x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 1 - KULU

  • 1 words
  • 3000 words
  • Out of 28650 words

Category: Tale Stories

Views 135

29 Aug 2025
Start ads
After Image Ads

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[10/23, 8:59 PM] CUTIE~RIAM: [10/23, 8:52 PM] CUTIE~RIAM: *KULU*

*BY:RIAMCOOL*


*Mikiya writter's Association*


*Bismillahirrahamanirahim dukkan yabo da godiya sun tabbata ga ubangiji da ya bani damar kammala littafin Bayan wuya hakikanin gsky Ina godiya ga masoyana da suka nuna mani zallar love a litattafaina ,ga shi na sake dawo maku a KULU lbr Mai rikici da sarkakkiya fatan za ku bani hadin kai My Habibties*



*P.1&2*

A lulume garin yake da bak'in hadari wan da ya saka bishiyun cikin jejin kad'awa da k'arfi yayin da ba ka jin sautin komai sai sautin kad'awarsu da Kuma walk'iya da tsawar da ake yi

A hankali nake k'ara ware manyan narkakkun idanuwana na zubasu a sararin samaniya ina kallo yadda baƙin hadarin ke gudun tseral a sararin samaniya, hankalina a tashe na fara ɗaga ƙafafuwana da niyyar barin jejin domin gudun kar ruwan saman ya dakeni, sai dai bakin Alƙalami ya bushe, nan take wasu ruwa masu ƙarfin gaske suka tsage, sosai nake gudu ina jefa ƙafafuwana duk inda suka faɗa, yayin da ƙayayyuka suka sossokar min ƙafa amma ba ta ita nake ba, nafi jin ruwan ya dakeni, domin ni kaɗai nasan wahalar da zan sha idan ciwona ya tashi,burina bai wuce na ganin na isa cikin gari ba,tamkar wacce za ta tashi sama haka nake ɗaga ƙafafuwana ina jefasu duk inda suka faɗa yayin da suke man raɗaɗi amma a haka na dage ina fyalla gudu har na isa cikin gari, yayin da numfashina ke gargada yana sama da ƙasa


da taimakon Ubangiji na samu na shiga ragargajajjen gidan ina mayar da numfashi, ban iya ɗaga fatar bakina nayi sallama ba saboda nauyin da tayi man, ɗaga labulen ɗakin zanyi na tsinkayi Muryar Mamah Khubrah "Innalillahi'wa'inna ilaihirraji'un, wallahi ta kashe ta KULU ta kashe man yarinya" duk yadda nake jin jikina bai hanani faɗuwa ƙasa ba ina mayar da wani wahalallen numfashi wan da nake jin ya sarƙafe man duk wata kafa ta fitar numfashina, da ƙyar na iya samun ɗaga bakina na kurma ihu wanda nake ji ko zan samu sassaucin abinda nake ji,


tamkar an jefosu haka na gansu sun fito sunyi carko_carko a kaina,idanuwansu sharkaf da hawaye kamar yanda nima nawan yake yana malalar da hawaye, "KULU kin kashe man yarinya hankalinki ya kwanta,amma wallahi ki sani kema sai kin tafi inda kika tura man yarinya" Mamah Khubrah ta faɗa tana tunkaroni da wuƙar dake hannunta,da sauri na rintse idanuwana ina jiran tsammani,sai dai shirun da naji ne na ƴan second ya sakani ware idanuwana sai dai abin da na gani ne ya sakani ware idanuwana, ganin yadda Mama Khubrah ke zubar da jini ta baki,hakan ya sakani kai dubana ga wacce ke gabanta wan da iya ni kaɗai ce ke ganinta,hannu ta miƙo man tare da kama nawa hannun ta fita dani



Kamar yanda ta saba fita dani ta zaunar dani a kogo yauma hakan ce ta faru, zaune nake ina sauke ajiyar zuciya hawaye na sintiri a kumatuna "KULU" naji ta ambaci sunana wan da ya sakani ɗago da fuskana ina dubanta tare da furta "Diyana wane laifi na aikata maki da kike kashe mutanen dake tare dani"

"Kulu ba wani laifin da kika aikata man,ina yin hakan ne ga duk wan da ke yunƙurin cutar dake,sannan Zainab ba kashe ta nayi ba, na ɗauki ruhinta ne a jikinta"


Share hawayen dake fuskana nayi ina furta "Diyana na roƙeki da Allah ki mayar mata da Ruhinta kar ki ƙara yunƙurun kisan kai a kaina, ki bari ayi man dukkan abinda za ayi man Ni kaina na gaji da baƙar ƙaddararriyar rayuwar da nake ciki,na san tun lokacin da Mahaifiyata ta yar dani ƙaddara ke bibiyata, ita kanta Mahaifiyata na san tsanata tayi har ta yasar dani dokar jeji,to zafin mi zanji da waɗanda suka ɗaukenj suka renini duk da azabar da suke bani tun ina ƴar ƙanƙanuwa wacce ko kaɗan bani ganinta ina matuƙar ji dasu duk da ba suyi dani ina kallonsu a wani matsayi wan da bai kamata ace ta silata an cutar da su ba ko dan Baba" na ƙarashe zance da kuka


kafaɗa ta Diyana ta kama tana bubbugawa tace "naji zan mayar mata da ruhinta Kulu,ni ɗin Uwa ce a gareki ba zan so zubar hawayenki ba, tun lokacin da Mahaifiyar ki ta ajiye ki a rukata na ajiye ki a matsayin ƴata, duk ni ɗin ba Ƴar Adam vace amma na zaɓi rayuwa dake kulu tabbas ke ɗin asalinki wani jini ne mai ƙarfi wan da nake da tabbacin ke ɗin ba Mutum bace kamar kowa,ke ɗin kin kasance sirki biyu"


"Diyana ban gane ni ɗin sirki biyu bace shin ni ɗin ba Ƴar Adam bace hala ina da sirki da jinin Aljanu? ? Shi ya saka Mutane da yawa tsanata" na faɗa da hawaye


murmushi ta saki tana girgiza kai tace "zuwa gaba za ki san dukkan wani tarihinki wan da ni kaina shi nake da burin sani wan da duk ƙarfina na gagara sanin asalinki da kuma tarihinki, tabbas ke ɗin babban jini ce mai cike da ƙarfin Izza da kuma ƙaƙƙarfan iko" ta faɗa tana share man hawayen dake sintiri a fuskana,tare da yi man maganganun da tasan ina so sannan kuma suke kwantar man da hankali Abinci ta Bani naci sannan ta mayar dani har gidammu wan da nake ɗarɗar ɗin shiga cikinsa domin ban san mi zan tarar ba, DA fargaba na kurɗa kaina a ɗakin Mama Khubrah sai dai yanayin da na iske su ne ya sakani sauke wata nannauyar ajiyar zuciya ganin Zainabu ta tashi alamun Diyana ta mayar mata da ruhinta dubana na kai gun Mama Khubrah wacce itama ke ta faman hararana tamkar idanuwanta za su faɗo "Toh tsinanniyar Tsintacciyar Mayya Allah ya nufi Zainabu kwananta basu ƙare ba, ba kiyi nasara ba, da ace wallahi kin kashe man yarinya kema sai na kashe ki, wato dan karna ɗau mataki ya sakaki fara sha man jini a ɗazu kika zubar min dashi to wallahi sai nai maki dukan da jinina ya zuba hakanan Malam ya tsinto mana bala'i" ta ƙarashe zancen da miƙewa tana nufo wurina gadan_gadan za ta dakeni


"KHUBRAH wallahi kika daketa sai ranki yai mummunan ɓaci za kiyi tsantsar nadama,sannan nai maki abin ban taɓa maki ba a duk tsawon shekarun da muka kwashe dake,shin ita Kulu da take Ƴar tsintuwa ba Mutum bace?" BABA ya faɗa da tsantsar ɓacin ran da ya bayyana a fuskarsa

Duk da Mama Khubrah najin shakkar Mijin nata bai hanata faɗar "wallahi Malam ba zan ƙyale Kulu ba sai na ɗauki mataki a kanta naga ƙarshen maita ko ita Sarkin Mayu sai na kawo mata ƙarshen maitarta ,sannan ta san a ɗakin da za ta kwana ba dai a wannan ɗakin nawa ba sai dai ta kwana a waje" tana gama faɗin hakan ta fincikoni tana fito dani waje tai wulli dani wan da ya sakani faɗuwa ina fasa ƙara sakamakon ƙashin hannuna da ya bugu da wani dutse dake girke a ƙofar ɗakin da gudu Baba ya fito yana miƙar dani ya rarrasheni, tsaye muke daga mu har shi ga hadari ya ƙara harhaɗuwa da alamu dai wasu ruwan za a sake yi,kallona yayi yana faɗin "KULU ko za ki kwana a ɗakina ni sai na fita waje na kwana a shagon Ilah"


ban musa ba na shiga ɗakin Baba shi kuma ya fita rufe ɗakin nayi ina kwanciya hawaye na biyo kuncina, a hankali na fara jin jikina na sauya man yayin da na dinga gani abu mai sheƙi da kuma walwali a duhun yana tunkaroni miƙewa zaune nayi ina ja da Baya kafin wani haske mai tsanani ya bayyana, wan ba komai bane ya saka wannan haske sai wata narƙeƙiyar macijiya wacce tai man ƙur da idanuwa,yayin da Kanta ke ɗauke da Kambun sarauta, kallona take tana ɗaga kai ,ban ida shiga ta shin hankali ba sai da naji tana magana "me ya saka da kimarki da darajar ki kike rayuwar ƙunci da ƙasƙanci,ke ɗin fa Babban jini ce wanda ya kamata ace a halin yanzu kina daula hadimai na bauta maki" ta ƙarashe zance da ɗaga wutsiyarta na baya za ta shafo ni,sai dai tun daga lokacin kuma ban kuma sanin inda kaina yake ba sai dai na tsinkayi dukan ƙofar da ake yi tamkar za a cire ƙofar, A hankali na ware idanuwana na tashi na buɗe ƙofar ɗakin wan da naci karo da Halime Babbar ƴar Khubrah,kallona take irin na tuhumar nan ganin ana sanyin damina amma jikina ni sharkaf yake da zufa ina mayar da numfashi " dama ke ce a ɗakin ba Baba, waye a ɗakin naki ? naga kina mayar da zufa kar dai ace naman wani ne kike dahuwa da jikinki za kici"



girgiza mata kai nayi ina faɗin "a a wallahi bacci na tashi yanzu " fizgoni tayi tana faɗin "dallah fito kiyi mana girki da gyara gida" da toh na amsa har a lokacin hankalina sam ba ya tare dani ya karkata can ya zuwa wata duniyar tunanin, wan da nake tambayar kaina "wacece ni,Miye alaƙana da har nake iya ganin wani baren jinsi ba nawa na ƴan adam, na fara gazgata zancen Diyana tabbas na cewar ni ruwa biyu ce,to amma miye alaƙata da Macijiyar ji" bani da mai bani amsar waɗanan tarin tambayoyin



*******************************

*Masarautar JOHAAN*


A hankali wani sautin busa mai cike da firgitar da Bayi na cikin gidan Sarautar ke karaɗe ko ina wan da ke masu nuni da cewar akwai wani gagarumin Abin da zai faru a cikin gidan wan da a iya bayin gidan ne suka shiga ruɗani, yayin da kafin su ankara duk wani bawa da aka gani ake korasu da matsanancin bugu har izuwa ƙofar Fada wan da ta cika da mutane mabanbanta, tun da ake dukan fatar jikin nasa ta ɗayaye amma shi sam ko ɗar iya abin da ya sani kawai yana cikin farin ciki marar misaltawa musamman da yaga cikar burinsa ya gabato..............



*Riamcool ce*
[7/17, 8:06 PM] RIAMCOOL: *kULU*




*By; RIAMCOO*





*Mikiya writter's Association*


*Bismillahirrahamanirahim*



*P.3&4*


Dukkansu zubewa su kai a bakin Fadar yayin da suke mayar da numfarfashi,daka musu tsawa wani dogari yai wan da ya sakasu ɗagowa, kallonsu nan take aka fara cinikayyar su ya zuwa wasu masarautun,tun lokacin da akai cinikayyarsa ya zuwa Masarautar da yake burin komawarsa ya tsinci kansa a matsanancin farin ciki miƙewa yai tsaye yayin da fadawan masarautar suka nufosa, tamkar za su rissina masa sai dai kallon da yai masu a faƙaice da kuma ƙyalla musu ido ɗaya ya saka su juya akalarsu ya zuwa daka masa matsananciyar tsawa, wanda ya sakasa shima duburburcewar ,yana nufar inda aka tanadi wasu Amalanke da ake zuba bayin a ciki, shiga ciki yai Yana bin masarautar Benin da kallo wacce akewa laƙani da JOHAAN wacce har ya zuwa datsewar numfashinsa ya san da cewar ƙabilarsa ta Ogboni ba zasu mance illatarwa da ƙabilar Ozo su kayi musu ba, hakan ne ya saka sa shigowa a cikin masarautar JOHAAN domin ɗaukar sirrinsu ta yadda su ƴan ƙabilar Ogboni za su fuskancesu


Wani ajiyar zuciya ya saki yana fito da wata sirriyar sarƙa mai ɗauke zanen wani kan halitta mai ƙaho,ɗagawa sama yayi yayin da ya fara magana kamar haka "Olorun jowo ran awon ara ilu Ogboni lowo, bawo ni mo se kuro nijoba yi nigba ti mo yan lati pada, mo gbe ori awon eeyan si inu mo si se ileri lati mu eje won. (Ya abin bauta ka taimaki ƴan ƙabilar Ogboni ka bamu nasara a kansu, ka sa yadda na bar masarautar nan a lokacin dawowata na ɗauki kawunansu ni kuma nayi Alƙawarin zan shayar da kai jinanansu)" yana gama faɗin hakan ya mayar da sarƙar nashi



tafiya suka fara yi yayin da suka yiwa masarautar JOHAAN nisa hakan ne ya saka su dakata wa da Amalanke, fitowa yayi daga cikin bayin yayin da suma Dogarawan suka fito a motocin su sai dai dukkansu suka faɗi ƙasa suna masu rissina masa tare da furta magana da Yaren yarbanci " ọmọ ọba (Yarima) Abiodun Adewale femi takawarka lafiya Ya Abiodun Adewale femi takawarka lafiya sha kundum shamaki,takawarka lafiya ubangabasawa Yariman masarautar OYO Mai shayar da abin bauta jinane takawarka lafiya Bijimin duniya waye zai shiga masarautar JOHAAN da Ƙulli ya fito da rai in ba kai ba,mun rantse da Abin bautar mu Dodo soluwole kai ɗin Yariman sa ne baya ga Yariman HANDAASH takawarka lafiya Yariman yaƙin matsafa........" Shiru su kayi sakamakon ɗaga musu hannu da yayi, yana mai basu umarni da su miƙe da hannunsa,miƙewa su kayi yayin da suka nufo wurinsa suna mai saka hannayensu a fuskarsa su ɗebe masa jemammiyar fuskar da ya liƙa a fuskar sa wacce za ka rantse da cewar ba ta roba bace,


nan take haɗaɗɗiyar fuskarsa ta asalin kyawawan Yoruba ta bayyana mai cike da tsantsar kyau wan da ya kasance Black beuty sai dara daran idanuwansa na asalin ƙabilar Ogboni da madai_daicin lips nasa da kuma zara_zaran gashin giraren ido da gewayayyen sajensa wanda yai yawa tsabar daɗewar da yai ba a askesa ba,sai dai fuskar nan a haɗe take tamau babu alamun wani haske a tattare da ita ko annuri, kallo ɗaya za kayi masa ka tabbatar da shi ɗin ƙaƙarfane ta ko ina kama daga siffar jikinsa,



shiga yai cikin ɗaya daga cikin motocin yayin da suma Dogarawan suka shiga sun jima suna tafiya before su isa a cikin garin Oyo wan da tun a matsayar shiga suka fara tarar da manya manyan motoci na Alfarma ƙirar lamborghini a jejjere buɗe masa a kayi ya fito da cikakkiyar Izza da ƙasaita wan da ya saka Mutane ihu da kirari wan da yake ƙara jin wata cikakkiyar Izza na zauna masa,Zama yai a Back seat Yana mai lumshe idanuwansa, yana ƙara jin wata nutsuwa na ziyartarsa,



*MASARAUTAR HANDAASH*


cike take da tarin manyan makaɗa da kuma bushe_bushe yayin da Mutanen cikinta ke cike da tarin farin ciki da murnar dawowar Yarima Abiodun Adewale femi,sai dai a wani ɓangaren ba za a rasa tarin masu baƙin ciki da dawowarsa ba kamar yanda ya kasance a gun Boluwatife matar Babansa



tsaye take a gaban wani baƙin gunki yayin da idanuwanta sun kaɗa sunyi ja magana ta fara tana faɗin "Ọlọ́run, ẹ̀ṣẹ̀ wo ni mo ṣẹ̀ tí ogun ìbọ̀rìṣà mi sì jẹ́ ìtẹ́wọ́gbà"(Ya abin bauta wane laifi na aikata da tsafina yaƙi karɓuwa?"

dogon numfashi taja yayin da taci gaba da faɗin "na kwana ina shayar da kai jinane da ruwan jikin mutane amma tsafina bai tafi dai_dai ba akan Abiodun, mi ya sa na gaza yin nasara akan Abiodun har yanzu,me ya saka masarautar JOHAAN ka sa gano Abiodun??? na so ace Abiodun bai dawo ba" ta faɗa wani sabon kukan takaici na kamata

Motsin da taji gunkin nayi da kuma sheƙewar wata dariya da ta tabbatar mata data Boka Olusegun ne, "Boluwatife!!!" Ya ambaci sunanta da ƙarfi wan da ya sakata kallonsa

"Boluwatife kin gaza nasara akan Abiodun ko? na faɗa maki daman ba za kiyi nasara akan tonuwar asirin Abiodun a masarautar JOHAAN ba, ballantana a samu damar kashe sa, sai dai kina da dama ɗaya wacce zan faɗa miki duk da ba lallai ki yarda ba" ya faɗa yana tunkarota


"faɗa man ita Olusegun" ta faɗa da son samun mafita

dariya ya kuma kecewa da ita yana faɗin "mafitarki ɗaya
End Ads