da haushin su yaya babba ko kuma fushin da Salma takeyi da kai.
*Mmn Abdul& Noorain*
[17/12 06:24] Hajara: *ππIN SO CUTANEππ*
*Fasaha Online Writers.*
*F.O.W*
*By Anty Rukie (Mmn Abduljalal)*
11.
ππππππ
*Assalamu alaikum warahmatullah.*
*Ina taya d'aukacin iyalan margayi Hamma Umar da kuma makaranta littafin rubutaccen al'amari alhinin rashin wnn bawan Allah, Allah ya ji qanshi yasa ya huta , mutuwar wnn bawan Allah ya shigeni ba kad'an ba,Allah ya bawa iyalanshi haqurin rashin da sukayi, Allah ya jiqan dukkan musulmi ,Allah yasa mu cika da imani*
Kullu nafsin za'iqatil maut.πππ
*Ina kike Mmn Ukhty (Lubabatu kyauta ) ga taki gaisuwar ta musamman.*
*Allah ya bar qauna.*πππ
WasaΒ² saida suka kwashi kwana biyu Salma tana mishi wasa da hankali ,gefe d'aya kuma yayanshi ya bud'a mishi wuta akan lallai sai ya rabu da ita ,dan yace ya nema mishi auren 'yar abokinshi kuma an bayar sbd haka ya cire hankali kan Salma ya rike wacce aka bashi hanu bibbiyu.
A rana ta uku ne tana zaune