x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 7 - ABULLE TA MAI UNGUWA

  • 18001 words
  • 21000 words
  • Out of 44439 words

Category: Love Stories

Views 287

17 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
ki yi, zuwa yamma yayanki zai fita da ke sai kiga gari ko?"

Da murna ta ce,

"To, Baffa!"

"Ɗan gidan wanene angon ne? Na manta ban tambayi Ilu ba."

Sunkuyar da kainta ƙasa ta yi, ta kamo bakin mayafinta rufe rabin fuskarta sannan ta ɗago fuskar ta buɗe ido ɗaya ta ce,

"Mai Unguwar yankinmu ne."

Ta ƙarashe faɗa cikin jin kunya, ta duƙar da kai.

Dariya suka sanya, Hajiya Sabuwa ta ce,

"Da alama ana ji da maigidan nan! Wannan irin jin kunya haka?"

Ta kaɗa kai ba tare da ta sake dagowa ba.

Alhaji ya sake tambayarta.
"Wani yaro ne ɗaya daga cikin gidan? Ko cikin jikokin gidan ne?"

Ɗagowa ta yi, fuskarta na nuna alamar rashin jin daɗin tambayar, har da 'yar ƙaramar harararta.

"Mai Unguwa fa nace Baffa!"
Gyara zama ya yi sosai don bai fahimci wani Mai Unguwar take nufi ba.

"Mai Unguwar Yankin mai Ludaya ƙarama kike nufi kokuma yaronshi da ake cema Mai Unguwa?"

Kaɗa kai ta yi ba tare da ta bashi amsa ba.

"Ban fahimta ba, ki buɗe baki ki yi min bayani."

"Baba Mai Unguwa Rabi..."

Bata kai ga karasawa ba, ta miƙe a guje ta yi ɗaki.

Hannu ya shiga tafawa yana salati yana sanar da Ubangiji.

Su kuma yaran sai dariyar Abullen suke yi.

"Alhaji lafiya kake ta jero salati?"
Hajiya Sabuwa ta tambayeshi

"Ina fa lafiya?"
"Me ya faru?"
"Ban taɓa sanin cewar Ilu baya da hankali ba sai yanzu. Kin san wa zai aura ma yarinyar nan kuwa?"

Girgizar kai ta yi, kafin ta amsa

"A'a."

Tsaki ya ja cikin ɓacin rai kafin ya ce,

"Tsoho ne fa da ya kusa ba shekaru ɗari baya."

Kirji ta buga ta ce,
"Mun shiga uku! Shi ko Ilu me ya yi mishi daɗi haka da zai ɗau 'yar jaririyar 'ya ya ba wannan tsoho?"

"Rashin tunani da rashin hankali mana."
"Gaskiya Alhaji gara tun wuri asan abun yi. Ni kam da haƙura aka yi da auren nan ta yi zamanta anan, a sama mata makaranta."
"Hakan ma za a yi, ba sai sun ga ƙafarta a goben bama."
"A, to. Ai wannan abu da cutarwa. Duka-duka Zainab ɗin nawa take da har za a yi mata aure?"
"Kin san mutanenmu ai, yanzu idan kin je can ma za ki samu ana ƙorafin girmanta."


_Ummyn Yusrah_

*ABULLE TA MAI UNGUWA*

*HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*

     _Ummyn Yusrah_


_25_

"Lallai akwai su da yi ma yaro auren wuri."
   "Ai ba auren wurin ne ma damuwa ba, da ya zaɓa mata tsaranta ai ba damuwa. Amma a ce  ya ɗauki yarinya ya danƙata hannu tsoho ai abun bai yi ba."
   "Kuma fa kaga ita yarinyar kamar tana son shi, ji wani sunne kai da take ta yi ita a dole kunyar nan."
    "Koma menene ita dai ta sani na riga na gama magana."

Ya kalli Afreen ya ce,
"Anjima ka kaita taga gari, kasan su basu saba zama waje ɗaya ba, tanan za a ɗauke hankalinta."

"To, Daddy! Amma ka faɗa ma Labano ta daina kyararta."

Hajiya ta ce,
"Waye kuma Labano?"
Dariya yake yana nuna Lubna da hannu
"Wai Lubnan ce ta dawo Labano? Wannan suna daga ina kuma?"

"Daga wajen Zainab, wannan ai kafin ta saitu sai ansha fama. Daddy wai kai ma haka ka yi ne farkon zuwanka Jinjin?"

Filon dake kan kujera ya ɗauka ya jifeshi da shi yana faɗin,

"Ka ci gidanku! Kana raina mana 'yan gari ko? Can zan kai ku ku yi wata ɗaya ku saba da 'yan uwa."

Afreen har da murnarshi

"Eh, wallahi Daddy ina son zuwa ƙauye."

Labano kuwa yamutsa fuska ta yi, ta turo baki tana faɗin

"Daddy har wata ɗaya? Ni dai ba za ni ba. Sai dai ko Afirij."

Duk suka sa dariya, Hajiya ta kalli Alhaji

"Ni ko Lubna za a ba Mai Unguwar tunda ta girmi Zainab ɗin?"

Kwaɓe fuska ta yi, kamar zata yi kuka, ta ce

"Mommy!"

Sai kuma ta miƙe ta nufi hanyar ɗaki.

Afreen da ke ta kwasar dariya harda kwanciya kan kujera ya ce,

"Labano ta Mai Unguwa! Kuma fa za su dace sosai Mommy."

Juyowa ta yi, ta jefomishi remote ɗin tibin da ke hannunta.

"Wayyo Allah matar Mai Unguwa zata yi min illah."

Ya sake ƙular da ita, Daddy ya ce

"Ya isheka, zo abunki 'yar Daddy ba mai yi miki wannan aikin ina raye."

Da gudu ta shige ɗaki abunta.

"Sai ki je ki rarrasheta, kin santa ai idan ta kumbura sai an nemi allurar da za a soka mata ta sace."

"Ai Lubna ban san wace irin yarinya ba ce, bata son mutane ko kaɗan ga ta da ƙin 'yan ƙauye, ko don ba ta zuwa ne yasa hakan?"

"Zata daina ne, yanzu duk lokacin da aka yi hutu zan riƙa kai su akai-akai."

"Gaskiya ya kamata kam."

Ta kalli Afreen da tun ɗazu ke kwasar dariya ta ce,

"Kai kuma abun na ya samu ko? Ba a taɓa ganin dauriyarka sai ta ɓaci. Tashi ka je ka shirya idan zaku fita ku sauƙeni gidan Suwaiba in dubata da jaririyarta."

Ciki ya shige ya bar su suna ci gaba da tattaunawa.

Sai ƙarfe uku aka gama abincin rana, lokacin duk yunya ya addabi Abulle, tun tana shan ruwa yana riƙe mata ciki har ya dawo da ta sha jimawa sai banɗaki.

****

"Daga ɗauko shara ka je ka zauna, wata yarinya ta yi ta jiran zuwanka zai ta tsinci kwalin sabulu ta yi jere baka fito ba."

"Bari kawai Ɗalliti, na yi zaton sharan kaɗan ne ashe da yawa, na yi tunanin in ce ka shigo sai naga gara ka zauna ko za mu sami masu saye kada mu ɓata lokaci a waje ɗaya mu zo kuma bamu sami komai ba."

"Gaskiya! Kuma ka yi farar dabara don ina nan mutane biyu ma sun zo sun saya."

"Kaga ai da yanzu ciniki ya wuceemu, don ma naga layin nan ba ba irin layin masu sayen gauta bane."

"Yo, Hamisu gautar abinci ne da mutane zasu yi ta jidarshi? Ina jibi idan na tafi gida in zan dawo zan nimo wasu 'yan kuɗaɗen in sake jarraba wani sana ar."

"Allah ya kai mu. Barin kai wannan ɗin idan na dawo sai ka shiga kaima ka ɗebo."

"To, ba damuwa."

Ya tura baron zuwa wajen da ake tara shara.

"Na yi tunanin fa kai zaka zaga da gautarnan, ni sai in ƙarasa kwashe sharar kawai."

Hamisu ya faɗa ma abokinshi lokacin da ya dawo daga kai shara.

"Allah ko? To inaga kuma za a yi fa! Kada mu taru mu zauna waje ɗaya."

Ya faɗa lokacin da ya ɗaura tirenshi a kai, ya miƙo hannunshi Hamisu ya ɗoramishi nashi tiren.

Har ya yi gaba ya juyo ya ce,

"Idan ka gama kawai mu haɗu wajen Goshi mai abinci."

"To, ba damuwa."

*Ummyn Yusrah*

*ABULLE TA MAI UNGUWA*

*HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*

_Ummyn Yusrah_

_Ina taya Haziƙan Marubuta murnar kammala littafinsu, mai suna TA FI BAGARUWA IYA JIMA. Zeety, Ummyn Yusra, Beauty Queen. Allah ya kara hazaƙa ya ƙaro kaifin ƙwaƙwalwa._

_Ruƙaiya Haroun (Maman Nour) ina tayaki murnar kammala littafinki mai suna RUƊANIN RAYUWA (Ƙalubalenmu a yau) Allah ya kara hazaƙa da fikra._

_26_

Bayan sun ci abinci, sun yi sallar la asar ne, Abulle ta je ta tsalo wanka. Kwalliya sosai ta yi cikin atamfarta riga da zani da ɗankwali mai kalar koriya da ruwan ɗorawa.

Ta shafe fuskarta da fauda, ta ɗauko ƙwalli ta yi ɗigo uku a saman goshinta, biyu a ƙasa ɗaya a sama. Haka ta yi a gefen kumatunta na hagu da dama da kuma ƙasan haɓarta.

Ta sanya jan jambaki a leɓenta ta sa kwalli a cikin idanunta. Sabon silifas ɗinta mai soso ta sa ta sanya hijabinta, sai gata ta fito cas! Kamar ranar sallah.

Ta fi minti goma tana kallon madubi, tana ƙare ma kanta kallo, domin ita kanta ta san yau ta yi kyau! Idan ta juya furkarta gefe ta yi fari da idonta, sai ta sake juyawa ɗaya gefen ta sake fari da idanun. Tana yi kuma tana murmusawa.

"Na shiga uku! Wannan wani irin hauka ne? Kin gama ƙwaɓa fuskarki wai ke kin yi ado, kuma kina nufin a haka za ki bimu? Gara ma ki koma banɗaki ki je ki wanke fuskar nan wallahi idan ba haka ba sai dai ki zauna." Lubna ta faɗa lokacin da ta fito daga wanka.

Kallo ta yi mata, irin mai nuna amar kin taƙura min ɗin nan, 'Ba ke aka ce ki fita da ni ba, kama albarkacin Hajiya ne ta ce ki shirya ku je gidan barkar haihuwa.'

"Afirij zan bi ai! Ke kuma Hajiya za ki bi."

Ɗagowa ta yi daga shafa man da ta fara, ta yi mata kallo na sakan biyu, kafin ta ce,

"Owo! Shine baza ki goge fuskar ba kenan? Ki barshi to don Allah, zamu ga wa za ki bi. Mara kunya kawai. Ana magana kina ba mutane amsa."

Cike da haushi ta nufi bayan gidan ta wanke fuskarta. Tana fitowa ta nufi hanyar fita.

"Zo nan."

Lubna ta ce da ita, har ta kara gaba sai kuma ta juyo ta dawo.

Kaya ta miƙo mata ta ce,

"Ki cire na jikinki, ki sa wannan."

Murmushin takaici ta yi, zuciyarta na faɗin

'A rashin sani, baƙo ya sha ruwan wanka. Ki bi a hankali, idan na bauɗe sai kin raina kanki Labano, sai kin san Abullen Inno ba baya bane.'

Karɓar kayan ta yi, ta cire nata ta sa. Doguwar riga ne, da ɗan mayafinshi. Ta rasa yadda zata yi da mayafin, don santsi ne da shi, kawai sai ta tattaro ta ɗaure a wuya. Ta yi waje.

****

"Kai! Na aikatu sosai yau, amma na fanshe gumina fa."

Hamisu ya faɗa lokacin da suke zaune a ƙarƙashin biya.

"Gaskiya kam! Nima da na gama zagawa, na je gurin Goshi na ci abinci na jima sosai a wajen kafin ka zo."

"Bari ka gani Ɗalliti!"

Ya faɗa yana ciro kuɗin da ke cikin aljihun rigarshi.

"Ka gansu."

Ya nuna mishi ɗari biyar-biyar guda uku.

"Dubu ɗaya da ɗari biyar ya bani, da abinci mai yawa. Ya kuma ce duk bayan kwana biyu in rinƙa zuwa ina zubar da shara da share musu harabar gidan sabida furannin da ke zuba." Ya kare maganar yana kunce wani baƙin leda da ya taho da shi.

"Ga naka abincin, ni na ci na ƙoshi a can."

"Kai mutumina!"
Cewar Ɗalliti, lokacin da yake miƙa ma Hamisu hannu suka tafa, fuskarshi cike da annuri ya ci gaba da faɗin.

"Ka ce dai mun shiga wannan layin a sa a?"
"Ba laifi, mun taki babbar sa a. Ya kasuwar taka?"
"Ba laifi, na ɗan taɓa ciniki."
"Mun gode Allah!"
Janyo ledar abincin ya yi, ya wurga wani ƙaton yankin nama a bakinshi, sannan ya ce,
"Niko Hamisu me zai hana mu kama ɗaki a gidan Malam Bukar, zai fi mana sauƙi da kwanan ƙofar shagunan mutane ko cikin rumfar kasuwa ko? Kaga kullum Da u, cikin kai mana hari suke, sai ka yi nisa cikin barci wani ƙaton ya mirginaka ya kwashe abunda da wuni kana nema."

Ajiyar zuciya Hamisu ya yi, da godiya ga Allah da ya haɗashi da abokin ƙwarai, mai son ci gabanshi. Bai da ƙyashi ko hassada.

"Kuma fa ka kawo shawara mai kyau wallahi. Amma kana ga zamu iya biyan kuɗin?"

"In Allah ya yarda zamu iya. Dubu huɗu ne fa a wata guda, kasan ɗakunan ba wani fasali ne da su ba."

Dariya Hamisu ya yi, ya ce,
"Allah na tuba! Wa ke duba wani fasali Ɗanliti? In dai asiri ya rufu ai shi ke nan."

"Haka ne kuma."

Ya faɗa yana ciro kuɗi daga cikin ramin zariyar wandonshi.

"Ga dubu biyu nan, ka kawo na wajenka mu haɗa sai ya bimu bashin ɗari biyar ko?"

"Kawo dubu guda a wajenka ka gani."

Ya karɓa, ya haɗa da na aikinshi, ya ciro wata tsohuwar dubu ɗaya a ramin zariyar shi shima ya haɗa.

"Kaga sun cika dubu uku da ɗari biyar, ka adana dubun kaga tafiya ce jibi a gabanka, ba lallai ka sake samun wasu kuɗaɗen kamar wannan a gobe ba."

"Ikon Allah! To, ai na gama shirye-shiryena, na sai musu omo, sabulu, manshafawa, da farin magi. Burodi kawai dama ya rage in saya."

"To, ka gani ai. Ko mu hakura har ka je ka dawo?"

"A a! Daga yanzu ai duk aikin da ya samu yi za mu yi. Kaga tanan zamu riƙa samun wasu kuɗaɗen."

"Allah ya taimakemu, yanzu ina muka dosa?"

" 'Yan kura za mu, mu yi haya kagani mu ɗebi ruwa mu shigar unguwannin da suke da ƙarancin ruwa ka gani."

"Hhhhhh! 'Yan Garuwa kenan?"

"Ƙwarai!"

Ya faɗa yana wanke hannunshi da guntun fiya watan da ya sha.


_Ummyn Yusrah_

*ABULLE TA MAI UNGUWA*

*HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*

_Ummyn Yusrah_

_27_

Kai tsaye fallo ta dawo ta zauna, zuciyarta sai ƙuna yake yi mata. Walaƙanci na ɗaya daga cikin abinda ta tsana, sai dai ta lura wannan Lubnar mutuwar 'yar walaƙanci ne. Amma, ba komai. Gobe i yanzu ma ta yi nisa da garin.

" 'Yammatan mai ludaya an sha kyau."
Bata ɗago kai ba, murmushi kawai ta yi. Sai dai idan ka dubeta zaka iya hango ɓacin rai maƙale a fuskarta."

"Yaya ba ki yafa mayafin ba, kika tukuikuyeshi a wuya?" Afreen dake tsaye ya sake tambayarta.

"Ƙauyanci mana. Kasan ko yaya baƙauye yake sai ya nuna halin nashi."
Lubna ta faɗa lokacin da ta iso falon tana ɗaura ɗankwali.

Kallon takaici bita da shi. Yanzu kam ta gama gano tsanarta ce ƙarara a fuskar Lubna.
"Hummm! Na gode Allah ina da tushe ba a kwararo aka tsintoni ba. Ki sani ko yaya mutum yake daraja ce da shi. Ɗan adam ba abun walaƙantawa bane. Idan ma kin yi haƙuri, gobe iyanzu babu ni a gidan nan."
Harzuƙowa ta yi, ta nufota gadan-gadan tana faɗin,

"Iye! Ashe rashin kunyar naki har ya kai haka ne? Har kin kai ki faɗamin magana?" Afreen da ya tare ta ne ya ce,
"Haba Anti Lubna! Abin da kike yi mata bai dace ba wallahi."

Kallonshi ta yi rai ɓace ta ce,
"To, mara kunya! Sai ka koyamin abin da ya dace." Tana kaiwa nan ta ja tsaki kan kujera ta zauna.

Ya juya da niyyar yi ma Abulle magana yaga bata nan. Da sauri ya nufi ɗakin Lubna.

Ji alamar motsin tafiyar mutum yasa ta yi saurin sanya bayan hannunta ta goge hawayen da ya wanke mata fuska.

Shigowa ɗakin ya yi, ganin ta canza kaya yasa shi tambayarta.
"Ya naga kin canza kaya kuma mu da zamu fita?" Ba tare da ta ɗago kai ta kalleshi ba ta ce,
"Ku je kawai."
"Me ya sa?
Ya sake tambayarta
"Akwai abin da zan yi ne."
"Ban yarda ba! Abin da Anti Lubna ta yi miki ne ya ɓata miki rai ko? Ki yi haƙuri kada abun ya dameki, rashin fahimtar juna yasa hakan da zarar kun kun fahimci juna komai zai daidaita ki yi..." Bai kai ga ƙarashe maganar ba muryar Lubna ta katseshi tana faɗin,

"Kai! Dallah ka zo, ka bar mutane tsaye a waje suna jiranka ka zo nan ka yi zamanka. Idan ba za ka kai mu ba ka bani makullin."

Tana kaiwa nan ta juya.

"Ki yi haƙuri kin ji? ki sako mayafinki ki zo mu tafi. Muna jiranki."
Ya fita.

Yana fita ta yamutsa fuska, ta ce
"Ko maton ubana Ilu ne, ba zuwa zan yi ba. Idan kun gaji da jira sai ku yi gaba."
Jakar kayanta ta janyo ta zazzage kayan ciki duka, ta shiga ɗaukarsu da ɗai-ɗai tana sake naɗesu, duk da a naɗen suke.

"Wallahi Mommy mu tafi, ta sanfa ita muke jira don iskanci ta je ta yi zamanta. Sama da minti goma muna zaman jiranta." Lubna dake zaune a bayan moto kusa da Hajiya ta faɗa.

"Fita ki je ki dubota. Meyuwa wani abun ya tsaida ita ko batasan mun fito ba." Cikin yanayin shagwaɓa Lubna ta kalli Hajiyar ta ce, "Mommy!"

Itama kallonta ta yi, fuskarta ba alamar wasa ta ce, "Eh!"
Ganin yanayin Hajiyar yasa ta fita da sauri badon ta so ba. A sonta a aiki Afreen.

Tana zaune a ƙasa, ta jingina bayanta da gado. Ta gama naɗe kayanta ta mayar cikin jaka, hotunan da ta ciro take kallo, wasu da ƙawaye, wasu 'yan uwa, wasu kuma ita da Hamusu. Jin motsin tafiya yasa ta yi saurin turasu ƙasan gadon ta rarumo jakarta tana ƙoƙarin jan zif ɗin ne aka buɗo ƙofar.

Fuskarta ba annuri ta leƙo ta ce,
"Malama ke fa muke jira, kin wani nemi waje kin zauna."
"Ku je, ba zani ba." Ta bata amsa
"Ya fi miki." Ta juya ta fita, ita kuma ta janyo hutunanta ta mayar cikin jaka ta zuge zif ɗin ta ɗauka ta koma ɗakin da tun farko aka yi musu masauƙi ita da Inno.

"Ina Zainab ɗin?" Hajiya ta tambayeta ganin ta shigo tana jan ƙofa zata rufe
Fuskarta a sake ta ce,
"Kanta ke ciwo ashe, na ce ta zo mu tafi, ta ce ba zata iya ba, shine na bata magani ta sha ta kwanta."
"Subhanallah! Ta sha maganin ta kwanta dai ko?"
"Eh!"
"Mu je mu dawo da wuri sai in dubata."
"Gaskiya kam, ta riga ta kwanta kada ki je yanzu ta tashi ciwon kan ya ƙaru."

Hannu ta miƙa daga baya ta zare abin sauraron sautin da Afreen ya toshe kunnuwanshi da shi, ta ce
"Mu je ko?" Ta faɗa tana ɗaga mishi gira
"Ina Zainab ɗin kuma?"
Ya tambaya lokacin da ya juyo.
Harara ta zabga mishi,
"Kanta ke ciwo ta sha magani ta kwanta."
Kai kawai ya gyaɗa, don yasan kwanan zancen, sai dai bai ɗauka yarinyar na da zuciya har haka ba.
Zama ya gyara, sannan ya ja suka tafi.


*Ummyn Yusrah*

*ABULLE TA MAI UNGUWA*

*HAZAƘA WRITER'S ASSOCIATION*

     _Ummyn Yusrah_

_Matso kusa ku ji! Ko kuna da labarin shahararren kamfanin nan mai suna *RANDAWA MEDIA CONCEPT* kuwa? Kamfani ne ɗaya tamkar da dubu. Aiki cikin aminci, inganci, rangwame da kuma rahusa. Ku dai kawai ku tuntuɓemu ta wannan number domin samin biyan buƙata cikin sauƙi 08062176520. Ga kaɗan daga cikin aiyukanmu_
_1. Waƙar biki, suna, siyasa, ring tone da sunanki/ka, waƙe masoynka/ki, miji ko mata._
_2. Calendar da sticker  biki, suna sauƙar karatu, ko dai na wani abun._
_3. Tallata haja ko wakar ma aikata ko company._ da dai sauransu
_Kai tsaye ku tuntuɓemu ta numbermu dake sama don samun aiki cikin rangwame da rahusa, sai kun zo._

_28_

Ada baya tana son zuwa cikin garin Jinjin, sai dai a yanzu da take cikinsa duk ta ji ya fita mata a rai. Ta tsani garin gaba ɗayanta, ko kaɗan ba zata iya rayuwa cikinta ba. Gara ta koma inda ta fi wayo, gurin da aka san kimarta da darajarta.

Sai daf magriba Hajiya suka dawo. Kai tsaye ɗakin Lubna suka nufa dukansu, bata ciki, har banɗaki tasa Lubna ta duba bata ciki.

"Ina ta shiga to? Kika ce ta kwanta ɗazu, shigowarmu kum bata falo."

Hajiya ta tambayi Lubna da ta yi tsuru-tsuru da ita. Cike da tsoro ta ce,
"A nan fa na barta tana kwance."
Ta faɗa tana nuna gefen gado

"Barin dubata ko tana kicin
End Ads