x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 1 - HANYAR RUWA COMPLETE

  • 1 words
  • 3000 words
  • Out of 25515 words

Category: Romance Story +18

Views 180

09 Jun 2025
Start ads
After Image Ads
⚖️ 💧HANYAR RUWA💧⚖️
💦The way of water 💦






Together 💪
BY


'KANWAR SOJA


RUMMY'N ROYAL


ZAHRA ROYAL ,


A heart toching story 💔 say NO to rape❌







In the name of Allah the Beneficent the Merciful




_After the successful of (MAI CIKI CE &. RABI DANJA ) & ( FANSAA ), now we are back with ( HANYAR RUWA )_






🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, fad'akarwa, ilimantarwa da kuma nishad'antarwa_*
_(R.S.W.A)Ruwa kad'ai ke maganin k'ishi_


*Alk'alaminmu 'yancinmu*





Page _1️⃣


SADAUKARWA


Wanan littafin sadaukarwa ce ga fittaciyyar ƙunƙiyar nan ta haziƙan marubuta , jajirtattu , ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION, muna farin cikin murnar zagayowar ranar samun wanan ƙunƙiyar shekaru biyu , Allah ya ƙara mata ƙarfi da darajar ta a idon Duniya up up up 🔥 ROYAL.











Ina mai rok'on ALLAH subhanahu wata a'la kamar yanda ya bamu iko da damar farawa lafiya yasa mu gama lapiya, ya kawar da idon shaid'anu akan mu,ALLAH yasa mu amfana da abunda muka zo dashi.








Kano






Alhaji BELLOH RABE mazaunin garin Kano state a can gabashin 'kauyen Bichi, wani shahararren mayaudarin mutum ne mai taurin zuciya da saurin fusata, wanda ya kasance mai mugayen halaye ƙwatar filayen bayin Allah da gonarsu, kota halin 'ka'ka ne zai kwace musu da 'karfi da tsiya , mahaifin sa Malam Rabe ya kasance mutum da ake girmamawa a cikin wannan 'kauyen nasu ,ya kasance mai jan sallah masallacin su ,wanda mutane sukai amanna dashi gun riƙo da al'kawari da amana har suka fara mayar dashi tamkar mai gari , a kwana a tashi kuwa haka ya kasance sai da aka bashi wannan sarautar ta mai gari duk wani harkar filli da gona yana hannun sa ,sai dai duk kyawun halinsa Allah kan jarabci bawa ta hanya daban- daban ,hakan ta faru ne ta hanyar jarabtar imanin Malam Rabe ta hanyar bashi wani fitinannan Yaro mara jin magana wato BELLOH ,

















Tun ranar da aka ce Malam Rabe ya koma ga Allah ma'ana Allah ya mai rasuwa Alhaji BELLOH ya kwashi duk dukiyarsa da nashi da wanda ba nashi ba ya koma cikin gari da zama , hankalin mutane ya tashi matukar gaske ganin yanda lokacin ɗaya BELLOH ya kwashe dukiyar su a sannu a hankali a ka bishi birni sai dai abin mamaki ba da gaban ba yana ganin su yasa aka kawo musu jami'an tsaron cewa sharri da 'kazafi zasu mai, hakan yasa suka koma ƙauyen Bichi da baƙinciki, sanadiyar wannan al'amarin wasu sun mutu da takaicin da tsinewa Alhaji BELLOH.....














Alhaji BELLOH matar shi d'aya tak a duniya wacce sukai auren lalle tun suna yarintar su a gaban iyayensu har takaika duk sun rasu sun barsu , Hajiya Lubabatu da Alhaji BELLOH Allah bai azurta su da yara masu yawa ba yaro d'aya tak suke dashi mai suna Muhammad (Faisal) BELLOH,,,,,,,,




Suna zama cikin zaman lafiya da wadatar zuci duk wata shiga da fita idan ya cutar da bayin Allah sai ya bi court da doka ya saye su kaf, talakawa na kai yawan kukan su akan hukuma amman a banza sai a kore 'karar domin kud'in sa , tun ana kai 'korafi filin jami'an tsaron har ana tsoron tinkarar jan ragamar Alhaji BELLOH don tuni yayi suna a garin Kano duk wanda yayi taurin kai kuma to ha'kika zai bar duniya ,,,



Hajiya Lubabatu 'yar jahar Adamawa state daga 'karamar hukumar Yola ta arewa, wacce ta taso a gidan talakawa kyaunta bai sa ta sayarda gangar jikinta ba, kasancewar su talakawa tunda taga Alhaji BELLOH RABE take ta kamu da tsanamin soyayyar sa kamar yanda yace shima yana son ta basu tsaya dogon bincike ba aka d'aura auren domin ganinsa mai arziki da faran-faran da mutane , Hajiya Lubabatu batayi karatun boko ba don iyayen ɗsu basu da wannan 'karfin sai dai an sanya tayi ilimin addini har islamiyya ta kammala jiran miji take Alhaji BELLOH na zuwa aka bashi ita suka yi birnin Kano har Allah ya azurta su da samun Faisal daga shi kuma ba wani motsi .........,.











Al'kalamin ƙanwar soja ✍️💞










⚖️ 💧HANYAR RUWA💧⚖️
💦The way of water 💦






Together 💪
BY


'KANWAR SOJA


RUMMY'N ROYAL


ZAHRA ROYAL ,


A heart toching story 💔 say NO to rape❌








In the name of Allah the Beneficent the Merciful




_After the successful of (FARASHIN SO &. RABI DANJA ) & ( FANSAR MACIJIYA), now we are back with ( HANYAR RUWA )_






🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, fad'akarwa, ilimantarwa da kuma nishad'antarwa_*
_(R.S.W.A)Ruwa kad'ai ke maganin k'ishi_


*Alk'alaminmu 'yancinmu*













PAGE _2️⃣











SADAUKARWA


Wanan littafin sadaukarwa ce ga fittaciyyar ƙunƙiyar nan ta haziƙan marubuta , jajirtattu , ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION, muna farin cikin murnar zagayowar ranar samun wanan ƙunƙiyar shekaru biyu , Allah ya ƙara mata ƙarfi da darajar ta a idon Duniya up up up 🔥 ROYAL.









In kina group ɗina bakya comments zan cireki*










*******************************************










Har Allah ya azurta su da samun Faisal daga shi kuma ba wani motsi.








Kamar yauma zaune hajiya Lubabatu take kan kujeron parlornta wadda suka gaji da had'uwa tana danna wayarta mai tsadar gaske ga wani shayini take kai daka ganta kasan kud'i da hutu sun zauna a jikinta,















Shigowa taji anyi an fad'a kanta "Mommy" cewar Faisal d'ansu d'aya tilo wadda bazai wuce shekara 27 zuwa da 28 amma duk haka zaune yake ya mak'ale mata a jiki itama dai suna bala'in son yaran nasu wadda Allah ya basu shi d'aya shi yasa suka d'au son duniya suka d'ora masa shi yasa duk wadda ya tab'a sa sai inda k'arfin su ya k'are shafa kansa take tace

















"Ɗan albarka ya haka ko yinwa kake ji ne uhm?", Tab'e baki yayi da cewa "a'a fa Mommy wai Dad ne yace saina bisa wajan aiki" ya idasa maganar yana kwab'e baki Dad dake shigowa yace "bafa wani aiki zaka yiba ba kawai ka fara sanin ya abubuwa suke ne" da sauri Hajiya Lubabatu tace "hakane kuma tashi kaji Allah ya tsare hanya" tashi yayi yana b'ata fuska dariya suka bisa dashi harya suka shiga mota aka bud'e masu get suka wuce.



















Wata mata ce zaune ita da yarinyarta tsakiyar hanya yarinyar ta juwa baya da alama bara suke daka kalle su kasan suna cikin wahala daka kalle su suna da d'an yawa wajan da alama basai ka tabbaya ba y'an gudun hijira ne yarinyar ce ta juyo da sauri ta washe baki da alama sadaka aka bata kyakkyawar gaske ce yarinyar ni kaina saida na girgiza da kyawunta fara sal Amma wahala duk ta b'oye hasken fatar tata ga d'an k'ara min bakinta mai d'auke da jan leb'e yarinyar da bazata wuce shekara 14 amma daka kalle ta kai kace ta Mayan tane saboda halitar da Allah ya zuba mata kamar ita tayi kanta ga gashinta mai kamar na turawa dan hijaf d'in data sa duk ta yayyage ana iya hango tudun gashin murmushi take jefama uwar mai k'ayartarwa da sauri uwar daka kalle ta suna kama da yarinyar uwar tace .

















"ILIHAM wannan farin ciki haka mi muka samu ne" da sauri ta matsa kusa da uwar tace "Ummah kin gani d'ari biyar aka bani sadaka yau mun samu na cin abinci" Allah sarki wasu hawaye ne suka zuboma Ummah da sauri ta share na tausayinsu dankar Iliham d'in ta gani.














Motoci ne suka tsaya wajan bada hannu dai-dai wajan su Iliham da sauri masu barar suka tashi da sauri Iliham tace "Ummah bari naje kona k'ara samo mana" da gudu ta tsaya dai dai wajan motar su Faisal Ummah na kiranta amma ina takai wajan tana bara "a bamu sadaka saboda Allah da Annabi" Faisal da dama cike yake gashi basu son tallaka Alhaji BELLOH kuwa wani uban tsaki yaja Ilham kuwa da bata san miye ba tasa hannu tare buga gilas d'in motar da sauri wani b'acin rai ya ciyo Alhaji BELLOH b'alle murfin motar yayi ya fito yana huce ita kuwa Iliham tsora tayi tad'an ja baya batai aune ba taji an d'auketa da gigitaccan marin daya sata fad'uwa k'asa fashewa tayi da kuka da sauri Ummah tayi wajan d'iyar tata tana rungume ta tana hawaye itama Alhaji BELLOH kuwa nunasu yayi da yatsa.























"ke harkin isa kisa hannu kina tab'a mana mota mai daraja haka ke wacece k'azama dake banzaye kawai" Faisal daya fito shima ganin Dad d'in ya koma cikin mota ya tsaya kansu yana tofa masu miyau da cewa "bakuda aiki saiyin bara masu matatar zuciya kawai" shima ya shiga mota yana wani abun tsaki Iliham kuwa zuciya ce ta ciyo ta ta shi a harzik'e dan Allah yayisu a haka ai bawai baya sunsu ba ne da sauri Ummah ta rik'eta tana girgiza mata kai hawayen tausayin su na zuba ita kanta Iliham d'in ganin Ummah na kuka ta fad'a jikinta tana k'ara fashewa da kuka mai ban tausayi mutane duk sun taro wajan........


























Share fissabilillahi 🤳


ZAHRA ROYAL STAR CE✍️✍️✍️✍️✍️🥰
[2/5, 7:33 PM]






https://chat.whatsapp.com/GlC9QmyuWMG7PmC1vhGp4I






https://chat.whatsapp.com/EkTp0cXsTThKckSR3CG8aW








⚖️💧HANYAR RUWA⚖️


💦The way of water💦






Together
By


ƘANWAR SOJA


RUMYN ROYAL


ZAHRA ROYAL.




A heart toching story💔say No Rape❌








In the name of Allah, the beneficent the merciful.








After the successful of
(FARASHIN SO, RABI DANJA) & (FANSAR MACIJIYA), now we are back with (HANYAR RUWA).










🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}


https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, fad'akarwa, ilimantarwa da kuma nishad'antarwa_*
_(R.S.W.A)Ruwa kad'ai ke maganin k'ishi_


*Alk'alaminmu 'yancinmu*










PAGE 3️⃣













SADAUKARWA


Wanan littafin sadaukarwa ce ga fittaciyyar ƙungiyar nan ta haziƙan marubuta , jajirtattu , ROYAL STAR WRITERS ASSOCIATION, muna farin cikin murnar zagayowar ranar samun wanan ƙunƙiyar shekaru biyu , Allah ya ƙara mata ƙarfi da darajar ta a idon Duniya up up up 🔥 ROYAL.






Ina mai rok'on ALLAH subhanahu wata a'la kamar yanda ya bamu iko da damar farawa lapiya yasa mu gama lapiya, ya kawar da idon shaid'anu akan mu,ALLAH yasa mu amfana da abunda muka zo dashi.



---










Abin mamaki shine tinda wannan lamari ya faru tsakanin su Alhaji Bello da Faisal da su Ilham 'yan gudun hijira, Faisai yake tunanin abinda yayi bai dace ba, yaji babu daɗi, ko kaɗan baiji daɗin abinda sukaiwa waɗan nan almajirai ba, abin ya matuƙar tsaya masa a rai, ta yadda idan ka dube shi sai kaga damuwar a fuskarsa mai cike da ƙawataccen kyau irin na Yaran da hutu ya ratsa,




Lokacin da Hajiya Lubabatu ta fahimci wannan damuwa a fuskar Faisal hankalinta ya matuƙar tashi, dan ko misƙala zarratin bata ƙaunar taga yaron ta ƙwalli tal a cikin damuwa, nan take ita ma zaka ganta duk ta birkice, da haka ta fuskance shi














"My dear kwana biyu na ganka sai a slow, shin me yake damar min ya_rona abin tinƙawo na, ya kamata ka sanarwa daahaifiyarka", ta faɗa tare da shafa gefan fuskarsa, murmushi ya ƙawata fuskarsa da ita sannan ya kwantar da kansa a kafaɗarta ya ce "Mom banida damuwa karki damu kaina ke ciwo but nasha magani nasan zai dena", ya faɗi haka ne dan ya kwantar mata da hankali,











"Hmm Faisal kenan, kawai kace ka ɓoye min damuwar da take damunka, amma zan rabu da takura maka da tambaya, kaje ka kwanta ka huta, in sha Allah idan ka tashi zaka ji ciwon kan ya barka uhm", ta faɗa cikin so da kulawa, murmusawa yayi kafin ya sumbaci kumatun ta ya miƙe ya nufi side ɗinsa wanda ya ƙawatu da kayan more rayuwa,






Ƙaton Falonsa ya nufa mai ɗauke da kujeru saiti biyu kalar green da white, direct bedroom ɗinta ya nufa mai ɗauke da Italian bed mai kyau da tsari, kalar white ne komai na room ɗin white ne,











Toilet ya shiga ya sakarwa kansa ruwa, bayan yayi wanka ya fito yana tsane jikinsa da towel, yalwataccen gashin kansa ya busar da handryer, bai shafa komai ba sai bin jikinsa da yayi da turaruka masu ƙamshi da tsada, ɓangaren da kayansa suke ya nufa, wani ɗaki ne na musamman wanda gaba ɗaya wardrobe ɗin kayan sawarsa ne a ciki da takalma, da agoguna, belts, da sauransu, babu abinda babu a wannan waje, side ɗin kayan bacci ya nufa ya ɗakko wata riga mai maɓallai da wandonta iya gwiwa, sanyawa yayi kana ya fito ya nufi ƙaton bed ɗinsa ya kwanta tare da jan blenket, kallon saman ɗakin yake yana tuna lokacin da Dad ɗinsa ya mari wannan Yarinyar, hango kukan da take yi da yadda Mahaifiyar ta ta zo wajen da gudu ta rumgumeta suna kuka,

















"Why Dad, why?", ya faɗa tare da rintse idonsa, baya ƙaunar a wulaƙanta wani, balle ƙaramar yarinyar da abinda zata kai cikinta kawai take nema, "Dad me yasa ka cika zafi akan talaka ne, me yayi maka da zafi haka?", ya tambayi kansa yana jin ciwon yadda Dad yake mu'amularsa, da wannan tunani bacci ɓarawo yayi awon gaba dashi, a cikin baccin ma mafarkin yarinyar kawai yake tana ta kuka.










Bayan kwana biyu damuwa duk ta addabi zuciyar Faisal, bashida wata walwala kamar yadda yake, akan dinning suke suna breakfast, Dad da Mom suna ankare da shi, duk ya sauya, gyaran murya Dad yayi masa saurin ɗagowa yayi ya sauke face ɗinsa a kan Dad "Son what is in your mind", kasancewar bai fiye ɓoyewa Iyayenan nasa komai ba sai yaji yana son ya gaya musu, "Dad ina son na dubo yarinyar nan na bata haƙuri akan abinda ya faru ranar nan", ya faɗa yana kallon Dad, "Son wace Yarinya maiya haɗa ku?", cewar Mom.




Dad kuwa kafa masa ido yayi, "Mom wasu mabarata ne", "what mabarata son, bazan tambayeka abinda kai musu ba dan basuda wannan darajar, sai dai ka sani ban yarda da ka bawa kowa haƙuri ba balle wasu ƙasƙantattu marasa galihu, ka maida hankalinka a jikinka bana son shashanci", cewar Dad daya miƙe a fusace ya bar dinning ɗin, binsa Faisal da Mom sukai da ido, dan lamarin ƙiyayyar da Dad yakewa talaka abin har tsoro yake basu,


"wato Dad harka manta marin da kayiwa ILHAM kenan, to shi Faisal bai manta ba dan
End Ads