jan numfashi na zuciya tare da dafe kirjin shi dake halbawa kamar zai fito .
Komawa yy yana rintse idon tare da yi mawa zuciyar sa Alkawarin kota halin kaka sai ya keta mawa wannan bafullatanan hadin ta .
Itakam Shatu ganin ta samu ya cika ta da kyar ne tayi saurin gyara goyon bayan ta tana daukar mayafin ta tuni ta silale ta gudu ba tare da dukkan su sun lura ba . Sai Sadeeeq kadai ne yaga ta juya takoma ta hanyar da ta fito... Shiru Sadeeq yayi yana tunanin abubuwa kamin lokaci daya kwakwalwar shi ta bashi cewan Wannan Bafullatanan ba mutum bace ba ,aljana ce...
Sai a sannan Abbas ya bude idon shi da yakoma kaman an watsa mashi borkono don jah ,bin Sadeeq yake da wani irin kallo kamin yace " Allah kasa ifritu ce wlh sai na kyeta mutumcin ta .
Bin su da Kallo Anwar yayi kamin yace " Daddy na kirana har ya katse ban dauka ba akan wannan wahalalliyar bagidajiyar bafullatanan dajin . Mtswww tom me ma zakayi da itane Abbas ,mu wuce kawai yakamata a yau na koma gida saboda ina tunanin Dad ya dawo ". Huuuuummmm A tare shida Abbas suka sauke numfashi kamin su shige moton nasu suna bata wuta don ko wannen su ransa a bace yake . Shikam Sadeeq ran sa ya baci don kwartancin Abbas ya fara damun shi a cewan sa yanxu yafara kokarin jawo masu balai ,tun da yafara kokarin yin iskancin shi da mutanen 6oye .
*******
Shiru_shiru Mama tana xaman jirar fitowan Asma'u a dakin nata amma shiru bata fito ba. Mikewa Mama tayi tana nufar dakin nasu wanda ya kasance nasu ne itada Teemah . Mamaki ne sosai ya kamata ganin Asma'u na salla da tsakar rana wuraren 11am. Sakin labulen dakin tayi tana komawa inda take zaune hadi da daukar tray din shinkafan da take tsinta hadi da fidda shefin dake ciki .
Tsawon lokaci sai ga Asma'u ta fito sanye cikin wata doguwar riga roba da yake kama jikin ta ta yana karamin mayafi ...Abun ka ga mamaki da Mama tayine yasata cewa" Asma'u yau kece da Sallah bama na farillah ba Nafila??. Keko me kike nema haka har kika dawo kikasan Allah daya ne??. Cewar Mama tana kallon Asma'u da itama Maman take kallo .
Murmushi tayi kamin tace " Ohh mama kenan ,tom Teeema nake tayawa addu'a don samub miji kaman leutanant Anwar abune mai wuyar gaske . Yau zata sanar mawa Mahaifiyar sa da Abun dake zuciyarta game da d'an ta kinga kuwa sai da rokon Allah muyita jamata sura.
Wani dariya Mama tasa wanda ya 6ata ran Asma'u ,buden bakin Asma'u cewa tayi " kai Anya Mama kece kika haifemu kuwa ? Sam baki son ganin cigaban mu ,mudai gsky idan bakece kika aifo mu ba ki fadi mana kawai munema Uwar mu mu huta . Cewan Asma'u tana wani irin gallare gallare.
Wani irin murmushin takaici Mama tayi kamin tace" hmm banyi mamakin mgnan ki ba Asma'u don dama kunsaba fadimun abun da yafi hakan ,kuma koda nayi dariya naga shashancin kune da har kuke tunanin wai auren Wannan matashin sojan ,a irin wannan dabi'ar takuce kuke wannan tunanin tabdijam....hmmm Allah sarki na tausaya maku ,bakwa ganin mahaifinku ,mahaifiyar ku da kima har daa akwai wani mutumin arxiki da kirki da xaiso hada zuria daku kunyi gwari kam yara !! Mama tayi maganan tana ca6e baki ,kamin tace nice mahaifiyar ku Asma kije Allah ya shuryaku abun da nake maku fata kenan a kullum kuma akoda yaushe .
Uhmm Asma'u tace tana barin mawa Mama filin tsakargidan hadi da ficewa daga gidan tana wani irin tafiya da motsare botsaren jiki da duwawu ,kunsan dai Cat Walk irin tafiyan da takeyi kenan tun tana na iskanci yanxu ya zama mata jiki .
Da kallon shiriya mama tabita dashi har ta bar gidan kamin ta girgixa kai tana cigaba da tsintar shinkafan nata.
*******
A 6anagaren gidan Dr Haulat kuwa fada ne ya kacca6e tsakanin Teemah da Zabeena ,don tun isan ta ta tadda Dr Haula bata nan tana daya daga cikin Asibitocin ta .hakan yasa Teema ta zauna a falon nata ,nan itama Zabeena ta zauna ,a nanne suka hau yadawa juna da habaici da maganganu tsawon lokaci don dukan su sun san manufan su a cikin wannan gida .
Hmmm lallai wannan shine hausawa kece mawa iska na wahalar da mai kayan kara ,ina mutum ina gwarzona Anwar ? Hmm abun ma baa hadi sam....Waye ne mutum waye kuma ubanshi....uhmmm bari na baimawa kaina amsa na daya dai mutum dinnnan ba kowane ba face dan gidan talakawan likis...na biyu kuma uban shi ba kowane ba face cikakken misakin talaka wanda babu sana'a cikakke sai buba buga....hmmm uhmmm tom ina ke don allah ina Anwar ,Anwr nawa neni Zabeena... Kutumar ubannan Abun da Teemah tace kenan kamin ta daga ruwar dake glasscup din gavan ta tana wanke wa hadi da sheka shi saman fuskan Zabeena da tayi gigif ta mike daga tsaye ,don batasan da zuwan ruwan ba .
Itama Teeman mikewa tayi a fusace tana kallon Zabeena da take bun ta da kallon mamaki . Nine kika watsa mawa ruwa a saman fuska....cewan Zabeena cike da mamaki.
Wanii irin kallon sama da kasa Temmah tayi mata kamin ta ta6e baki gyefe tana mai cewa" kwarai kuwa kena watsa mawa ,kinsan duk sabo dameye nayi maki hakan ?? Saboda ambaton sunan Anwar da kikayi da mijin ki ,tom kisani wannan ruwan ruwa na watsa maki na gaba ruwar petir ne ko kalanzir zakiji a saaman fuskar ki na kyetta ashana na babbakaki ,wannan duknasaboda son da nake mawa Mijina Anwar ne??? .
Mijinki?? A yaushe ne Anwar din ya xama mijinki sauna? Cewan Zabeena tana fiddo da ido waje cike da bakin ciki . Kamin ta cigaba da cewa" wlh nikuma duk ranan da kika kara kirar sunan Anwar da mijinki sai na Kashe kin bar duniyar baki daya ....
Allah ko tom ko zaki kwatantan ta eiye? Cewan Teemah tana fito da ido hadi da matsawa kusa da Teemah na ki kwatanta mana .
Meye haka kuma? Meye kukeyi ne?? Shigowar Dr Haula tana mgnan murya sama_sama kaman numfashin ta zai dauke yabar gangar jikin ta .
A matukar fusace Zabeena ta juyo ga Hajiya Haula kamin tace " kiji mun wannan shashashan yarinyar don Allah Mom ". Wai Anwar ne takeso...!!
Yau ni naga takaina Haula ,har nine Alhaji Jalingo zai yaudara ya cuceni nida da na?? Wlh bai isaba sam vazai yuwuba...Cike da mmki Zabeena take bin Dr Haula da kallo kamin tace" Momy me yafaru ne?? ... Dago da idanunta Dr tayi tana watsasu akan na Zabeena kamin ta kuma kaiwa ga na Teema da take cika hannun ta stiill da glss cup din. Hmmm kuna ta hauka a cikin jaji kuna ta lalube cikin duhu ,kun jirarr jirara tom duk wanda kuka fada akansa a yanxunnan mahaifin sa ya kirani a waya yana shaidamun cewar Y aura masa wata yarinyar dani bansan taba ,shima kanshi Anwar din bai san taba .....wani irin jiiri ne ya kwashi Zabeena batasan lokacin da ta zube a saman kujera ba tana dafe kanta dake sarawa ba kakkautawa .
Itakam Teema sakin glsscup din tayi lokaci daya kwallah yafara zubo mata ta cikin kwarmin idon ta masu zafi da tafasa zuciyarta.
Itakam Mom Haula wani irin gumi ne ke karyo mata na takaici da tsananin bakin.ciki ,idon ta ya sauya ya rine buden bakin ta cewa take wacece wannan yarinyar da tayi mun shigar sauri a rayuwata da na Anwar? Wacece ke shirin mun yankar kauna tsakanina da d'ana?? Wlh ko an daura auren sai an warware indai ina raye kuma ni nake da iko ga Anwar!!!
_*Littafin WALIJAAM na kudi ne kaman yanda kuka sani*_
_*Ga masu bukatar wannan littafi xasu na iya mgn dani ta wannan whatsap link din👇*_
https://wa.me/qr/7UGIAODZY3LON1
_Normal grp 200_
_Vip grp 500_
_Spc group 1k👌_
_Idan kati xaki turo MTN ne ._
_Idan kuma ta account ne ta nanan👇_
_0028799846_
_Farida Hashim stanbic bank_
_Yan niger kuma zaku tura katin 500f ne na Airtel ta wannan number na kasa👇_
_+22797780373_
_Idan kuma Spc grp kk bukata 800f ._
_________________________
Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I selling MTN data with this cheap price*
*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*
*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* Whatsapp OR
Call 08066268951
_________________________
_FREE page na dab da karewa masu bukata zasuna iya magana dani ta link din dake saman page ,Don Allah kar kimun mgn kiga ban baki amsa ba , kwana biyu ina busy sosai ,idan biyan littafin zakiyi ga hanyoyin biya nan nasa a kasan wannan page din ,idan kin biya kimun screen short na evidence dinki ,idan kati ne kk turo zan gani kuma xan saki a paid grp 2 inshaallh... Masu tambayar grp link na comment wlh ya cika ,idan biyan littafin xakiyi sai ki biya kaawai a saki a paid grp 2 ngd..._
*_Taku mai kaunar ku tare da nuna mawa masoyan ta soyayya da kauna ,kulawa duka wato_*
*MAMAN TEDDY🧸*
*🐄WALIJAAM🐄*
_free page_
_15_16_
*_Ga masu bukatar wannan littafi xasuna iya mgn dani ta wannan link din 👇_*
https://wa.me/qr/7UGIAODZY3LON1
*_SADAUKARWA GA DUK KANIN FULANI🐄_*
*Alheri writers asso.📚*
_________________________
"Na shiga uku na ni Haula..!! Wannan wacce irin masifa ce Alhaji ya dauko mun ,lallai yau na yarda cewa Bayason farin ciki na dana Anwar ,aiko lallai baxan ta6a yarda da wannan lamarin ba ,yanda aka daura Aurennan a duniya haka zaa rabashi acan. Don ba a haufo wata diya da zata tako mun kafa ta shigo gidan mijina a matsayin suruka ta ba ,haka ba a haifo wata yarinya da xata Aurar mun d'a wai ta zauna mun dashi a matsayin mata ba ,nice kadai nake da za6i akan d'an dana haifa...ta karke maganan tana jan wani irin numfashi ma tattare da bacin rai da takaici ,tana mai dafe goshin ta .
Momy duk a yanxu ba lokacin mgn bace meye mafita a yanxu ko haka zamu saka idanu har abun da muke gudu ya faru?? Cewan Zabeena tana maganan hadi da matsar kwalllah". Itakam Dr haula taakaici ne ya hanata bata amsa sai dai kawai ta mike tana barin komutsan da ta shigo dasu anan wurin hadi da nufar bedroom din ta ,don yanda zuciyar ta ke wani irin tafasa yana halba mata kamar xai tarwatse yayo waje .
Itakam Teema hawayen ne ke dada wanke mata ido kaman baxai dakata da zuba ba ,yyn da cikin sauri ta fice daga falon tana mai nufar gidan Mahaifin nata don neman Asma'u ta fidda mata da wata mafitan.
******
Bangaren shattu kuwa ganin irin Waaannan miyagun mutanen da ta hadu da su ,a cewan ta marasa imani ne yasata nufar rugar su tana komawa inda ta fito ,gab da xata isa Bukan su ne ta hango Hardo na tahowa daganin sakasan ba a hayyacin sa yake ba . Hango ta da yayi ne yasa shi tsayawa yana nisawa dama daga jiron su yake . Har tazo dab dashi bata nuna wani alama na tasan hardo ba illlah ma rabashi da tayi tana kewaya shi xata wuce .
Ke Ballagaza karuwa!!! Sunan da ya kira Shatu da shi kenan yana wannan numfarfashi kaman wanda yayi gudu ya gaji . Cak tajah ta tsaya ranta na suya sakamakon kirar sunan ta da hardo yayi da karuwa....Naam mijin karuwa inajin ka. Ta bashi amsaa a takaice tana murmushun bakin ciki .
A kufule Hardo yace waye mijin naki? , ni hardo Kuwa allah shi kyauta ai na dade da sakin ki ,kije ki nema fasikin da kukasaba fasikanci ki Aureshi.
Kasa basa amsa tayi sai binsa da wani irin kallo da take na mmmaki ,kamin lokaci daya kwallah yafara kwaranya mata yana gangarowa saman fuskan ta . Baki na rawa tace " Hardo ni ka saka ? Ashe dama duk rantsuwar da kakeyi akaina na zaka zauna dani duk wuya duk dadi karya ne Hardo??. Ashe cewan da kakeyi tare zamu rayu zamu mutu duk karya ne?? Akan wannan abun ne xaka ce ka juya mun baya wai harda tukucin saki . Maganan nata ne ya harde sakamakon wani irin kuka da ya kubce mata .
Shikam Hardo juya mata baya yayi kamun ya cigaba da cewa " eh ba sakeki shatu ,don nace xan rayu na mutu dake shine kkje kika dauko mun yar xina? Tom nafasa yanxu kowa na nemamawa yayan sa uwa ta gari ne ,kinga ko bana nemo masu mazinaciya ba...na sakeki Shatu bana sonki bana kaunar ki . Yana fadin haka ya juya fuuu yana cigaba da ta fiyar sa kaman xai fadi kasa saboda sauri fakakan² gashi babu kiba dan filinge kaman iska zai kada shi kasa .
Itakam Shatu anan wurin ta tsaya kamin ta zube kasa tana wani irin kuka ma gunji tsawon lokaci tana a haka ,kamin ta lalla6a ta tashi daga cikin wannan siyayin tana nufan jiron su hadi da isa buka .
Da shugarta ne Umma ta bita da wani irin kallo ,da yake nuni da abubuwa da dama ,Yawindo ne tayi saurin tarota tana kwance yarinyar bayan ta kana tace " daga yau Shatu kar ki sake fita ko ina ,saboda ke matar Aure ce a halin yanxu ,Hardo ya sake ki a cikin dubbin jama'a kuma a daidai wannan lokacin ne wani bawn Allah ya roka a daura auren ki da d'ansa tunda baki da idda akan Hardo shi yasa aka daura Auren ki da wani mutumin na dabam .
Kirjin Shatu ne ya buga mata da karfi ,wanda saboda firgici sai da ta dafe wurin ,shikenan a yanxu na tashi a matar Hardo ,duk so da kaunar da nake masa ,kawai sai kuka hawaye na bun kuncin ta sharrr_sharrr.
Kwance yarinyar bayan Yawindo tayi tana zaunar da Shatun kamin ta zauna gyefen shatun tana kallon jaririyar tana fadin Mashaallh yarinyar kyakykyewa kamar diyar larabawa mene sunan ta ?. Jan hanci Shatu tayi cike da muryar kuka tace " na sa mata sunan Umma na Fatima ". Aaaa mashallh ashe Nana ce....kai Yawindo wannan abun da kkyi tayi yawa banason a saka suna na sam wlh ta dai nima wani sunan tadabam ba suna na ba...Aiko baxa'a canja ba sunan diya Zahara. Cewan Yawindo tana murmushi hadi da mawa jaririyar wasa.
Itakam Shatu juyawa tayi tana kwantawa a hankali hadi da lunshe ido kwallahnna dada zubo mata ,ko wanni secon tunanin mgnan da Hardo yayi mata takeyi ,wanda zuciyarta kuwa kaman a wannan lokacin ne yake kara ingixa mata wutan soyayyar hardo .
********
Zaune suke Anwar da Abbas Sadeeq a dirning area suna lunch ,hankalin ko wannen su a kwance yake kowa na cin abuncin shi banda Abbas da yake dauke da fork ya kasa cin komai .
Anwar ne ya kallin Abbas kamin yace masa," kai malam yadai kana ta rike da fork baka ci komai ba har yanxu kasan fa tafiya ce damu yanxu ,tun jiya Mom ta kirani tace na dawo gida tanason mgn dani ,kuma kai kana ta rike da Fork kaki cin komai yanxu fa xamu tafi.
Nisawa Abbas yayi yana lumshe makirarrun idon sa ,kamin ya taune la66an sa na kasa .
Murmushi Sadeeq yayi yana fadin bai wuce jarabarsa ce ta motsa ,tom oga Abbas ka kwantar da hankalin ka ,acan ma idan munje xaka samu hadaddun fine fine ladies . Just kaci abincin ka mu wuce kar ka 6ata mana lokaci plz.
A hankali Abbas ya furta ina son ta ne!! Ina son wannan yarinyar i really luv her .
Mamaki ne ya kamasu duka amma sai Anwar cike da miskilanci ya kawar da kai ,shikam.Sadeeq cewa yayi wace kenan..? Kai tsaye Abbs ya basa amsa da wannan bafullatanan ,a ina take aina xan sameta ? A ina xan ganta??. Karyar banza kanaso kayi iskanci da yar mutane tom bakaga da goyo a bayan t ba ,matar aure ce kayi wani abu da ita bulallai xaka shako ba haka ba Anwar ? Sadeeq yayi maganan yana duban Anwar da sai a sannan ya kalli inda suke .
Kwashewa da wani wawan dari su biyun sukayi suna kallon Abbs da yake kire da kwalin Exotic .
Hmmm kuna shirme ne cewan Abbas yana tsiyaya lemun a cup ,sai da ya kurba kadan sannan ya ajiye yana fadin " ba son ta nake na lokaci daya ba ,wai nayi sex da ita shikenan ba ,Aaa son nake ta kasance dani har Abada ,tazama mun uwar y'ay'ana ba wasa ba yayi mgnan yana kallon su Anwar dasu ma shi suke kallo .
Cigaba yayi da cewa" kowaye mijin ta wlh indai ina lumfashi a duniya sai ya rabumun da ita na Aureta dani ta dace ba da wani ba.
Tsagaitawa yayi da mgnan yana kallon su . Murmushi Anwar yayi kurum kamin yace " tom ai sai kabi kauyakun fulani ka nemo ta... Dariya sadeeq ya hauyi kamin yace irin wannan fulanin ne da hausa basu iyaba sam....idan kaje da kanka zaka dawo mayaudari. Aa bazai dawo ba , kamin yafara neman ta sai yafara koyon fulatanci sannan kaga idn ya iya neman nata zai zo maasa da sauki....cewan Anwar yaana murmushi da hushiryar sa ta bayyana .
Kwarai kuwa hakane Anwar kaga sai ka fara zuwa ka koyo Fulatancin kasan meye WALIJAAM da imfinijaam...
Dariiya duka suka saka a wannan karon har da Abbas din kamin ya ajiye fork din da yake tsakarar ppr chicken yana daukar tissue hadi da goge la66an sa yana mikewa daga tsaye yana fadin kun kawo shawara kam mai kyau ,ku mu tashi haka mu dauki hanya .
Mikewa su duka sukayi suna ficewa daga falon hadi da fita fitowan da xasuyi ne naga ashe a barikin sojoji wannan gidan yake nufan daya daga cikin motocin su sukayi suna shiga kamin su dau hanyan zuwa gidan Mom Haula .
********
Ummie inaso idan na samu hutu naje Garin kaduna gidan Momyn Abbas acan zanyi hutu ,kinga na dade banje ba ummie . Diyanan tayi magana tana kallon Ummien nata da hankalin ta ke akan laptop din dake gaban ta . Idon kuwa na ta sanya masa siririn gewayayyan Eyeglass wanda yakasance fari