x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 7 - WATA RAYUWA

  • 18001 words
  • 21000 words
  • Out of 27012 words

Category: Love Stories

Views 91

02 Jul 2025
Start ads
After Image Ads
ajiyar zuciya kafin yace .
"ina kika shiga faryah ? ina kika shiga sarauniya ta ?,hakika kin kasance wani bangare na jikina a halin yanzu ,rayuwa babu ke zaimin wuya a rayuwata ,kaman yanda na fada a baya ke tawace ,kuma da sannu zamu hadu duk daran dadewa sannan ............"
bai gama surutun dayake ba yaji motsin mutane a bayansa ,yana juyawa yayi arba da dogarai a bayansa ,dauke kansa yayi daga kallonsu kafin yace cikin muryar fushi ,"meyake tafe daku ? waya aikoku wajena iyeee ?😠"
sukuyawa sukayi alamar ladabi a gareshi kafin sukace ,"takawarka lafiya sarki dan sarakai ka gaji sarauta gaba da baya da girman daukakar ka yariman da babu kamar sa ..................tohh yadai ?? 😊😊,me kukace reader ,show me your perceive😊😊.
。。。。。。。。。。
Farfadowar fahreeyah ne daga doguwar suman da tayi ta tsinci kanta a cikin wani keji na itace tare da wasu sauran yan mata guda biyu da kuma wasu samari suma guda uku ,kallonsu take tana rarraba ido yayinda suma ita suke kallo alamar wuya a tattare dasu .
Babu abinda yake tashi acikin kejin sai numfashin su dayake tashi mai cike da wuya acikinsa ,bayan anyi tafiya mai nisane sukaji antsaya,wani mutumine yabude su tareda mika musu wani ruwa acikin gora mai masifar datti ,wawar karbar ruwan akeyi har ana ture wasu gefe ,kallonsu ta tsaya tanayi wanda tashinta kenan daga suman datayi bata gama gane mai yake faruwa ba ,saidai lokacin da taga ana kokuwar ruwane tagane cewar ashe fah itama kishirwa taci jikinta sosai ,saida suka gama kokuwar kafin suka dan diga mata a makogaranta itama ta shaida dan ruwan.
Bayan sun gama hutawane kuma aka sake cigaba da tafiyar da bawanda a cikinsu yasan lokacib tsaywarsu.
Darene yafara kama waje yayinda hasken rana yafara hada nasa yanasa domin ya tattare yabawa dare shima yaci tasa kasuwar ,a dadai lokacinne kuma zazzabi yayi dirar mikiya a gaba daya ilahirin jikin fahreeyah ,wani irin jijjiga takeyi sakamakon karfin zazzabin daya fi karfin tunaninta ,wata yarinyace bazata wuce sa'arta ba ta matso kusa da ita tareda tambayarta ,
"baiwar allah mai yake damunki haka ?"
"b....bansaniba n...nnn...nima ,amma jiki..........jikina zai...kkk...kama ....da wuta "
"ahah mai yayi zafi haka ? ko zazzabi ne yake damunki ?
"ehhh "
tafada hawaye yana zubowa daga cikin idonta ,saboda azabar ta ke ji a cikin ta ,matar ce ta dauki ta dauki wani dan tsummanta ta kara yafawa fahreeyah akanta saboda ganin karkarwar datake yi ,
"nagodee baiwar allah da taimakonki saidai bansan sunanki ba ?"
"ahh sunana LEEMAH ni y'ar cikin garin barduguce ,nice wacce kikaga suna dukana har suka kamaki "
"ayyah to me suke nufi damu dazasu kamamu ?"
"nima bansaniba ,amma daga gani ba nufine mai kyau ba saidai muyi ta addu'a "
"shikenan na gode da kulawarki "
"nima nagodee ki kula da kanki allah ya sawwake "
"ameen "
Haka suka ci gaba da tafiyahar sujayi kwana biyu a hanya ,wani gari daban suka fara hangowa tun daga nesa mai girman gaske,gofar garin aka bude musu domin basu damar wucewa ,kalle kalle suka farayi ganin abubuwa iri iri acikin garin har akazo wani waje mai tarin mutane ,korosu aka farayi daga cikin kejin ana jerasu kaman kaji ,saida aka gama jerasune wasu mutane sukazo suna kallonsu da alama zana zasuyi daga ciki ,wani babban cikinsune ya fara magana da cewar ,
"umarnine daga masarauta kaman yanda yake ,zaku bada bayi biyu ga masarauta a kowane kawowa kafin ku wuce inda zaku je "
"ehh mun sani zamu fitar da haraji kaman koyaushe,saidai kuyi mana uzuri ,domin zamu baku wanda suka gaji sosai saboda bazasu iya tafiya daganan zuwa masarautar saraham ba "
"shikenan ku nuna mana su ,babu komai idan suka huta za'a basu aiki "
mai bayinne ya jawo wani dan saurayi mai laushin jiki dakuma fahreeyah ya turasu gaban mutanen da suka zo ,
"wannan sune lagar tattu a ciki ,wanda bazasu iya doguwar tafiyarmu ba ,"
kallonsu suke kafin suka bawa wasu bakaken bayi dasuke tare dasu damar sakasu a wani kejin ,amma shi na karfene yana da zanen sarauta a jiki
tafiya akeyi saidai basa ganin hanya saboda yanayin tsarin karfen kejin ,kofar masarautar aka bude suka shiga har zuwa harabar wajen masarautar ,fito dasu akayi zuwa gaban UWAR BAYIN masarautar aka durkusar dasu ,kallonsu take cikin kaskanci kafin tace,
" menene sunanku ? "
"ni sunana fahreeyah "
"ni kuma sunana KHAMEEL "
"to ita wannan macen (tafada tana nuna fahreeyah )ku kaita sashen DANDALIN BAYI ,shikuma ku kaishi wajen YAN BARGA ,kutashi ku bisu maza ,gakunan kaman a karya ku ".
Tisa keyarsu akayi kowa zuwa inda aka bashi yayi aiki.
Tafiya sukeyi fahreeyah na binsu abaya ,tana tunanin tashi daya rayuwarta tasake juyawa a karo na biyu ""an gudu ba'a tsiraba kenan "",ta fada acikin ranta ,wani doguwar hanya suka bi tana biye dasu a baya har zuwa wani katafaren muhalli mai dauke da dakuna a cikinsa da yawa.
Wata mata ce tafito daga cikin wajen ta zuba wani uban adoo mai daukar ido ,maraba tayi musu cikin rangwada da kalmasa harshe ,
"maraban ku da zuwa wannan dandali mai dauke da abubuwan shakatawa dakuma dauke kewa ,mai yake tafe daku ?"
"sakone daga uwar bayi ,tace a kawo miki wata sabuwar baiwa zata fara aiki anan wajen ,"
"shikenan zata iya shigowa domin baje tata basirar a wannan fagen "
"tohh maza ki shiga ta amsheki ".
Matarce ta jata zuwa cikin harabar muhallinnasu ,tsayawa tayi ta tareda zuyowa tana kallonta,
"yan mata baki bani sunanki ba ?"
"sunana fahreeyah "
"ohhh suna mai dadi tun daga sunanki ke mai kyau ce sosai ,gaskiya zaki haska idan kika goge nan gaba kadan "
"uhmm addah bangane abinda kike nufi ba fah "
"😊😊,baki ganeba ,ki bari nan gaba kadan zaki gane mai na ke nufi ,kedai ki biyoni kawai yar sheela 😊😊"
"uhmm amma addah ..........."
"daina kirana da wata addah ,kice kawai ZILZILIYYAH ,haka sunan yake "

SADI -SAKHNA ce

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(18)

Shiru tayi a tsaye bata da niyyar shiga cikin dakin saida zalziliyyah ta ne takula da cewa ita kadai take tafiyanta wanda takee bayan ta bata ma biyota ba ,juyowa tayi takalleta tareda cewa ,
"Menene kuma yatsaida ke haka? Kibiyoni na nuna Miki inda zaki zauna ko a wajen zaki kwana iye?"
"Ahah dama naji kince wai zamu dunga shakatar da wasu .......nikuma ina da aure fah gashi....."
" Ya'isa haka yan mata , me kike tunani,kina da zavi? to kicire hakan a zuciyarki ke baiwa ce yanzu Wanda zata bada jikinta don bakin masarautar nan suji dadi,Dan kimanta da cewar kintaba rayuwa a baya bare kuma aure ,idan kuma bahakaba zaki fuskanci hukuncin da bakya tsammani"
Jikin fahreeyah ne yayi sanyi game da jin furucin shugabar tasu, Wanda har aka kaita wajen dazai kasance muhallinta kukane yake zuba daga idonta saboda rashin mijijnta datayi Wanda tasan a yanzu yayi mata nisan da bata tsammanin zata iya cimmasa .
Wani daki zalziliyyah takaita mai girma ,saidai daga gani akwai mutane masu Dan dama dasuke rayuwa a ciki, saboda abubuwan kwanciya da kuma shirgi na masu dakin da idonta yayi arba da shi ta ko'ina,muryar zalziliyyah ce ta saka ta dawo da hankalinta daga barin kallon dakin zuwa kallon shugabar tasu,
"Toh wannan shine rukunin dakin dazaki dunga zama ,shi wannan wajen shine muhallin Wanda zasu dunga taryar bakin dasuke tsaka tsaki,wato ba masu matsayi sosai ba, yanzu bari naje ina da abinyi,zamu kiraku training idan kinyi s'a zaki iya shiga rukunin bayi masu tarar manyan baki,"
Duk magananr da takeyi har tayi ta gama fahreeyah bata tanka mata ba, saboda zabar jimamin halinda ta tsinci kanta a ciki.
Dudduba dakin tafarayi kozata samu wajen da ba kayan wata a gurin ta zauna,wani waje tagani mai a gefen kayan wata ta wajen barin dama a dakin, saida ta fara dan gyara wajen kafin ta zauna,jin kamar jikin ta yayi tsamine saboda tafiyar dasuka yi a hanya ya sata dan kishingida ko zata samu dan hutu kafin jiran mai rayuwar zata zo mata dashi kuma in an jima.
Can cikin baccine taji ana zungurar ta kafa,hakanne yasata tashi a razane domin ganin mai ya,wata mace tagani a tsaye a kanta tana mata wani irin kallo na rashin mutunci,yayin da matan dasuke bayanta kuma suka fara magana cikin dariya,
"Yau zaki san taka wajen KIRISAH,duk abinda ya faru dake kinyiwa kanki"
Ita wacce suka kira da Kirisah dinne tafara hura hanci cikin fushi tareda cewa
"Ba magana nake Miki ba?ko keh kurmiyace ba zaki ban amsa ba iyee?"
"Uhm ban.......san .wajenji bane,dazu zalziliyyah ta kawoni, kuma na ga,bakowa a wajen ne shiyasa na zauna"
"Kutt harni kike cewa dan kinga ba kowa a wajenne kika zauna?t to barikiji nafada miki,cewa nan duk wajena ne, domin ni waje daya yayimin kadan, kuma duk abinda bayanke a dakinnan akeyi,tashi kibani waje,kinyi sa'a ke bakuwa ce dakin fuskanci hukunci daga wajena"
Tashi fahreeyah tayi tareda matsawa can gefe a dungun dakin ta zauna tana mai da numfashi sakamakon wani zazzabin daya fara ziyartar jikinta a karo na biyu,zawo rigarta take tana sake rufe dukkan jikinta saboda sanyin da take ji yana ratsata,a dunkule a wajen da take baccin wahala yadauke ta.
Washa gari da wuri ta tashi saboda baccin kasan datayi saidai bataji zazzabin a jikinta ba kaman yanda ta kwana da shi jiya da daddare,yunkurawa tayi ta tashi saboda jikinta ba karfi,mata tayi arba dasu sun cika dakin masu irin kayan ta sak, saidai kaman wanda ita suke jira da gansu,haka taga sun fara tashi a tare kowa tana nufar hanyar waje,itama binsu tayi dan dama tanason ta rage marar ta saboda fitsarin daya ci karfinta sosai,wani wajen ta kula dashi suna shiga dakayansu wasu kuma na fitowa jikinsu a jike, jikinta ne yabata cewar bandaki ne dan haka kawai sai ta nufi wajen,ta saka kai zata wuce kuma sai taji maganar wata a bayanta tana fadin
"Baiwar Allah naga kina shirin shiga wajen wanka amma ba kayan dazaki sanja,ko ba'a baki kaya kala biyu bane?"
"Ahah an bani yanzu fitsari zanyi ne"
Murmushi tayi mata kafin ta ce
"Kuma fitsari a wajen nan, Hala ko ke bakuwa ce?"
"Ehh ni bakuwa ce"
"Ayyah to zo muje Nara kaki wajen fitsarin toh"
"To nagode"
Bin take a bayanta har suka je wani wajen amma ginin wajen sa masu matsakaicin girma ne, tsayawa tayi tareda juyowa ta kalli fahreeyah,
"To nan shi ne wajen bahaya da fitsari,wancan kuma da kika gani wajen wanka ne"
"Nagode baiwar Allah"
"Kikirani da Sareenah"
"Toh"
Saida tashiga tagama abinda zatayi kafin ta koma inda aka kaita da sunan shine dakin ta, sake zama tayi wajen da ta kwana,saikuma ta ji ana shelar zuwa cin abinci, itama binsu tayi a baya domin ganin wace hanya zasubi.
Wajenne Shima kaman tsarin dakunansu,wato filine kowa yasamu wajen da zai zauna kawai.
Bayan sun gama zama ne aka fara binsu da abinci a kwano ana raba musu,duk wanda yagama sai ya kai kwano zuwa wani waje daban kafin ya fita,ita dai duk abinda suka yi binsu take tana aikatawa kawai, wajen wanki ne kawai bata bisu ba saboda kayan ta sabine babu datti a jikinsu tukunna.
A haka dai suka gama al'amarinsu na ranar har zuwa lokacin da wani daren yasake shiga inda shima zazzabin ta yasake lallabowa daya ga dare yafarayi,haka ta gama sheshekar zazzabin ta har bacci ya dauketa.
Washa gari bayan sun tashi, fahreeyah bata sha wahala ba wajen gano dukkan al'amuran da suke gudanarwa a kullum.
Saidai yau shugaba zalziliyyah ta kirasu zuwa training lokacin dasuka gama cin abinci,da koyarwar gyaran jiki aka fara nuna musu,sai kuma kwalliya da kuma karairaya domin birge duk wani da na miji,sabin bayin da'aka kawone aka fara yiwa kwalliya don ganin nasu zubin,tun ana fara kwalliya zalziliyyah ta kalle ta tareda cewa
"Fahreeyah na maida ke rukunin masu tarar manyan baki"

SADI-SAKHNA ce

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(19)

Wajen kwalliya aka shiga da duk wata sabuwar baiwa domin gwada yanayin salon ta dakuma roll din dazata taka a matsayin ta na baiwar daza ta na dauke wa bakin masarautar kewa.
Tun daga wajen gyaran jiki fatar fahreeyah tayi wani irin laushi da haske tun kafin a je ga dora kwalliya dakuma kayan sakawa, zalziliyyah ce ta matso kusa da ita bakin ta a bude saboda kyan da taga fatar ta tayi da kwalliyar,
"Gaskiya jikinki yana da kyau sosai,zaki kasance a wajen masu tarar manyan baki"
Wani irin faduwar gaba ne ya riski kirjin fahreeyah sakamakon furucin daya fito daga bakin zalziliyyah, yayin da a bangaren Kirisah kuma bakin cikin ya lullubesu ita da mabiyanta saboda jin matsayin da aka bawa sabuwar baiwa bayan su sun dade a wajen basu samu ba, fahreeyah yace ta daga idonta tana kallon zalziliyyah da take ta kwaro mata bayani kafin tace,
"Shugaba da kinyi hakuri kin barni a matsayina na da din kawai domin inaga kaman shiya dace dani,a matsayina na sabuwar baiwa a wannan wajen"
"Nariga na Yankee hukunci, sannan inaso ki sani cewa abinda ya dace da masarauta nakeyi ba wai ra'ayinku ba, domin inaso kusan cewa tun ranar da kuka shigo wannan masarauta da sunan bayi kuka rasa duk wani yanci da kuke da shi dan haka banason wani yasake saka min baki ko shishshigi a cikin aikina"
Shiru ne ya ziyarci wajen sakamakon yanda sukaji zalziliyyah tana ta fada akan maganar da fahreeyah tayi dahaka wajen ya watse kowa yakama hanyar inda aka kaishi domin yin aiki.
Fahreeyah ce tsaye a bakin dakin su na da, kafin a sauya mata matsayin ta, shiru tayi kaman mai tunani tana cizon yatsa, domin daga ganin ta zakasan cewa tsoron shiga dakin take,waigawa tayi da saurin jin anayi mata magana a bayanta,a jiyar zuciya da sake dan ganin mai maganar ba kowa bace illah Sareenah,wanda suka hadu a wajen wanka jiya, murmushi tayi mata kafin tace," me yasame ki haka kike tsaye a wajen? Ko tsoron shiga kike?"
"Ehh to.... dama kayana zan dauko a dakin"
"Karki damu muje na rakaki dama nazo wajenkine, domin naji dazu shugaba ta mayar dake sashenmu kuma naga baki zo ba har yanzu to shine nazo Naga ko lfy?"
"Ahah bakomai kawai ina tsoron shiga dakin ne"
"Hmm ai naga alamar hakan, karki damu muje na rakaki"
Shiga dakin sukayi amma duk da haka fahreeyah na boye a bayan Sareenah,
"Hhhhhhhhh hmmmm wai ke gaki baiwa mai matsayi ko? to ki saurari zuwana cikin rayuwar ki,sai kin kwammace ba a haifeki ba wlh, hmmmm mujuba ni dake,nadade ina mafarkin zama baiwa mai babban matsayi amma wai zuwan ki yau har kin samu, hakan bazai yiyu ba .......
"Gashi kuma ya yiyu kuma, sannan da kike zancen ta kwace miki matsayi ai ba ita ta Hana a dauke ki ba koh!??baki cancanta bane shiyasa,ke fahreeyah je ki dauko kayan ki kizo mutafi"
Cikin sanda kaman za'a ce arrrrr ta ruga da gudu,taje ta dauko kayan a wajen kwanciyar ta jiya, hanyar kofa suka nufa zasu fita,sai kuma muryar Kirisah ta kara ziyartar dodon kunnensu,
"Da gake har mai daure miki kan macijin kina wasa da wutsiyar zaku ga abinda zan muku hmmmmm"
Ko ci kanki basu ce mata ba suka fice daga dakin,tana ta bambamin fada ita kadai.
Bayan sun fitone Sareenah ta kalli fahreeyah kafin tace,
"Gaskiya kina da sanyi dayawa sannan tsoron ki yayi yawa"
"Kiyi hakuri nasaka ta zageki koh"
"Ina zancen kinada tsoro amma kina ban hakuri"
Murmushi kawai fahreeyah tayi mata kafin tace,
"To ai bansan mai zance miki ba saboda ban tashi cikin mutane sosai ba, shiyasa"
"Menene tarihinki to?zanso naji sannan kuma mai yasa kika tsinci kanki a wajen nan?kada kiyi tunanin ni macuciyace, kawai tun ranar da nafara ganin ki nasan bakiyi kama da irin bayin nan wajen ba,naji kawai kin burgeni sosai".
"Shikenan nayi alkawarin zan baki tarihin rayuwa ta amma inaso kidan bani lokaci kadan, sannan inaso kibani takaitaccen bayani akan wannan masarautar ko kadanne"
"Shikenan inshallah zan sanar dake dan abinda nasani akan wannan masarautar,amma kafin sannan mudan zaga sauran wajajen da baki saniba tukunna"
Sareenah ce ta jaa fahreeyah sukayi cikin fadar domin zagawa da ita ko ina.
Tafiya suke suna dan taba hira,duk inda suka wuce sai Sareenah ta fada mata inane sannan kuma ya ko'ina yake dakuma tsarin sa, fahreeyah yace ta tsayar da Sareenah tare da nuna mata wani gini mai kyau amma da alama bakowa a wajen,bayan ta nuna matane kuma ta tambayeta to wajen shikuma inane,ajiyar zuciya Sareenah tayi kafin tace,
"Fahreeyah ba'ason a dunga maganar da ta shifi wancan ginin a wannan masarautar saboda hukunci yakan iya hawa kanki idan akaji hakan,tunda na gama nuna miki komai yakamata muko ma haka kuma,"
Zanta Sareenah tayi suka fara komawa muhallin su,amma har sannan idon fahreeyah yana kan wannan ginin da tagani, haka kawai taji wajen ya birgeta sosai.
Saida sukaci abinci kaman kullum kafin suka koma dakin su, fahreeyah ce ta kalli Sareenah cikin kaguwa da san jin labarin masarautar,
"Uhmm Sareenah ina jinki bani labarin to"
"Uhm dama kinada surutu haka fahreeyah? Sanda na fara ganin ki ban zata zakiyi surutu haka ba"
"Eh nidai naji,mufara labari tunda kinmin alkawarin koh?"
"Shikenan to"
""Da farko naji kince baki san ko sunan masarautar nan ba, to sunan ta*masarautar BAHMEER* ita wannan masarauta tana da karfin mulki da iko domin itace da biyu a duk duniya mai fada a ji,dazu kin tambayeni wani gini muna tafiya,to wannan ginin ba mallakin kowa bane face na babban dan sarkin wannan masarauta wanda yayi batan zana shekaru uku dasuka wuce sanadiyyar wani sabani sa suka samu shi da iyayensa,mai suna yarima SAHEEL, kuma har yanzu ba wanda yasan inda yake, saidai labari ya taba zuwa cewar anganshi a garin bardugu ...........
Ehh saheel, kuma garin bardug????!!!!😯..

SADI-SAKHNA ce

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(20)

Fahreeyah ce a tsaye kamar
End Ads