x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 3 - WALIJAAM

  • 6001 words
  • 9000 words
  • Out of 30771 words

Category: Tale Stories

Views 64

01 Sep 2025
Start ads
After Image Ads
daukar mataki akan shattun .

Lokaci daya yaji wani irin masifaffan tsanan Wannan bafullatana ya shige sa . Kasa maruri yayi gashifa moton daya daga cikin motocin sa ta buga da sandar nata . Tattarawa yayi yana ficewa daga barikin don baya tsammanin zai iya samun wani natsuwa jin yanda zuciyar sa take maasa . Don tun da yake a rayuwarsa ko sa'ar sa bai ta6a yi masa abunda Shattu tayi masa bare kuma Wai wata diya mace ,macen ma karamar yarinya !!!

*****

Bangaren shattu kuwa Sam yagwalgwal bata samu natsuwa ba ,sai da taga sunyi nisa sun nitsa daji sosai babu yanda xaayi sojojin nan su biyosu sannan hankalin ta ya kwanta ta fara yi mawa Shattu fada ,da fadi mata sudin su waye . Koda ta fada mata ita sam bata damu ba ,don bata ga abun da tayi badai dai ba . A haka suka cigaba da tafiya suna kiwo ,kamin wani lokaci daga yagwalgwal din har shattun sun manta da wani leutanant da abun da yafaru tsakanin su .

Bangaren Anwar kam a wannan rana gaba daya ya kara zama wani hero . Ko sakin fuskan ma ds yake yi ana jin dadi yanxu ya daina ,ko mgn su Su Abbas sukayi masa bai basu amsa ,sai aikin tukukin rai hadi da daddakan kwalaben sa . A washe gari bai mgn da kowa ba ya dauki hanyar Garin Abuja don Mahaifiyar tashi ce kadai zao iya sanar mata da wannan mummunan lbrn ,ta kuma rarrashe shi . Toh waye ma Leutanant Anwar B jalingo???!

"Anwar ya kasance d'ane ga Alh Bashir jalingo ,wanda wasu ke kirar sa da Alkalin alkalai na abuja. Mahaifin shi shine shugaban kotin koli na nigeria . Shi kadai ne Allah yabaimawa mahaifin shi haka ma mahaifiyar shi wato Hjy Dr Haula. Wannan yasa suke son dan nasu tankar bugun zuciyar su , don ko sojan sbd shine ambition nashi tun yana yaro shiyasa Mahaifin nashi amince masa har a yanxu ya taka matsayin sa na Leutanant . Anwar matashi ne wanda ashekarun shi na haihuwa baifi shekara 30 zuwa 32 ba . Iyayen nashi suna son shi fiye da komai sun gatantashi fiye da kansu da komai suka mallaka .

******
_Mai duguri_
Ummie ummie Ki taimaka mawa Diyana n ta ki , bani da kowa bayan ki ,Ummie ki fadamun mai ke damunki waye kike yawon ambaton sunan shi a baccin ki ? Ummie dama kina da d'a ne a duniya bayanni? ,a iya sanina baki ta6a haihuwa ba .nice kadai y'ar ki .

Wata kyakykyewar budurwace mai kama da balarabiyan shuwa ke maganan cikin sanyayyar muryar ta ,fuskan ta dauke da damuwa hannayen ta nasaman gwiwowin dattijuwar wanda ashekaru zataiyi Hamsin . Amma kyawun fuska n ta dana jiki ya boye shekarun ta baxaka ce ba ,musamman idan kayi duba ga diyar nata Diyana da batafi shekara 25 ba ,kuma acewan ta itakenan mata . Don haka wannan zaisa bazaka ta6a bata wannan shekarun ba . Kuka Dayana tasa hadi da dora kanta bisa gwiwar ummin nata a tunanin ta da akwai abun da Ummin ke boye mata ne a rayuwar su . Cike da muryar kuka cikin harshen larabci take fadin " _ana ahibuki ya Ummie."_

D'agota Ummien nata tayi hadi da gyara jallabiyar jikin ta tana dora Diyana saman cinyanta hadi da manna mata kiss saman kumatun ta tana mai sa hannun ta hadi da dauke mata hawayen dake saukowa daga idon ta ". Kamin Ummien nata ne ta kuma mgn Diyana ta kuma cewa "
_"ya ummie billah guline wushefik wush indeik allamni izamagulni mafi ahat yaalam_ .

( Ummie na , ummie ,idan bansan damuwar ki ba wazai sani a yanxu ?. )

Rungumeta Ummien tayi tsam a jikin ta tana dan bubbuga bayan ta da taffan ta alamun rarrashi a cikin sanyayyar murya na uwa idan tana son rarrashin da ko yar ta ta fara mata mgn da murya mai kama da rad'a da cewa " _"shufi ya binti Diyana , inti maalum ana ma inde iyal anama aulat walawahik ana manikazzif alaiki_ ( _Diyata Diyana kaman yanda kika sani ni ban ta6a haihuwa ba ,hakan yake baxan maki karya ba kinji ?._ ).

kece kadai Y'ata a wannan duniyan kece kadai na haifa har zuwa lokacin da Abi din ki ya rasu . _Ana ahibuk ya bint ,ina sonki yata bani da kowa sai ke kinji!_

Numfashi diya ta sauke hadi da kara rumgume Ummien nata tana murmushi hadi da daga mawa Ummien nata kai ,itama Ummien murmushi tayi mata hadi da kokarin son ta kawar mata da duk wani damuwa . Zuciyar ta kuma yana tunano mata abubun da suka faru a lokaci baya da suka shude ,wanda wannan shine tambayar da Diyanan ke yi mata .

******

Hangosa tayi zaune a sopa cushine sunan rana ne amma ya rufe ko ina na bedroom din nashi ,ya kuma kashe hasken dakin ,hakan yasaka hasken dakin kadan ne kake hangowa .

A hankali ta kai hannun ta hadi da kara hasken dakin , kana tafara takawa cike da takon ta wanda da kagani kasan da kasaita da mulki ga boko a wannan wurin .

Shigar Hausa fulani ne a jikin ta ,don atampha ce supar ta saka wanda akayi mata dinkin riga da zani. Sosai ya kama wannan Hajiyar . Idanun ta sanye suke cikin medical eye glss . Hjy Haula kenan . Zama tayi gyefen Anwar tana dago sa hadi da kirar sunan sa cike da tausasshiyar murya " My lovely son". Ta kira sunan sa cike da sanyar murya tana shafa sumar gashin kanshi .

Lumshe ido yayi a hankali ya cije labban sa kamin yayi mata mgn ne ta kuma ce masa " sorry my son nasan da akwai abun dake damun yaro na ,waya tabamun Habibi na ?! Tayo maganan cike da muryar sokana hadi da son kwantar masa da hankali .

Murmushi yayi wanda sai da faffadan hushiryar sa na da ya raba hakoran sa na gaba y bayyana .

Sosai taji dadi ganin yanda y sauka lokaci guda ,don dama itace kadai mai kwantar masa da hankali da saukosa duk idan ya shiga halin bacin rai . Mom na tsane ta ! Banason ganin wannan yarinyar ....

A hankali take kallon sa kamin ta bude baki cike dajin dadin kalmar tsanan da ya ambata ,don batason ganin ko wacce diya mace ta ra6a mata Anwar yaron nata ,saboda tana da wanda takeson ta bashi.

Budan bakin ta cewa tayi My Love calm down ohk ? Fada mun wacece ka tsana haka??. Nisawa yayi yana mikewa daga zaune yana cewa " Mom banason duk wani FULANI dake gidannan da sunan aikatau . Mom a koresu duka! .

Murmushi tayi kawai ,kamin tace shikanan Son inshaallhu babu wani fulani da xai kara ko zata kara kwanan gidan Daddyn ka . Ka kwantar da hankalin ka dear . Muskutawa tayi tana mikewa daga tsaye hadi da cewa yanxu xatasa duk kan fulanin dasuke aiki subar mata gidan ta .

Rufo masa kofan bedroom din nashi tayi tana takawa hadi da sauka daga kasar stairs .
Ina kuke masoya littafan marubuciya maman teddy...🧸? Nasan ko waccen ku ta daga hannun ta tana amsa mun da "Gani ".
Ta baje maku kolin littafan nata gama su tambaya tare da bukatan su :
Bafullatanan ruga #200
Gidan kwarata #300
Y'ar Aiki na! #100
Dijama y'ar fulani 200
Kwaryar sama #300
Zuma da mad'aci #200
Siyasa taah #300
Y'ar maula #200
Kawaliya #200
Habiby Da'iman free
Y'ar Waye!! #100
Bintoto free👌 yanxu kuma na dawo maku da gawutacce kuma kayatacce wato WALIJAAM🐄 .
Shikam yaxo maku ne akan sassaukar farashin Vip payment 500 .
Normal payment 200
Special Payment 1k .
Masu bukatar wannan jeran giyar littafan duka xaku yi mun mgn ta hanyar dannan wannan blue din link din 👇 .
https://wa.me/qr/7UGIAODZY3LON1

*****

*******

Watanni sun shud'e wanda kusan watannin Shattu goma kenan da tafiya ciranin kiwon nata ,nan suka rabu da yagwalgwal akan cewan xata dawo rugar su ,sosai shanayen ta suka ha6aka wasu suka haihu sinyi mata albarka matukar gaske .
Sanin idan ta dawo sai tarewan ta gidan mijin ta ne yasata shirya komai nata tsaf .hadi da tarkatowa ta nufo rugar surbajo . A kwana a tashi tafiya tayi nisa har ta kusa dawowa rugar tasu baifi sauran Garuruwa uku ba ta isa .

Tsallakar wani hanya ta zoyi ,wanda titi ne abun hawa na wucewa ita kuma xata shiga ta wannan dajin dake gyefe ta ritsa ta cigaba da tafiya zuwa rugar su .

Mmkine ya kama shattu hango wata moto da tayi akamu dai mai moton yana bukatar taimako . Saurin karasawa tayi da shanayen ta ,wanda ganin matan rike da jaririya a durkushe daga wajen moton yasa Shattu saurin karasawa tana dukawa inda take . Kaman a lokacinne akace mawa Jaririyar cigaba da ihu .kawai sai kukan jaririya ya fara karade wannan wuri .

Cikin gwarancin Hausar Shattu ta kalli matan da duk ta jigata da alama matafiya ce da abun hawan ta . Ina kike ne ? Ina zaki ? Ki bata ruwa jariri na kuka . Abunda shattun tace kenan tana karban jaririyar hannun matan da take a wahalce cikin jini alamu ya nuna anan kan hanyan ta haiho yarinyar .

Amaimakon taba Shattu amsa n tambayar nata ,sai kawai rike mata hannu tayi tana mai xubar da kwallah mai ban tausayi da tsayawa arai . Yar fulani ga Amanar yata nan ,na baki halak malak ki rikamun ita kyauta na baki kuma Amana .

Idan mahaifin wannan yarinya tawa ya ganta ko kin ganshi ki bashi ita ,idan kuma baki ganeshi ba ki riketa har mutuwa don Allah...wani orin numfashi wannan mata tajawo da kyar kamin ta ciro wani abu mai kama da sarka amma dagani kaga irin na jarumannan ne . Gashi yar fulani ,ki samawa diyata aduk lokacin da kk nishadu ,inason wannan sarkar saboda na mahaifin ta ne . Koda ya manta da komai navrayuwa na dashi da kuma soyayyata tom baxai ta6a mantawa da wannan sarkar ba ,saboda mah......wani irin tari ne ya kwace mawa matan wanda nan take jini yafara fita ta bakin ta ,na yafe masa kome yy mun so....salati ta fara yi kamin kawai jikn ta ya saki hannun ya ragwab .

Tofah wannan shine mafarin labarin WALIJAAM🐄.
Rudewa Shattu tayi sosai lokaci daya hawaye ya fara zuba mata ,ga jaririya tana mata ihu babu kakkautawa . Urincewa tayi rasa abunyi yasa Shattu kawao saba yarinyar tans dorata saman gadon bayan ta ,yarinyar ko kaya babu bata damu da jinin jikinta ba ta dorata a saman bayan ta tana kwance dankwalin kanta hadi da daure jaririyar da shi . Ba tayi tunanin komai ba don tarasa yarinta kawai sai ta cire wani mayafi da ta gani gyefen matan ta yafe jikin ta dashi tana nufar cikin dajin da zai sada ta da rugar su itakam Jaririya sai uban tsala ihu take....

Jaririya na kuka shattu na sharce kwallah ita burin ta taga inda zata samu ruwa ta baima Jaririyar ko ta daina kuka .



_*Littafin WALIJAAM na kudi ne kaman yanda kuka sani*_
_*Ga masu bukatar wannan littafi xasu na iya mgn dani ta wannan whatsap link din👇*_
https://wa.me/qr/7UGIAODZY3LON1

_Normal grp 200_
_Vip grp 500_
_Spc group 1k👌_

_Idan kati xaki turo MTN ne ._
_Idan kuma ta account ne ta nanan👇_
_0028799846_
_Farida Hashim GTbank_

_Yan niger kuma zaku tura katin 500f ne stock na Airtel ta wannan number na kasa👇_
_+22797780373_
_Idan kuma Spc grp kk bukata 800f ._

_*Maman teddy🧸*_
_*Littafin WALIJAAM na kudi ne kaman yanda kuka sani*_
_*Ga masu bukatar wannan littafi xasu na iya mgn dani ta wannan whatsap link din👇*_
https://wa.me/qr/7UGIAODZY3LON1

_Normal grp 200_
_Vip grp 500_
_Spc group 1k👌_

_Idan kati xaki turo MTN ne ._
_Idan kuma ta account ne ta nanan👇_
_0028799846_
_Farida Hashim stanbic bank_

_Yan niger kuma zaku tura katin 500f ne na Airtel ta wannan number na kasa👇_
_+22797780373_
_Idan kuma Spc grp kk bukata 800f ._

_*Maman teddy🧸*_
*🐄WALIJAAM🐄*
_Free page_
_7_8_

*Tun daga farkon littafin WALIJAAM har karshe sadaukarwa ne ga duk kan fulani🐄*
_*Ga masu bukatar wannan littafi xasuna iya mgn dani ta wannan link din 👇*_
https://wa.me/qr/7UGIAODZY3LON1
*Alheri writers asso.📚*
______________________
"Ba tare da Shattu tayi wani dogon tunani ba ta cigaba da tafiyar ta wanda a dan kankanin lomaci ta isa rugar Surbajo . A wannan lokaci jaririyar ta tsagaita da kukan ta koma tayi luff kaman ba ita ce ke tsala wannan ihun ba ,saboda irin dumin bayan da taji na shattu yasa ta tajita kaman a cikin mahaifiyar ta take bata fito duniyar ba .
Shattu! Shattu!! Shattu!!! Ji tayi an kira suunan ta har kusan sau uku ,sam shattun bata juyowa ba ,kuma bata tsaya ta dakata da tafiyar nata ba . Tafiyan kawai take jikin ts duk a raunace ,tom me ma xatace mawa Abba da umman nata ne? Wannan shi yafi tsaya mata a kahon zuciya . Kuma tabbas tayi ma kanta alkawarin boye Asalib komai ,daga wannan rana kuma wannan lokaci watannan jaririya nata ne ,tazama diya kuma gudan jinin ta . Mareeya ce ta sha gaban Shattu hadi da ce mata" ke shattu ba magana nakeyi maki ba kinmun banza ? Ashe kin dawo ,kin san yau dinnan liman yagama cema Umma na Wai kina dawowa da kwana biyu xa'ayi biikin ki da Hard'o...maganan takeyi hankalin ta na akan Shattu sam bata lura da abun dake tare da ita ba ,sai surutu take antakowa kaman mene ,hannun ta dauke da kwaryar da tashake shi da nono har baki ta rufe shi . Tsayaawa tayi tana shirin yin masifa ganin aminiyar nata shattu bata bata amsa ba . Itakam shattu gaba tayi ta cigaba da tafiyan ta . Wani irin kara ta saki kamin Mareeya ta saki kwaryar nonon nata ta fadi kasa duka ya nonon tayi asarar shi a wannan wuri ,cikin rawar murya hadi da dagawa tana zaro idanun ta waje tace " Shattu a ina kika samu jariri?? Dan waye shi shattu???. Sakin kwaryar nonon da tayi yasaka hankalin fulanin dake nesa dasu dawowa kansu . Wanda sai a sannan Shattu ta dago lulun idanun ta wanda babu tsoro irin na fulani tace " ba nimiji bane ,ta macace kuma diyata ce .
Dafe kai Mareeya tayi yyn da sauran fulanin jin abun da Shattu tace yasa su saurin matsowa suna takowa xuwa inda suke . Kallon banza Shattu tayi masu duka har da Mareeya data kama a tsaye ta kasa motsa koda dan karamin yatsar kafarta ne.
Wuce su Shattun tayi zuciyarta na dada tafasa ta nanl nufan Garken su ,da shanayen ta tuni sun isa zuwan ta Umma ke jira a yanxu". Irin kallon da tayi masu yasaka kowa kasa cewa ufunnnn har sai da ta wuce. Innalillahi wainnailaihir rajiun . Aradun allah na dade da sanin Shattu yar iska ce ,yaudarar Hardo takeyi ,aiko hukuncin ta jifa ne a musulunci . Cewan wani saurayi wato Auro wanda ya kasance abokin Hardo ne mijin Shattu da akayi masu aure tarewa ya rage a yanxu . Kai da allah rufemun baki ,mara hali da hankali ,tom kaji kasani wlh billahi baka isa ,babu mai rabani da shattu sai mutuwa ko mutuwa rana guda ce xata dauke mu . Ni nasan halin shattu ,shattu ba mazinaciya bace ,babu mai taba ta ,ina tare da ita har abada .
Wani irin dariya Auro yayi yayin da sauran fulanin suka juya suna kus_kus kowa da gulma a cikin shi kuma tuni suka fara mawa Shattun kallon marigayi ya ,don su a wqnnan ruga tasu basa amfani da wata sharia turawa sai na musulunci kowa yayi abun da ba dai dai ba da alkurani ake yanke masa hukunci .

Wannan dan daga sama ta tsince shi ,wannan wani irin lalacewa ne ? Da auren ta taje tayi zina ?!. Cewar Auro yana bin Hanyar da Shattu tabi da wani irin kallon tsana da kyema. Aradu na fadeka shattu va haka take ba ,sai dai idan dan Hardo ne ,shine kadao mijin ta bayan shi babu wanda xai mata ciki har ta haihu . Mareeya ta kuma katse shi tana sharce kwallah .
Ai sai kiyi kuma mareeya ,nine fa Auro abakin Hardo babu abun da ya ta6a hada Hardo da Shattu .tabbas sai an yanke mata hukunci dai dai daa abun da ta aikata ,dama faduwa yazo dai dai da xama ,Baffan nata ai malami ne duk rugar nan babu mai ilimin sa har liman kuwa . Dariya wasu daga cikin fulanin suka sa ,wanda ganin haka yasa Mareeya rugawa da gudu tana bin bayan Shatttu don ta tambaye ta d'an waye a bayan ta...a tunanin ta dan Hardo ne!!.
********
Shigowa tayi bedroom din Diyyana da keta kwasar baccin ta hankalin ta kwance. Bin agogon dake makale tayi a bangon dakin nata da kallo ,kamin tabi yar nata da sanyayyar murmushi kaman tana kallon ta ko idon ta biyu ne ta hau bude bargon hadi da cewa " _"Sahanou y habibaty Ahalai y Banat... Ganin Diyana har a wannan lokacin bata farka bane yasa ta kuma ce mata" sahanou ya bintee rukhy..._

Motsawa diyana tayi hadi da dan jan bargon da tayi rufa dashi tana bude idon ta walan hadi da kara rufesu alamun baccin bai isheta ba , murmushi ta sakin ma Ummie nata cike da muryar bacci ta amsa Ummien nata da " _Yah Ummie habibty ummie y rukhy"...._
_"Naam Rukhy kalbi"._
_Ammien ta amsata tana fadin tashi safe tayi kar ki makara ,breakfast dinki ya kammalah"_
A hankali Diyana tafara bude idon nata tana sauka daga kayataccen gadon nata ,kamin ta rungume Ummie tana fadin " Ummie na Yau me kikayi mun?? Abinda Rukhy na tafi so!. Ta bata amsa a takaice tana kama hannun ta hadi da nufar privacy da ita dukan su fuskar su dauke da murmushi .
*****
BAFULLATANAN RUGA
labarin badakala akan yar fulani kunsan dai badakalan da muka zuba tsakanin gwarzon jarimi aliyu Haidar da yar bafullatanan ruga
YAR WAYE
kanannadaddiyar badakala kenan Tom yar waye ita?? Kunsan dai yanda dai cakwakiyar littafin ya kasamce ta yanda ta jero maku gwaraxan jarumai ko wanne da badakalan rayuwar sa .
YAR AIKI
tofa kalubale gareku mata ,kunsan dai yanda labarin yazo maku a kalubalance ,da cakwakiya a kasa kanannadaddiya
DIJAMA YAR FULANI
hohoho cakwakiya kanannadiyya kenan yar fulani dai karshe kenan ,kunsan yanda badakal
End Ads