rame sosai, amma wannan kyawun yana nan sai dai babu gayun, kuma shekaru sun fito sosai a fuskarsa harda strings of furfura a gashin sa. Ta gane kayan jikinsa, sune kayan da yake sanye dasu ranar da aka kamashi a airport, she can remember yadda ya fito daga arrivals cikin yana taku dai dai yana jin duniya duk a tafin kafarsa ga kyakykyawar Fauziyya a gefensa but yanzu da ta kalle shi bata ga komai daga cikin characters din wancan Saghir din ba. He looked calm and very different.
Sadauki ne yayi knocking a tagar da Subay'a take, ta dago tana kallonsa sai yace "Subis ga Daddy nan" ta mike da sauri ta kalli kofar prison din, tana hangoshi sai ta kama kokawa da handle din motar sai Diyam ta bude mata central lock tana dariya. Ai kuwa nan take ta bude ta fice daga motar a guje, Diyam ma ta bude ta fito tana cewa "careful Subay'a akwai titi fa". Daga tsallake Saghir ya hango fitowar ta, ya kuma lura da yadda tayo kan titi da gudu dan haka sai shima ya taho da sauri gurin ta zuciyarsa tana bugawa. A tsakiyar titi suka hadu, ya daga ta sama amma sai ya kasa juyi da ita ya sauke ta yana haki yace "kinyi girma Subay'a, Daddy kuma bashi da karfi" sai ta rungume ƙafafuwan sa tana murmushi.
Ya kamo hannunta suka karasa tsallako titin zuwa inda su Diyam suke a tsaye. Unintentionally hannun Diyam ya sauka akan cikinta tana kallon Saghir, sai taga ya kalli cikin sai kuma tayi sauri ta dauke hannun tana sunkuyar da kanta. Yayi murmushin takaici Yace "amarya" sai ta gaishe shi ya amsa yace "a sake min godiya gurin Mr Abatcha. Na goge sosai Allah ya bar zumunci" ta gyada kai a hankali tace ameen tana kallon Sadauki wanda yake ta danne danne a waya kamar baya jin me suke cewa. Sai ta kalli Saghir tace "congratulations. Allah ya kiyaye gaba" daga haka ta bude mota ta koma ciki. Sadauki ya dago kansa yana kallon Saghir ya nuna masa mota yace "Bismillah, sai mu ajiye ka a gida ko?" Sai Saghir ya kalli Diyam, ya hadiye wani daci a ransa ya girgiza kai yace "no, thank you. Kar in takura muku maybe akwai inda zaku je. Bara in hau napep kawai" Sadauki ya daga kafada kawai, sai ya tare masa napep din ya kuma biya kudi sannan ya yi wa mai adaidaitan kwatancen sabon gidan Alhaji Babba, tunda Saghir din bai sani ba.
Saghir yace da Subay'a "zaki bini gidan Alhaji?" Ga mamakin su sai ta kalli su Diyam ta kuma kallonsa sannan ta girgiza kai tace "no, Aunty Asma'u tace yau Uncle Bassam zai zo, kuma na bashi sakon abubuwan da zai taho min dasu in zai zo, ka ga kar yazo bai same ni ba" Sadauki ya bude ido yace "Subis akwai zarar magana sai kace wata babba" Saghir yayi murmushi yana kallon inda Diyam take yace "gado tayi ai". Har adaidaitan zai ja sai Subay'a tace "Daddy zan kawo maka ziyara gidan ka".
In silence suka bar gurin kowa yana lissafe lissafe a zuciyarsa. Sai can sannan Sadauki yace "ba zan bashi aiki ba kamar yadda kika bukata. Bana son drama, nafi sonsa a nesa damu" bata ce komai ba, ya cigaba "amma zanyi masa komari ya samu kudin sa na gurin Kabir" Diyam tayi sauri ta kalle shi tace "kudin ka dai, ai kudinka ne" ya girgiza kai yace "nayi signing takarda cewa na bar masa kudina daya dauka, so legally yanzu kudin sa ne ba nawa ba. I have already talk to my lawyers, za'a siyar da kadarorin Kabir maybe za'a samu part of kudin amma nasan ba za'a samu gaba daya ba" Diyam taji dadi sosai a ranta tana yabawa kyawun zuciyar Sadauki, kamar yadda ya taba fada mata shi fire ne da ice, duk da wadda kazo dashi za'a tarye ka.
Tayi masa godiya sosai sannan yace "kin san wani abu? Ni da Saghir are alot alike" ta bude ido dan ita bata ga hadin su ba bayan kasancewar su musulmai kuma half fulani tace "ta yaya?" Yace "kinga ni da shi duk only sons ne a gurin iyayen mu. Kuma iyayen mu suna son mu sosai sannan sun nuna mana soyayya in their own different ways. Duk kanin mu iyayen mu sun bamu kudi, the only difference is yadda muka yi da kudin da suka bamu. Sannan kuma duk muna sonki" ya fada yana kallon ta, tayi saurin girgiza kanta tace "he doesn't" yace "he does. I saw it in his eyes yanzu da yana kallon ki"
Tayi saurin kawar da maganar ta hanyar cewa "kuma duk ku biyun kuna da kanwa mai suna Murja" yayi dariya yace "ni kanwa ta Murjanatu sunan ta ba Murja ba, kuma ni nafi shi son kanwa ta" tace "ita kuma duk duniya gani take yi kafi kowa kinta" and they laughed together.
*************************
Saghir ya juyo yana kallon Subay'a, yana kallo Sadauki ya kama hannunta ya bude mata kofa ta shiga mota sannan shi kuma ya zagaya ya zauna kusa da pregnant Diyam. Yayi sauri ya rintse idonsa tare da dafe kansa yana jin hawaye yana zuwa idonsa. Bai dauka har yanzu Diyam tana da gurbi a zuciyarsa irin haka ba, ya dauka ba zaiji komai ba inya ganta musamman saboda kokarin da mr Abatcha yayi masa, amma ita zuciya bata da linzami dole ya ja baya dasu ya daina ganinsu, ko kuma abinda yaji din yana da alaka da yadda Diyam din ta zama? Irin kyawu da cikar halittar da tayi? Wai hakan na nufin da ace ya kula da ita tsahon shekarun da suka yi a tare da irin haka zata zama kuma maybe da zata so shi? Lallai gaskiyar hausawa da suka ce tun ranar gini tun ranar zane, shi kuwa nasan ginin ya bushe dole sai dai ya hakura da zanen ko kuma ta sake sabon gini, sabon ginin wata rayuwar.
But with who? Wannan wata tambaya ce for another time. Maganar da Subay'a ta fada ta dawo masa zuciyarsa "zan kawo maka ziyara gidan ka" wanne gidan? Shi fa yanzu ko gidan kansa ba shi da shi, wayake ma maganar gida, shi ko kwandala bashi da ita. Bashi da komai sai freedom dinsa, kuma ya dauki freedom din nasa ya zama another chance at life. Chance din kuma da insha Allah zai yi amfani dashi sosai yadda har sai mutane sunyi mamakinsa. Yadda har sai iyayensa sunyi alfahari da shi. Iyayen da a wancan lokacin ya wofantar ya wulakanta, abinda yake tunanin shine dalilin zuwansa inda yaje ba wai Diyam ba.
Maganar mai napep ce ta dawo dashi hankalinsa, yace "yallabai munzo" ya leko dakansa yana kallon gurin yace "nan ne?" Mai napep yace "nan dai yayi min kwatance, yace jaen layin shago tara, gashi nan kuma har mun kusa fita daga layin tunda mun fara hango diga. Sai dai ka sauka ka tambaya" Saghir ya sauka yana kallon gurin, not that bad. Mai adaidaitan ya miko masa dari biyar yace "dubu biyu ya bani, ga dari biyar ka sha ruwa kai ma" Saghir ya karba harda yi masa godiya sannan ya tafi gurin wasu mutane su uku da ya hango a kasan bishiya ya gaishe su yace "dan Allah tambaya nake yi, gidan Alhaji Babba, bai dade da dawowa unguwar nan ba" duk suka ce basu sani ba, yayi gaba ya cigaba da tambaya amma babu wanda ya sani sai ya juyo ya fara retracing ta inda suka shigo yana yi yana tambaya, ga rana gashi dama jikin sa duk babu karfi.
Da kyar ya samu wanda yace "inda akayi biki watannin baya?" Da sauri Saghir yace "eh" sai aka hada shi da yaro suka koma can inda ya baro, suka je har gaban wani gida sannan yaron ya nuna masa ya juya. Ya tsaya yana kallon gidan, a tsahon rayuwarsa bai taba tsammanin duniya zata yi juyawar da har nan gidan zai koma shine gidan baban shi ba, gidan ma kuma gidan haya, gidan hayar ma kuma Diyam ce ta ke biya masa.
Ya shiga soro yayi sallama, Hajiya ya hango ta fito daga wani guri daya ga kamar kitchen tana amsa sallamar hannunta rike da wuka tana goye da wani yaron da bai sani ba a bayanta. Ta yarda wukar tana kiran sunan Alhaji, Alhaji ya fito, Hajiya yalwati ta fito, sai ga yaran gidan suma sun fito daga wani daki duk suna binsa da ido. Shi ya karasa shigowa, ya tafi gaban mahaifinsa ya durkusa amma sai ya kasa gaishe shi sai kuka ya kwace masa. Alhaji ya sunkuya gabansa ya jawo shi jikinsa ya rungume shi shima yana hawayen yace "bansan yau zasu fito da kai ba Saghir, da ko ba zan iya zuwa da kaina ba da sai in gaya wa mahaifiyarka ta je ko ta tura aje a taho da kai" Saghir ya goge hawayen sa yace "Mr Abatcha ne yaje ai, dashi da Diyam da Subay'a" ya fada yana jin dacin zuciyar dazu yana dawo masa. Alhaji yace "madallah dasu. Allah yayi musu albarka ya jikan Usman".
Nan fa gida ya rude da murnar dawowar Saghir, dan ma yanzu duk yaran babu saura kadan. Hajiya Babba ce ta kama shi ta kaishi daki, Hajiya yalwati kuma ta dora masa ruwan wanka, alhaji kuma ya aika a siyo masa nama da lemo kafin a gama abinci. Babu laifi suna cikin rufin asirin su duk da cewa alhaji har yau bai kuma gwada kasuwanci ba amma matansa suna yan sana'o'in su sannan yayansa mata da suke aikin gwamnati suna kokari gurin taimaka musu sosai, haka ma surukan gidan lokaci zuwa lokaci suna aiko musu da kayan abinci ko kuma suttura.
A dakin Hajiya ya huta, naman da Alhaji ya siyo masa sannan yayi wanka ya chanja kaya zuwa wanda Hajiya ta ajiye masa akan gado. Sai ta kunto yaron bayanta ta mika masa. Kallo daya yayi masa yasan waye, sai kawai ya ajiye shi a gabansa ya sunkuyar da kai, tace "sunan babanku ne dashi, Jawad ake ce masa" yaron ya rarrafa da sauri yabi bayan Hajiya yana kuka alamar bai san shi ba.
Dakin da yake soro, wanda kuma yake da kofa a waje shi dama Alh yasa aka gyara tun sanda yaji labarin dawowar Saghir gida. Aka shimfida carpet aka saka katifa, wardrobe, da kuma standing pan. Nan ne ya koma dakin Saghir.
Kwanan Saghir biyar ya warware, duk da dai babu inda yake fita sai yan'uwa da suke ta zuwa yi masa murna. Inna ma tazo ita da Asma'u da Subay'a, suka kuma bar Subay'a anan tayi weekend tare da mahaifinta da kakannin ta. A ranar ne Alhaji ya kira shi dakinsa. Suka zauna sai ya dauko wata leda ya miko masa, Saghir ya karba ya bude sai yaga kudi a ciki, ya zaro ido "Alhaji kudi ai, kudin menene wannan?" Alhaji yace "kudi na ne, sauran kudin gida na ne da kuma abinda na samu daga gadon Usman, su nake ta ajjiye dasu da niyyar duk ranar da ubangiji ya sake baka dama a rayuwa ya saka ka fito daga prison nima zan sake baka dama in baka su kayi jari" Saghir yayi saurin girgiza kansa hawaye yana bin idonsa yace "Alhaji kar kayi haka, ka bani kudi sau ba adadi ina salwantar wa, kai ma kana bukatar kudin nan alhaji, kana da iyali kaima. Ka rike kudinka alhaji ka kula da kanka da matanka da kanne na" Alhaji yace "da wanne karfin Saghir? Ni ai tawa ta kare, karfi na ya kare, dan haka kai na dora wa wannan nauyin ka juya wannan kudin ka kula da kanka sannan ka kula dani da iyayenka da kannenka, kuma ka cigaba da kula dasu ko bayan rai na ne".
Saghir ya karbi kudin ya rike yana jin nauyi a zuciyarsa "anya kuwa akwai soyayya sama data iyaye?"
Alhaji yace "akwai kuma wata magana da nake so muyi. Ina so ka kawo karshen rashin jituwar da take tsakani na da danuwana, ina son ka auri Suwaiba" ya dago kai yana kallonsa, Alhaji ya gyada kai yace "ta inda ake hawa tanan ake sauka. Tunda kuka bata dan haka ku zaku gyara". Sai Saghir yaji Fauziyya ta fado masa a ransa. Bayan ya bata takardarta sun rabu, daga baya sai ta koma tana gaya masa cewa tana da cikinsa, ta kuma ce zata haifi cikin za kuma ta jira shi as long as bata samu miji ba har ya fito sannan kuma yana da sha'awar mayar da ita. Bayan ta haihu kuma ta kai masa babyn ya gani. And after seeing Subay'a rike da hannun Sadauki, baya jin zai kuma barin wata yar tasa a wani gidan. Dan haka indai Fauziyya bata yi aure ba to sai dai ya hada su ita da Suwaiba.
Wata daya bayan nan Diyam tazo yi musu sallama zata koma Oxford, England. Washegarin zuwanta kuma alert ya shigo masa. Ya bude ido yana kallon kudin cike da mamaki ya tafi da sauri ya nunawa Alhaji. Alhaji yayi murmushi yace "Diyam ta gaya min jiya, kudin da Kabir ya gudu dasu ne aka dawo maka dasu. Zabi kuma ya rage naka kasan me zaka yi dasu".
Abinda Saghir ya fara yi shine ya dauki kudin da Alhaji ya bashi ya sayi gida madaidaici amma me kyau. Ba shine ya tare a gidan ba, Alhaji Babba da iyalin sa ne suka tare. Sai kuma ya sayi karamin fili a kusa da gidan a matsayin nasa "sai in zauna a kusa daku yadda zanfi jin dadin kulawa daku" next sai yaje har gidan Kawu Isa ya durkusa ya bashi hakuri sannan ya nemi ya bashi auren Suwaiba. Sai kuma ya tafi gidan su Fauziyya itama ya nemi auren ta. Amma duk kan su yace sai shekara mai zuwa idan ya samu nutsuwa sosai.
Daga nan sai ya tafi kantin kwari, tsofaffin shagunan Alhaji wadanda wuta ta cinye babu komai sai ginin, shima ginin duk ya mutu an sace kwanukan. Cikin kwanaki kadan ya tayar da ginin su, yayi komai ya saro kayan duk da yasan Alhaji yana siyarwa ada da kuma kayan da yasan zamani ya zo dasu ya zuba a ciki. Sannan ya nemo tsofaffin yaran Alhaji wadanda suke kular masa da shagunan a da ya dawo dasu dan su suka san kan kasuwa, shi kuma ya zauna cikinsu dan shima ya fahimci harkar.
Watanni kadan abubuwa suka warware wa Saghir, ya hada kudin neman aure ya kai gida biyu aka saka masa rana watanni takwas masu zuwa za'ayi duk a tare, sannan kuma ya fara ginin gidan sa a hankali. Gidan da yake da yakinin zai zamanto tushen sabuwar rayuwa a gurin sa.
****************************
A lissafin Sadauki so yayi in sun bar Nigeria su fara tafiya Canada suyi kwana biyu tukunna, amma Diyam ta tubure masa ita bata son zuwa, ya gane abinda yasa bata so, ita kunya take ji ake ganin ta da ciki. Yayi dariya "to wai ke banda abinki, ni fa banga abin kunya anan ba, kowa ma fa yana yi" ta juya masa baya tana kallon Subay'a a cikin swimming pool tace "kuma kawai sai in je gidan inyi ta yawo da ciki suna kallona?" yace "baiwar Allah, idan baki je da ciki ba in kika haihu dai ai dole zasu ganki da dan ko? Ko shima cewa zaki yi ba ke kika haifa ba?" Tace "ai kuwa in naje gidan da baby to har in bar garin ba zan dauke shi ba" ya rike baki "to waye zaiyi feeding dinsa?" Tace "sai ya sha madara" ya kwanta akan camp bed din da yake zaune akai ya rufe ido yace "you are impossible Diyam, ke fulatancin kamar a kanki ya kare" ya sake cewa "kiyi addu'a to, kar a saka bikin su fanna kafin ki haihu, sai muga yadda zakiyi da cikin a gurin biki" tayi saurin cewa "Allah ya kiyaye, insha Allah sai na haihu". Sai ta jawo kujerar da take kai kusa dashi tayi tagumi tana kallon sa, ya bude ido yana kallon ta yace "what?" A hankali tace "I want to kiss you, kuma Subay'a tana kallon mu" yace "ohh, a wannan bangaren kam kin ajiye fulatancin ko?" Sai kuma ta rufe ido tana dariya.
Addu'ar Diyam dai bata karbu ba, dan suna komawa makaranta aka saka ranar bikin su Sa'adatu kuma wata biyu kadai aka saka, meaning cikin Diyam yana da wata takwas kenan za'ayi bikin. A dole Diyam ta taho Maiduguri lokacin bikin da katoton cikinta, Sadauki yana ta yi mata dariya amma sai ta maze da shiga harkokin bikinta sosai ta rike role dinta na matsayin babbar yaya. Da ita akayi shawarar komai, da ita aka sayi komai, wani abun ma in ana nema sai Mama tace azo wajen Diyam.
Su Inna da Mama da Asma'u ma duk sunzo gurin bikin sun kuma Kawo wa amaren gift sosai har sai da Maman su Murjanatu tace "kayan nan anya basu yi yawa ba Amina?"
Aka daura aure aka kai amare gidajen su. Sa'adatu ta auri Aminu an kaita Abuja. Falmata kuma Saifullahi mutumin Kano amma mazaunin Canada dan haka can zasu koma, Fanna kuma ta auri cousin dinta Al-mustapha zasu zauna anan Maiduguri amma zata zauna a gurin su Diyam ta karasa karatun ta.
Bayan su Diyam sun koma England sai hankalinsu kuma ya koma kan haihuwa, Sadauki yana ta rawar kai, duk zuwa asibiti tare suke yi idan kuwa yaga namiji ne zai duba ta sai ya ja abarsa su bar asibitin. Twins ne kamar yadda Sadauki yake ta addu'a. Diyam tayi tunani sai taga cewa ba zata iya tuno yadda haihuwa take ba tunda bata yi labor a haihuwar Subay'a ba, haihuwar twins kuwa ba zata iya tuna yadda abin ya kasance ba dan haka sai ta shiga maternity classes, anan ta fahimci komai ta kuma yi browsing wasu abubuwan ta sake fahimta.
Abinda take tsoro guda daya shine shigar Sadauki gurinta in tana labor, tasan kuma za'a bashi option din shiga kuma