x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 13 - MINISTER ASHRAF

  • 36001 words
  • 39000 words
  • Out of 42082 words

Category: Romance Story +18

Views 264

22 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
iya d'aukar wannan al'amarin ba gashi ya zama dole a fad'a mata din nikam wannan abun bansan ta yadda zamu 6ullo masa ba".

Batare da Alhaji Tajuddeen ya d'ago ba ya sauke ajiyar zuciya yana d'an girgiza kai yace "na sani amma fad'a Mata din shine mafita koba komai yanxu tasan da maganar hakan zai bata damar samun lokaci ta zauna tayi tunani nasan abun yazo mata banbarakwai musamman da taji Ashraf ne da kansa yake sonta yake neman soyayyarta yana matsayin abokina ni kaina bansan yaushe ya fara sonta ko yake dakon sonta ba amma a yanayin sa lokacin da suke maganar ya nuna kamar ya dad'e yana sonta kawai dai yana dannewa ne ke kanki kinsan waye Ashraf kinsan halinsa basai nayi miki tuni ba kawai dai damuwar anan shine tare muka taso dashi abokina ne Nabilah kallon uba take masa a gareta bata ta'ba tunani irin haka zata faru a tsakanin su ba amma fad'a mata da nayi yanzu ta sani sannan zan bata lokaci ta zauna tayi tunani nikam maganar Allah bazan iya hana Ashraf auren Nabilah ba babu abinda zai nema a gurina ban bashi ba saidai idan yafi karfina kinga ko ina da iko akan Nabilah 'yata ce ke kuma kece mahaifiyar ta a koda yaushe kuna tare saiki rika tambayarta mene a zuciyarta zuwa nan da wata d'aya muga meye abinda zai faru".

Kai Hajiya Fatima ta jinjina tana cewa "to Alhaji ba damuwa Allah ya za'ba mana abinda yafi alkhairi agare mu da ita idan daga Allah ne ita matarsa ce bamu da ja idan kuma ba matarsa bace Allah ya sassauta abun ta ruwan sanyi tunda dan yana abokin ka ba haram bane dan ka haifi 'ya ya aura" kai Alhaji Tajuddeen ya jinjina yana cewa "Nima haka na gani Ashraf babu abinda zai nema a gurina ban bashi ba na fad'a na qara wallahi Fatima ko banida dashi zanyi iya kokarina saina samo masa balle Ina da damar bashi abinda ya nema a gurina Kuma insha Allahu wannan al'amarin saiya zama alkhairi gare mu".

"Haka ne insha Allahu zamuyi addu'a mu nemi za'bin Allah akan hakan maybe rabonsa ce shiyasa saida ya rage saura kwanaki kad'an wannan damuwar ta shigo Sultan ya'ki fahimta ya ha'kura da ba matarsa bace kila rabon Alhaji Ashraf d'in ce shiyasa kaga haka ta faru harya sameka ya furta abinda dake ransa".

"Kwarai haka ne Allah ya za'ba mana abinda zai zama alkhairi a rayuwar mu".

"Amin ya rabb"..............

........✍️Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë


See you tomorrow morning
We will meet again
Be with me at always my lover's.


Tnks for ur supports 🔥 nagode sosai masoya godiya sosai sosai godiya 🌺 ana tare insha Allahu.

Mu tsaya mu kwana anan sai ubangiji ya kaimi gobe darai da lafiya zamu d'ora inda muka tsaya.


YMA DUTSE NEW WORLD 🌏
🌳 🌲 🌴 🌳 🌲 🌴 🌳 🌲 🌴


TYPING📲 Wed, Jan7/25 10:25PM YUSRAH MUSA ABUBAKAR ✨✨.


💕Minister Ashraf💕

WhatsApp no:+234 816 098 3083
yusrahmusa65@gmail.com

_________________
__________________________
___________________________________

A*°•W*°•*A
ANNURI WRITER'S ASSOCIATION 💫 home of hospitality and harmony gidan kar'bar mutane hannu biyu da zaman lafiya ÀÑÑÙRÌ haske le'ka gidan kowa koda ma'kiya na kallon ka ramin kura sai'ya'yan ta haka taken mu yake tafiyar mu babu rago a cikin ta babu yaudara da ha'inci tsantsan gaskiya muke nunawa.


In the name of Allah the must benefits and the must merciful ALLAH THE MOST HIGH DOESN'T SLEEP ALLAH THE MOST HIGH IS PURE HE ACCEPT ONLY WHAT IS PURE we love our NABI MUHAMMAD SAW no success without him he's the light of every darkness he's the answer to every question he've no limits ya rasulullah muna sonka fiye darai da iyaye da dukiya muna sonka fiye da dukka muradi na zuciya ANNABI mu mu ganka shine buri na zuciya lamince mu ganka ya mai salsabil da khausara.


Official

By
°• °• °• °•©•° •° •° •°


STORY WRITTEN ND EDITING
✍️YUSRAH MUSA ABUBAKAR
Mrs Äl'ämëëñ Ähmäd çë.


°•°•°•°•°•°•°
°••°••°••°••°••°••°••°••°
°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•°•

15~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Mustagfirinah.


💦Yüsëëñ Sïr Äl-ämëëñ çë💦
PG______17&18
Sultan ne zaune a gaban Alhaji Mukhtar yana fad'a masa cewa aje masa ro'kon arziki ga wacce yake so domin har yaje gurin ta sun gama daidaitawa shiyasa yazo ya fad'a masa, kallonsa Alhaji Mukhtar yayi da mamaki wato dai bazai sauko yayi ha'kuri ya auri Nabilah ba bayan an gano gaskiya humm ba damuwa yasan da had'in bakin Hajiya Salmah zai rabu dasu ya xuba musu ido suyi gaban kansu amma ko menene ya biyo baya bazaice 'kala ba kaiya jinjina yana kallon Sultan a karo na biyu wanda shi kuma a nasa 6angaren ya mugun had'e rai sakamakon jin Alhaji Mukhtar ya'ki ya furta koda ah ce akan lamarin kodai bazai amince ya aureta ba aiko wallahi indai bai bari ya auri Hajeer ba tofa ko zai kashe shi ko yace su raba hanya bazai auri Nabilah ba saidai ya zauna iya tsawon rayuwar sa baiyi aure ba.................

"Abdul-azeez".

Yaji muryar Alhaji Mukhtar kamar bazai amsa ba saboda baisan mr zaice masa ba sai kuma ya tuna cewa koma mene mahaifin sa ne saida yardarsa zai samu sau'ki a rayuwa sa dan haka da'kyar kamar me ciwon baki yace.

"Na'am".

"A Ina yarinyar take"?.

"A limawa".

"Limawa kuma? Acan take 'yar waye ita a anguwar"?.

"Bansan sunan mahaifin taba saboda bata ta'ba fad'a min ba amma dai nasan mahaifiyar ta 'kawar Umma ce".

Jin abinda yace yasa Alhaji Mukhtar jinjina kai wato 'yar 'kawar Hajiya Salmah ce ko ba'a fad'a ba yasan wannan neman auren umarnin tane humm babu komai bari ya zuba musu ido....

"Ina jinka yanzu me kake so ayi maka"?.

"Abba mahaifan tane suka ce nakai ro'kon arziki idan da gaske nake yi ni kuma da gaske auren ta zanyi".

"Auren ta zakayi kuma Nabilan a wanne matsayi take yanzu ko mata biyu zaka aura rana d'aya"?.

Kai Sultan ya girgiza yana cewa "a'a nifa bazan auri Nabilah ba na fasa da ita na ha'kura bazan iya zama da ita ba domin bata dace da irin rayuwata ba".

Jin abunda yake cewa yasa ran Alhaji Mukhtar ya 6aci cikin fad'a ya fad'a magana "wato Sultan har yanzu baka sauka ka ha'kura ba ko Nabilan ce bata dace da tsarin rayuwar kaba kuma tsabar sakarci har kake fad'a min sabida rashin kunya Sultan kome zakace Nabilah 'yar uwarka ce kuma hannunka baya ru6ewa ka yanke ka jefar kai kuma naga take-taken ka kenan ashe har yau kallon 'yar iska kake mata wacce ta xubar da mutuncinta bayan gaskiya ta bayyana ba ita bace sharri ne fuskarta kawai wata arniya tai amfani dashi kasan da haka amma tsabar rashin hankali da rashin sanin ya kamata kaine me bud'e baki kana cewa wai Nabilah ya zubar da mutuncinta a gidan ubanwa ka ta'ba ganinta da zakai mata wannan shedar"? Ya karasa maganar a fusace yana kallon sa shiru Sultan yayi bai iya koda tari ba Alhaji Mukhtar yaci gaba.

"Kasan Allah Sultan ka kiyaye ni bana son shashanci wato ka biyewa mahaifiyar ka tana d'ora ka akan hanyar keken 6era ko? Zakai dana sani a gaba ina fad'a maka ka gane ka gyara tun kafin lokaci ya qure maka abu na karshe indai bazaka had'asu su buyun ka aura ba tofa wancan auren naka ma ban goyi bayan kayi ba ka gane? Tashi ka bani gu" Alhaji Mukhtar ya karasa maganar yana nuna masa kofar fita mi'kewa Sultan yayi ya fice ransa a mugun 'bace da kallon Alhaji Mukhtar ya bishi cike da mamakin yadda yayi watsi da tarbiyyar daya bashi wato yayi masa magana amma ya kasa buda baki ya bashi ha'kuri tsabar lalacewa kaiya girgiza cike da takaici ya mi'ke shima ya fita.

Kai tsaye bayan fitar Sultan gurin Hajiya Salmah ya wuce kamar zaiyi bindiga tsabar fushin daya d'auko Hajiya Salmah na ganinsa tasan ba lafiya ba da sauri ta tareshi tana cewa "Sultan lafiya meya faru"? Huce yake fitarwa kamar irin wanda yayi gudun nan sosai yana hura hanci da muzurai yace "Umma gaskiya Abba baya sona ya daina anya ma ni d'ansa ne naga bambancin da yake nuna min yayi yawa".

"Me yace maka wanne bambanci ya nuna maka baka fad'a masa abinda nace maka bane"?.

"Na fad'a masa man akan haka ya tozarta ni harda cemin shashasha wanda baisan ciwon kansa ba akan yace ya batuna da Nabilah nace masa nifa har yanzu Ina nan akan bakata bazan auri 'yar iska shine yace indai bazan had'asu biyu na aura ba wai Hajeer d'in ma ban isa na aure taba bai amince min".

Sultan yana rufe baki Hajiya Salmah ta zabura tana mi'kewa tsaye tace "meee bazaka aure taba saboda shine ya haife ka yake da iko akanka zaisa dole kayi abinda zai cutar dakai wallahi tallahi bazaka auri Nabilah ba Hajeer zaka aura zanje yanzu zanyi magana da Yaya Auwal yaje maka dad'in abun ma ina da yan uwan maza wanda zasu wuce min gaba ayi maka komai karka damu Hajeer kamar ka aure tane kabar min komai a hannuna tunda yace haka nasan komai zakai bazai je maka ro'kon arziki ita Kuma Nabilan bari naje gidan yanzu naci uwarta Fatima sai sun yabawa aya za'kin ta ai nasan da had'in bakinsu ake so a da'kile maka rayuwa a cuceka a aura maka karuwa wacce ta tsiyayar da mutumcinta a gurin maza humm to wallahi uban kuturu ma yayi kad'an ballantana na makaho dani suke zancen matsiyatan mutane bari na fito" tana fad'in haka ta shiga bedroom tana d'auko mayafi da key d'in motarta ta kalli Sultan da yake tsaye tun sanda yazo bai samu ya zauna ba tace.

"Kaje kayi tafiyarka hospital karka damu kanka akan abinda Alhaji yace shima ina daidai dashi tunda yunzu ba aurensa ne a kaina ba balle yace zai min wata magana ko ya nuna ikonsa na miji a kaina" gaba tayi yabi bayanta suka fita tare me gadi taiwa magana cewa zata fita duk wanda yazo nemanta karya bari ya shiga mata gida ko waye sai idan ta dawo sannan ta fita Sultan dama yana fitowa ya shiga motarsa ya fita bai tsaya ba.

A kofar gidan ta aje motarta ta shiga cikin gidan me gadi ya ganta har gaida ita yayi tunda yasan wace ita matar 'kanin mai gidan ce da sauri ta shiga parlor ko sallama babu ta fad'a musu domin ba arziki ne ya kawota ba Hajiya Fatima tana zaune tare da wata 'yar uwarta da tazo mata ziyara sai Nabilah suna zance kawai ba zato sai ganin mace sukai ta shigo wuff kamar wani ne ya hankad'o ta sai huci take da mamaki duk su ukun suka bita da kallo amma babu wanda yace 'kala tunda suka ga yanayin ta sunsan ba alkhairi ya kawota ba................

Kan Hajiya Fatima Hajiya Salmah taxo ta tsaye kamar zata rufeta da duka tacd "Fatima Fatima Fatima sau nawa na kira sunanki? Sau uku ba wani abu ya kawo ni gurin ki ba karkiyi tunani na sauko Sultan ya aure tantiriyar 'yarki ne hum'um Allah ya sauwake masa auren ballagaza ni nazo ne akan nayi miki gargad'i da babbar murya Nabilah ta fita hanyar Sultan domin yafi karfin auren irinta wato keda mijinki kunje kun kwarkwance Alhaji saboda ba'kin cikin kunji Sultan ya samu matar aure nutsattsiya saida kukai kutun-kutun d'in daya ce bai amince ba saidai ya had'asu biyu ya aura ko? Tabd'ijan heyyy aiko wallhi baku isa ba na rantse da Allah Sultan bazai ta'ba auren wannan karuwar 'yar taki ba taje taci gaba da baiwa mazan jikin nata amma dai ba Sultan ba gara da Allah ya tona mata asiri tun wuri muka gane 'yar iska ce to karshen iskanci ya qare na fad'a muku ku janye idanuwan ku daga kan Sultan ko ku mayu ne kurwarsa tafi karfin ku tirrr da hali irin naki wallahi Nabilah kinyi asara kin bada mata" ta karasa maganar tana tsartar musu da yawu akan carpet cike da wulakanci.

Kallonta Hajiya Fatima tai tana jinjina kai mamaki ya gama cikata itafa harta manta da wani auren da akace da za'ai da Nabilah da Sultan balle wata banza a banza Hajiya Salmah ai ko bata fad'a ba wallahi itama abinda ke ranta ciwon da Sultan ya sawa Nabilah bataga wanda zaizo ya bata ha'kuri ta yarda Nabilah ta auri Sultan ba.............

Katse mata tunani muryar Hajiya Basirah tai jin tace "haba ke kuwa baiwa Allah wanne irin abu ne wannan kizowa mutum har gida kina ci masa mutunci gaskiya wannan ba d'abi'a ce me kyau ba ki gyara".

Wani irin banzan kallo Hajiya Salmah taiwa Hajiya Basirah tana cewa "ke Kuma sokuwa daga Ina waye ya sako dake kinga da wacce nakeyi ki bari ta iya maida min martani idan ta isa amma bake karan kad'a miya ba".

Kai Hajiya Basirah ta jinjina tana cewa "Ai tunda kikai da ita kinyi dani".

Cikin rainin wayo Hajiya Salmah tace "Au haba sannu uwar kinibibi sabida neman isim ba kamun ra'asu yasa idan nayi da ita nayi dake ko? To bari kiji karki kuskura ki shiga abinda babu ruwanki wannan fad'a ne tsakani na da ita dan haka ki rufe min baki kin gane"?.

"Ban gane ba kimin yaren dazan gane shin waima tsaya na tambaye ki da wanne irin harshe kike magana hausa ce ko fullanci dan bana fahimtar abinda kike fad'a d'an sake maimaitawa kikace mee"? Hajiya Basirah ta karasa maganar cikin son 'kular da ita harda juyo mana da kunne alamar tana jiran amsa a fusace Hajiya Salmah ta bud'a baki zatai magana ranta a 'bace Hajiya Fatima da abun ya gama isarta tace.

"Kinga dan Allah kubar wannan abun Hajiya Salmah kiyi hakuri maganar da kike indai aure ne tsakanin Sultan da Nabilah babu shi anbar shafin babu abinda Nabilah zataje tayi a gidan Sultan yanzu saidai suyi zumunci amma ba soyayya ba balle aure nima na haramta mata auren naki d'an ko ba Sultan ba har abada shikenan an wuce wajen saidai idan kuma wani abu dabam kike nema a gurina".

Cike da masifa Hajiya Salmah tace "eh wani abu nake nema Ke dama yau saida na shawo bala'i Ina neman fitina sannan nazo gurinki idan ma asiri kaikawa Alhaji ya nace sai karuwar 'yarki tun wuri kije gurin malamin naki ya warware domin baiyi tasiri akaina da Sultan ba wallahi tallahi Nabilah ko mutuwa zatai sultan yafi karfin auren yar iska ma'abociyar bin maza irint...............

D'aga mata hannu Hajiya Basirah tai tana cewa "Ke dakata banza kazamar mata wacce batasan me take ba karya kawai uban meye a jikin jaki d'an naki da har Nabilah zata so wallahi itama a yanxu tafi karfin auren d'an jagaliya irinsa tayi masa nisa tsakanin su saidai hangen nesa uban me kike takama dashi waye ya tsaya miki? Tun wuri ki iya bakin ki kafin na saita miki 'kwa'kwalwa".

Hajiya Basirah tana rufe baki ba zato taji Hajiya Salmah ta dam'ki hijab din'ta tana cewa "Ke wai da kike fad'a min magana son ranki 'yar uban waye ke waye ubanki a cikin garin nan nuna min sh.........................

Tana rufe baki Hajiya Basirah ta d'auketa da zazzafan mari tare da murd'e mata hannu ta kwace ri'kon da taiwa hijab din'ta har tasa gurin ya fara squeezing.

"Kan bala'i ni kika mara"?.

"Am mareki d'in ki rama idan kina ganin zaki iya".

A fusace Hajiya Salmah ta kalli Hajiya Fatima wacce ke zaune ta d'ora kafa d'aya kan d'aya ta d'auke Kai kamar batasan me ake ba tace "kina kallo ai ta mareni ko? Bakice komai ba saboda ke ba'kar tsohuwar munafika ce to wallahi bari kiji" ta fad'a tana mayar da hankalinta kan Hajiya Basirah taci gaba "kinyi da 'yar halak kin mari masifa da bala'i kin mararwa kanki damuwa da tashin hankali ni ba'a biyu dani zakiga abinda zai biyo baya sai kinyi nadamar zuwanki duniya Kuma zaki gani".

"Naga alkhairi babu abinda kika isa kiyi min wanda Allah bai minba jakar banza dakikiya wacce bata da tarbiyya bata jan girmanta a gaban 'yar cikin ki kinxo kinata d'aga harshe kina zubar da ajinki wawuya".

"Ki dakata malama kada ki sake zagina kin gane"?.

Tsaki Hajiya Basirah tai tana binta da wani irin kallo tace "ban gane ko zaki ganar dani"?.

Kai Hajiya Salmah ta jinjina ranta in yayi dubu ya 6aci tace "na rantse da Allah daga shi babu wani wallahi saikin gwammace mutuwarki akan rayuwa zaki ga abinda zai biyo baya ki jira ni" tana fad'in haka fuuuuuu ta juya ta fice.

Kowama Hajiya Basirah tai tana zama tare da kallon Hajiya Fatima tace "wai Fatima dama haka wannan matar 'kanwar mijin naki take amma da kike Shirin d'aukar 'ya ki baiwa d'anta bayan bata sonki bata son 'yar hum'um gara da akai a gabana na gani wallahi da ace har yanxu ba'a fasa auren nan ba saina hana ba gara nasa Amaan ya aure ta ba amma ked'in da a hakan zaki gangancin daukar ta kikai wannan ai kasheta zatai".

Sauke ajiyar zuciya Hajiya Fatima tai tana d'an sakin murmushi tare da girgiza kai tace "humm Basirah kenan kedai kawai Allah ya rufa asiri shine abinda zance ita Kuma Nabilah Allah yai mata canji da mafi alkairi".

"To amin Allah ya bata nagari bari na tashi na tafi kinga lokaci yana neman ja sosai karfe daya da rabi gashi ina so zanje gurin Hajiya babba daga nan" mi'kewa sukai tare Hajiya Fatima tayi mata rakiya har waje kafin ta dawo parlon har lokacin Nabilah tana zaune da waya a hannunta amma kamar bata gurin tafiyar Hajiya Basirah da kamar awa d'aya mata kusan bakwai suka bankad'o kofar parlon ko sallama babu suna cewa.

"Tana Ina 'yar uban waye ita wallahi yau sai mun 6a66alla Mata ga6o6i da duka".

Da mamaki Hajiya Fatima ta d'ago tana kallon su 'kawayen Hajiya Salmah ne harda masu shaye-shaye domin ga alama nan ta gani kaita girgiza tana kallon Hajiya Salmah wacce ke hura hanci tace "Fatima bani akwatunan Sultan daya kawo gidan nan" humm dama Hajiya Fatima tasan za'ai haka tun wuri tace a mayar domin ko son ganin kayan batai amma Alhaji Mukhtar yace babu inda kaya zai koma koda ace Sultan bazai auri Nabilah ba bai isa a mayar masa ba saidai ya had'a wani lefen amma tunda yanzu Mai karba tazo masha Allah gasu".

"Fatima
End Ads