x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 6 - MINISTER ASHRAF

  • 15001 words
  • 18000 words
  • Out of 42082 words

Category: Romance Story +18

Views 266

22 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
'kin amincewa 'kudurina kin gane? karki wani damu ina tare dake babu yadda za'ai su gane zamu had'a baki tare da Danual komai zai kasance a sirrince ina kammala aiki na zamu tattara kayan mu harke mubar Dutse ko koma state namu acan za'ai bikin auren mu ni dake" kaita d'aga masa cikin jin dad'i domin tana mutuwar sonshi amma dalilin Nabilah yasa baya bata lokaci yanzu kuma da yaga Nabilan tayi masa nisa dole ya dawo gurinta.

Nabilah kam 6uya sukai ita da Husnah sai bayan sallar la'asar suka bar school d'in sakamakon Sultan ne yazo d'aukar Nabilah tun a cikin school d'in sukai sallama tana cewa mata sai ranar biki zata zo mata fitarsu ba jimawa Husnan itama ta dau'ki motarta ta nufi gida daidai tayi parking taga Hajiya Sadiya ta fito hankali tashe ranta a 'bace hatta mayafinta yana kafad'arta bata samu nutsuwar yafawa ba da sauri ta nufi parking space idonta a rufe ko ganin Husnah batai ba wacce ta tsaya kamar sanda cike da mamaki tana binta da kallo harta bud'e mota zata shiga Husnah tace.

"Momy".

A firgice Hajiya Sadiya ta juyo tana kallon Husnah da jan idonta domin batai tunanin ita bace bataso ta dawo ta sameta bata fita a gidan ba amma hakan ma bazai hanata fita ba batai magana har Husnah ta rufe murfin motar data fito ta karaso gurin Hajiya Sadiyan ta kalleta sosai kafin tace.

"Momy meya faru ina zuwa yanzu haka magriba tayi naga ranki a 6ace"?.

Shiru Hajiya Sadiya tai ta rasa me zatace mata dan haka kawai tace "eh akwai inda zanje ba zama zanyi ba yanzu zan dawo ki kula kar kije ko'ina" ganin tana shirin shiga mota Husnah tace "Momy dan Allah karki fita yanxu Ina zakije ne a wannan daren"? Husnah ta fad'a ranta duk babu dad'i a fusace Hajiya Sadiya ta juyo tana cewa "gidan mataccen ubanki Sahah Bilal zanje yanzu kin gane inda zanje"? Karasa maganar tana kallon yadda Husnah ta zaro ido jin abinda tace ganin batai magana ba yasa taja dogon tsuka tana shiga motar da 'karfi ta rufe tare da yi mata key ta fita daga rumfar aje motocin ta nufi gate tare dayin horn me gadi ya bud'e ta fita Husnah tana tsaye tana kallo saida taga me gadin ya mayar da gate ya rufe sannan ta sauke wani irin zazzafan numfashi idonta fal da hawaye ta koma gaban motarta tana d'auko handbag d'inta ta cire key d'in motar kafin ta rufe ta shiga gidan cike da tsananin damuwa.


Hajiya Sadiya tana fita daga mopal-base government house ta nufa da mugun gudu burinta kawai ta had'u da Alhaji Ashraf ko hankalinta zai dawo jikinta tsabar tsaron dake gidansa ba'a barta ta shiga ba ba'kin ciki kamar zai kasheta gashi ta kira numbern wayarsa yafi a kirga ta'ki ya d'aga tana tsaye ta jingina a jikin motar ta kifa kanta cike da damuwa da tashin hankali zuwa bayan sallar isha kusan karfi tara taji motoci suna parking da sauri ta juya tana kallon gurin motocin gidan Alhaji Ashraf ne daidai an bud'e kofar babban gate d'in gidan sun fara shiga Hajiya Sadiya ta cije yatsa cike da takaici tasan yau ko mutuwa zatai bazai saurare taba saidai ta barwa gobe, akan idonta suka gama wucewa kafin aka mayar da gate aka rufe runtse ido tai ba zato taji hawaye yana zuba kaita jinjina tare da nufar motarta ta shiga ta koma gida a parlor ta samu Husnah ko iya shiga part d'inta batai ba tunda taga fitar Hajiya Sadiyan ganin ta shigo yasa zubur ta mi'ke tana kallon yanayin rashin walwalar dake kan fuskarta tace.

"Momy ina kika je"?.

Wani irin kallo Hajiya Sadiya tai mata jin tambayar data jefo mata batare data motsa koda lips d'inta ba kuma bata tsaya ba ta wuce part d'inta da kallo Husnah ta bita tana sau'ke ajiyar zuciya itama ta shiga nata part d'in tunda tasan ko tayi uwa yata maye ayau Hajiya Sadiya baxatai mata magana ba saidai gobe idan ta huce........✍️ AYI HA'KURI YAU TYPING D'IN BABU YAWA.


MRS ÃL'ÅMÉÉÑ ÁHMÃD CË.
Mai tambarin yma dutse new world me alfaharin jihata ce ko'ina nake inda zan zarce a cikin Nigeria muke da gada mun taka kan dutse birnin daraja daya batse ga haske🎆 ga adon Dutse 🏞️.

See you tomorrow morning.
We will meet again.
Be with me at always my lover's.


6~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Taibanah.

∆Saleem Musa Abubakar
∆Naja'at Musa Abubakar
∆Fatima Musa Abubakar
∆Aishat Musa Abubakar
∆Abubakar Musa Abubakar.


@YUSRAHMS CE.


TYPING 📲 SUN, JAN3/25 10:18pm YUSRAH MUSA ABUBAKAR.


💕MÏÑÏSTËR ÄSHRÄF💕


ÀÑÑÙRÌ WRITER'S ASSOCIATION 💫
Home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan.


WHATSAPP NO:234 816 098 3083.
Yusrahmusa65@gmail.com



STORY WRITTEN ND EDITING
By°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

YMA DUTSE NEW WORLD🌏.


📝✍️WRITER
1_Yarima abdul-maleek
2_Rayuwa biyu
3_Safreeyyah
4_D'an millionaire
5_Royalty
6_Zuciyar Aliyu ce
7_Tajuddeen Aryam
8_Me kamar sarki
9_Husnah ko Badiyat
10_Dama kece
11_Minah-Umer
And now........✍️📝minister Ashraf


7~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Abidinah.


🌺🥀🌹🏵️🌷🌸💐🌻🌹🏵️🌹🥀🌺
Bismilllahir Rahmanur Raheem.


💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦
PG____07&08
Duk yadda Hajiya Sadiya taso had'uwarta da Alhaji Ashraf bai samu ba har hanya ta nema yadda zata samu ganinsa amma bata samu tayi ba'kin ciki ta shiga damuwa har saida ta d'orawa kanta jinya ta kwanta asibiti kusan kwana goma sha biyar bata samu sau'ki ba karshe da'kyar ta samu tad'an farfad'o aka bata sallama amma tsabar karfin hali tana daga ta d'ago tana kallon Hajiya Bilkisu dake gefe tana had'a mata tea d'in da Husnah ta dafa mata cikin muryar rashin lafiya tace.

"Bilkisu dan Allah bani waya ta a cikin handbag d'ina".

Hajiya Bilkisu batai magana ba saida ta gama had'a mata ta mi'ko mata kar'ba tai tana ajewa a gefe tace tare da girgiza kai da mamaki Hajiya Bilkisu tace "haba Sadiya ya haka kuma baki da lafiya fa ki duba yadda kika koma ke bakya tsoron abinda zai faru a gaba ne taya kike tunanin zaki samu sau'ki bayan kinsa damuwa a ranki"? Yamutsa fuska Hajiya Sadiya tai tare da dafe kanta da yake sarawa numfashinta na fita da hucin zafi tace "ba wannan ne damuwa taba Bilkisu please mi'ko min wayata dan Allah kar zuciyata tayi bindiga" zaro ido Hajiya Bilkisu tai tana cewa.

"Subahanallahi bindiga kuma 'kawata me yayi zafi haka"? Ta fad'a tana karewa yanayin da Hajiya Sadiyan take kallo ganin bata ko motsa ba yasa taci gaba "kinga Hajiya Sadiya dan Allah ki kawar da wannan abu samun lafiyarki a yanxu shine damuwata indai kika mayar da hankalinki kika samu sau'ki ni Kuma nayi miki alkawarin zan taya ki mu had'a karfi da karfe mu shawo kan Alhaji Ashraf ya aureki" jin abinda Hajiya Bilkisu take fad'a yasa da sauri ta kalleta alamar da gaske kike tace "dan Allah Bilkisu bansan wasa kar kisa na saki jiki Kuma baki biya min bu'kata taba kin tabbata zaki taya ni na samo kan Alhaji Ashraf"? Kai Hajiya Bilkisu ta d'aga mata cike da 'kwarin gwiwa da son 'karfafa mata zuciya tace "kwarai Sadiya nayi miki wannan alkawarin insha Allahu zaki auri Alhaji Ashraf ki zauna dashi kuyi rayuwa kamar yadda kike fata amma zan taimake kine kawai idan naga yanzu kin d'auke hankalin ki akansa ki kama shan magani ki samu lafiya bayan kin gama warwarewa saimu d'aura d'amarar neman ta yadda za'ayi mu samu ki shawo kansa ya tattare hankalin sa da nutsuwarsa ya fuskance ki ya soki sannan ya aureki humm 'kawata bake ba koni zanso ace na samu miji irin Alhaji Ashraf na aura wazaiyi sake da irinsu banga lefin kiba kome kikai akan Alhaji Ashraf saidai na sake zugaki 'kawar kada ki sake ki rabu dashi ki kasance me dauriya da yi masa naci a koda yaushe karki gajiya domin ni nagano dalilin da yasa kike shan wuya ba komai bane bari na fad'a miki gaskiya bawai dan ya wulakanta ki ko yasa kiji babu dad'i yake yi miki haka ba a'a saboda Alhaji Ashraf har yanzu shi d'alibi ne a 6angaren soyayya baisan komai ba tunda bai ta'ba yiba amma ke kin santa kin ta'ba yi kuma kinsan dad'inta to kamata yayi kiyi amfani da 'kwarewarki ki nuna masa hanya ki koyar dashi yadda zai koyi sonki ta ruwa sanyi cikin batare da kin furta masa kalmar so ba nina fad'a miki kina zaune zaki ganshi yazo miki har gida sannan ya nemi alfarmar ki ya furta miki so ya 'kas'kantar dakai ya baki ha'kurin Abubuwan da suka faru 'karshen wasan ya aureki shikenan fa burinki ya cika batare da 6acin rai ko hayaniya ba har aji kanku haba Sadi wise kamar mara wayo ya akai kofar tunanin ki ta toshe ne"? Hajiya Bilkisu ta karasa maganar tana kallon yadda lokaci guda Hajiya Sadiyan ta tashi zaune da kanta daga kawancen da take kamar ba me jinya ba haka ta ware har saida ta baiwa Hajiya Bilkisu mamaki ganin ta dau'ki kofin tea d'in ta fara shayasa ta bud'e cooler tana had'a mata abinci kafin ta gama, maimakon ta sauke kofin sai taga ta qara mi'ka mata tana cewa.

"Zuba min wani".

Murmushi Hajiya Bilkisu tai cike da jin dad'i da mamakin ganin yadda ta wartsake kamar me ciwon 'karya kafin ta kar'bi kofin ta sake zuba mata wani ta bata shima bata rage ba sai kofin ta dire sannan taja plate d'in abinci gabanta shima tad'an ci ba lefi kafin ta yagi tissue ta goge bakinta tare ta rufe ido ta bud'e had'e da sauke ajiyar zuciya tana kallon Hajiya Bilkisu tace.

"Na gode sosai 'kawata tabbas ke aminiya ta gari ce wacce mutum zai dau'ki dukkan yardarsa ya baki wallahi kafin kiyi min wannan maganar jikina a mace yake fiye da yadda kike tunani ko tashi bana jin zan iya yi amma ki duba kina fad'a min magana me dad'i wacce idan nabi zan samu abinda nake so cikin sau'ki lokaci guda naji wani irin 'karfi yana tunkaro ni tabbas ke amana ce Bilkisu duk ranar da nayi rashinki a rayuwa nayi babbar asara, insha Allahu abinda kika fad'a min dashi zanyi amfani naga cewa na juyo da hankalin Alhaji Ashraf kaina domin harga Allah ina son sa kuma har cikin zuciyata badan kud'in sa ko mu'kamin saba a'a nidai kawai nayi nisa idona ya riga ya rufe akansa tun ranar dana fara had'uwa dashi ban sake samun sukuni da kwanciyar hankali ba saboda jarabtuwa da sonsa daya same ni, amma shi sam baya gani meyasa Bilkisu ki fad'a min ko akwai wata da zanbi"?.

Gyara zama Hajiya Bilkisu tai tana cewa "akwai dalili shi baisan meye soba baisan ya yakeba bai ta'ba yiba sannan rana tsaka kice dole saiya soki kin ta'ba ganin inda malami bai koyawa d'alibi karatu ba kuma ya ri'ka tilasta shi akan dole sai yayi karatun zai yuwu"?.

Kai Hajiya Sadiya ta girgiza jiki a sanyaye tace "gaskiya bazai ta'ba yuwuwa ba taya ba'a koya maka ba sannan ace dole saikayi hakan da kamar wuya akwai 'kamshin 'yar damuwa a lamarin amma yanzu dai na fahimta inda matsalar take daga nine kuma zan gyara zan tsaya tsayin daka na ri'ka shawo kansa ina bashi kulawa ta masa magana me dad'i ina 'kan-'kan da kaina daga haka idan naga na samu kar6uwa sai nayi amfani da wannan damar na fara bayyana masa abinda nake so na nuna masa a zahirance aurensa nake so da burin yi indai nabi hanyoyin da kika fad'a min na tabbata zan dace zan riski nasara zan kai matakin da nake son zuwa".

Kai Hajiya Bilkisu ta jinjina tana cewa "Kwarai Hajiya Sadiya zaki kai labari na tabbata zaki nasara indai kikai amfani da shawarar dana baki".

"Ok shikenan Bilkisu na gode lallai kece irin 'kawar daya dace ayi 'kawance da ita bari nayi wanka yanzu ko jikina zai qarasa warwarewa ina zuwa" mi'kewa tai tana hawa stairs yayin da Hajiya Bilkisu ta sake sabon zama tana aje mayafinta itama ta d'ebi abinci ta d'auko drink sannan ta dawo ta zauna, duk abinda suke fad'a da irin hirar da suke Husnah tana sauraron su hankalin ta ya tashi da jin abinda Hajiya Sadiyan take so waye kumà Alhaji Ashraf a ina yake meyasa Hajiya Sadiya duk shawarar da aka bata bazata tsaya tayi nazari akai ba? dafe kai tayi tare da fad'in innalillahi wa Inna ilaihi raji'un Allah ka ganar da bayin nan naka kasa su dawo kan hanya Momy meyasa zaki min haka meyasa bazaki fuskance niba ki kankaro min martaba ta taya za'ai wanda yake sona da aure zai ganni da daraja wash Allah" ta fad'a tana sake dafe saitin inda zuciyarta take bugawa jikinta a sanyaye sosai ta juya tana komawa bedroom ta rasa me yake mata dad'i tayi nan tayi can karshe sai ji tayi hawaye yana zuba mata a ido kawai ta fad'a kan bed tana ruf da ciki ta soma kuka ko zuciyarta zata samu sassauci da sanyi daga zafin ba'kin ciki da 6acin ran da Hajiya Sadiya take jefata.


GIDAN ALHAJI MUKHTAR
Zaune Hajiya Salmah take ta cika tayi dam kamar ta fashe yayin da wasu mata su hud'u suke bubbud'e akwatunan da suke gabanta sunata sam barka babu wanda ya lura da yanayin ta daidai wata mata ta bud'o kofa ta shigo da sallama ganin abinda yake faruwa yasa ta tsaya durus tare da kallon Hajiya Salmah wacce ta kusa yin bindiga tace.

"Tofa wannan kuma daga ina ko lefen Rasheedat ne aka kawo kuma ko a gayyato mu musa albarka gaskiya Hajiya Salmah baki min daidai ba"? Ta karasa maganar tana shigowa kallonsu tai duk babu wacce ta sani da ido taiwa Hajiya Salmah magana mi'kewa tai suna shiga part d'inta cikin za'kuwa Hajiya Suwaiba tace.

"Me yake faruwa ne Hajiya naga wadancan matan suna duba kaya kuma ke kina zaune kin saka su gaba kina cin magani lafiya dai"? Cije baki Hajiya Salmah tai cike da takaici tace "hummm Ina lafiya Suwaiba Sultan ya gama mugun raina min hankali wai kayan lefe yake had'awa a part d'insa amma bai ta'ba nuna min ba ya had'e kai da ubansa suna komai tare sai d'azu kawai ina zaune kamar a mafarki naga wadancan matsiyar 'yan uwan nasu sun zo shi kuma Alhaji ko kunya baiji ba shine me d'auko akwati daga bedroom d'in Sultan yana kawo musu wai na tambaya daga Ina zuwa ina kinsan me yace" ta fad'a tana goge idonta da yake neman cika da hawaye kafin taja wani irin mugun tsakin tsanar da taiwa Nabilah da mahaifiyar ta tace amsar daya bani wai "lefen Sultan za'a kai gidansu wancan tsinanniyar yarinyar Nabilah kuma kona shirya ko ban shirya ba d'aurin aure ranar juma'a ta sama babu fashi kiji wata masifa da yake neman d'ora min".

Zaro ido waje Hajiya Suwaiba tai tana cewa "auren Sultan kuma? Nima fa abinda ya kawo ni gurin ki kenan da kikace kina so ya auri Hajeer shine nazo muyi magana sai kuma na samu wannan tsiyar yanzu ya za'ai kenan"?.

"Humm ya za'ai kuwa ni yanzu ban isa hana Alhaji abinda yayi niyya ba saidai wallahi bazan kalli wannan yarinyar matsayin surukata matar d'ana ba bana sonta dole ya qara aure ko yana so ko baya wallahi tallahi saiya auri wacce nake so saidai akan haka ko mene zai faru ya faru".

Kai Hajiya Suwaiba ta jinjina cikin zuga da son zuciyar aso 'yarta a aureta dan su samu dukiya tace "kwarai Hajiya karki ta'ba yarda da wannan lamarin tabd'ijan to bari kiji kwanan baya da idona naga yarinyar da Sultan d'in zai aura wani murgujejen Alhaji ba'ki mummuna me jan ido ya sauketa a mota sun shiga hotel tare hannunsu ri'ke dana juna da nazo gida ina jimami a lokacin Hajeer ta dawo daga islamiyya nake fad'a sai tace ai wannan 'karami na gani bansan komai ba har video akai mata ba kaya ana d'orawa a internet tsakani da Allah zan fad'a miki gaskiya Sultan bai dace da yarinyar nan ba domin muguwar 'yar iska ce mutum indai namiji ne babu kalar wanda bata mu'amala dashi a gari duk ansan da haka saboda ku kun dangance su kuma ana ganin d'anku ne zai aureta shiyasa ake 6oye muku amma ance har asibiti take zuwa wannan yarinyar anayi mata d'inki tana zubar da ciki".

Dafe 'kirji Hajiya Salmah tai tana cewa "dan Allah da gaske kike Suwaiba? Na shiga uku aiko wallahi Sultan bazai auri Nabilah koda ace nima zanyi asarar nawa auren saina wargaje bikin nan bari naje gurin wadancan matsiyatan suma su tashi su barmin gida na rantse da Allah bazasu kai wadancan akwatunan ba tashi muje" mi'kewa sukai suna fita daidai sun gama gyara komai suna shirin fita Hajiya Salmah ta dakatar dasu.

"Tsaya Labara ku dawo da akwatunan nan baza akai suba".

Da mamaki Labara tace "akan wanne dalili ne baza akai ba"? A masife Hajiya Salmah tace "akan haka nayi ra'ayi ina wanda zaku kaiwa d'ana ne nice nake da iko dashi to na hana zaku iya aje min ku bar min gida kin gane"? Da sabon mamaki Labara tace "mu aje mu bar miki gida saboda gidan kine"?.

"Kwarai baki 'karya ba gida nane tunda gidan mijina da 'ya'ya ne dan Alhaji yana d'an uwanki baki Isa kice zaki min gadara ba domin nike da iko da komai nasa baki da wani hakki akansa.

D'aga mata hannu Laraba tai tana cewa "kinga Salmah ki iya bakin ki a kaina kin gane ked'in banza ked'in wofi shashashar banza bulkumar asara uban waye yake miki gadara da dukiya ke kud'i na dama alhamdulillah masha Allah ubangiji ya bamu babu abinda zamu zo gurin wani so'ko'ko mu tambaya balle ayi mana gori da haka ki kama kanki kar kiga gidanki nazo kice zaki kawo min raini wallahi tallahi saina baki mamaki na nuna miki isar 'yar uwa tafi ta mace idan shekara d'ari kikai tare da Mukhtar kece kika haifa masa duniya daga ranar da yace kije ya sake ki dole kibar gidan nan niko Ina da gurin zama ko yanzu nazo gidan nan Kuma kedai banza a banza baki Isa kiyi komai akai ba".

Tada jijiyar wuya Hajiya Salmah tai tana cewa "a'a ki iya bakin ki wallahi kada ki kuskura ki fad'a min magana yanzu za'ai d'an karamin ya'ki a gidan nan dan
End Ads