tare da ya daga ba. Sai can ta sake ruri, afusace ya ratsa ya kara a kunne.
"Ina bin sahunka ban ganka ba, na tsorata da abin da ka fada dazu. Na kasa samun nutsuwa saboda na san halinka. To ka ji, wallahi ka keta mutuncin yarinyar nan, ba zan taba yafe maka ba — kai da iyayen da suka yi sanadin zuwanka duniya. Sai la’anar Allah ta tabbata a gare ka, azzalumi! Daga kanta zaka ga aya. Kuma ma, ko yatsanta ka taba, ina rokon Ubangiji ya yi gaggawar saka mata ta inda zaka kasa fita har abada. Sai Allah ya jarrabe ka akan wannan!”
"Ya isa haka!!"
"Haba, irin wannan jafai haka, kamar ba jinin kiba?"
Ta ja tsaki, ta kashe wayar. Duk tantirancinsa, yana tsoron bakin kakarsa. Tun kafin ya taso, ya riga ya canfata da cewa tana da kambun baka — duk ikirarin da ta yi, yawanci yana tabbata. Muguwa ce shiyasa kullum zaka ganta a kan buzu, gaba daya bata da lokacin bacci, hannunta kullum rike da carbi.
Ya koma falon cikin dakin yana ta zarya. Kalaman kaka ne suka dinga yi masa yawo a kwakwalwa, yayin da idanunsa ke haska masa halittar Ikhlas.
Ya sauke ajiyar zuciya.
Yadda yake jin ta a ransa ya kasa tantancewa — tsananin sha’awa ne, ko kuma takaicin sumbatun kaka?
Ya fara sumbatu kamar wani tababbe, yana maimaita kalmomi da ba shi da tabbacin ma’anarsu, kamar zuciyarsa na rikici tsakanin son wani abu da tsoron la’anar da aka jefa masa.
A’a, ban taɓa jin mace ta shiga zuciyata ta ratsa kowace jijiyata irin haka ba. Na gode wa Allah da ban keta mata haddi ba… amma inajin kamar an ajiye ni a hannunta ta hanyar da ba zan iya guduwa ba. Daga can ƙasan zuciyata, akwai wani ƙauna mai zurfi da dole sai na kare rayuwata da ita dole sai ita ce matata.
Sai dai gaba ɗaya na tsani kaina. Me yasa na bi wannan hanyar? Da wane ido zan sake dubanta? Yaya zan haɗa ido da ita? Zuciyata na ƙuna kamar wuta, zuciyata na harbawa da ciwo, amma har yanzu ina jin wani irin ƙarfin sha’awar ta a cikina. Wannan ji mai haɗa tsoro da farin ciki ya mamaye ni, har numfashina ya fara nauyi.
---
A gefe guda, Ikhlass ta motsa a hankali. Idanunta suka buɗe cikin kasala, amma ciwon kai ya daki ƙwaƙwalwarta kamar guduma. Tana yunƙurin tashi, sai ta ga hijabinta da dankwalinta a gefe, uniform ɗinta a cunkushe. Wani irin ƙara mai haɗe da kuka ya kuɓce mata. Da gudu ta fice, ba tare da ta ɗauki hijabi ko takalmi ba.
Tafiyarta cike take da girgiza ƙasa da bugun ƙafa, kowa na kallonta da mamaki. Ita wacce kullum ake gani cikin mutunci da kunya, yau tana gudu a haka.
Shi kuma daga nesa ya hange ta. Zuciyarsa ta doki ƙirji da ƙarfin da bai taɓa ji ba. Ya kira mai tsaron ƙofar da gaggawa, hannunsa na rawa.
“Dakatar da ita… don Allah, ka dakatar da wannan yarinyar!”
Kafin ya fito, mai gadin ya riga ya nufo shi.
“Tana ina?!” ya tambaya da muryar da ke girgiza zuciya.
“Sorry oga… mota ce ta bugeta,” mai gadin ya faɗa da lalatacciyar Hausan sa, ya wuce.
“What…!” Kalmomin suka makale a makogwaro. Idonsa ya fara juyawa da tsoro, zuciyarsa na bugawa da ƙarfi. Ya gangaro daga bene da gudu, kowa na kallonsa amma ba wanda ya iya tambayarsa.
A waje, ya tarar da taron mutane. Jini yana kwance a titi. Zuciyarsa ta yi nauyi kamar an ɗora dutse a kai.
“Ina yarinyar da ta yi hatsari?” ya tare wani saurayi.
“‘Yan sanda sun ɗauke ta. Na tabbata asibiti za su kai ta Allah dai yasa bata mutuba ,dan wannan sai wani ikon Allah,” saurayin ya ce, ya wuce.
Wannan shine last free page mai son cigaba ya tuntuɓe ni a wannan numbar -08031307884
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng