x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 5 - MATAR HABIBI free pages

  • 12001 words
  • 14474 words
  • Out of 14474 words

Category: Tale Stories

Views 99

25 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
Dai-dai gwargwado tsaye yake kansu. Data nemi komawa makaranta bai tauyeta ba, dakyar dai ta hada takardun sakandire, dole ta hakura, sabodq hidimar gida data yara. Tana da cikinta na biyar ya rasu, bayan gajeriyar jinya. Wannan rasuwa ta kidima Rahanatu, gashi daga shagon nan sai gidan daya bar musu. Yara kanana, tunda a lokacin Khalifa ne kawai yake da shekaru goma, Anwar takwas, Jalila shida, sai Aziza uku, dan ta samu tazarar shekaru 3 ne a wannan karin. Bayan ta haihu ta samu namiji sai aka mayar masa da suna Ayuba suna kiranshi da Nur.

Sai ga takardun sunyi mata rana, shige-shigen mahaifinta da mutanen daya sani, sai gashi an samar mata aikin rubuta kati a Asibitin Aminu Kano. Kuma bata zauna haka da aikin ba, duk wata sana'a da zata kawo mata karin kudi bata sanya da ita. So take yaranta su haska sufi na kowa a unguwar tasu, su samu ilimi tunda ita dai taga ranarshi. Rayuwar karyar dai data dorawa kanta, Malam Ayuba kan nuna mata rashin jin dadin shi akan irin rayuwar lokacin da yake da rai, tunda yanayi mata komai, bayason yanda dai idonta yake kan wasu a cikin kawayenta, tana so ta taddosu ko ta zartasu. Yanzun da kasa ta rufe masa ido, ga aikin data samu, sai abinda yayi gaba.

Cikin yaran nata biyar kuwa, Khalifa ne ya fita zakka. Ya samu karatu zuwa NCE, yana aikin koyarwa, yanzun haka yana da mata da yaro daya. Ko kadan Khalifa bayason irin rayuwar da Mummy kamar yanda suke kiranta takeyi, ta kuma dora kannenshi akai. Ga Anwar nan, yana BUK a yanzun haka, saboda shi yace daman ba zai iya FCE ba, kusan yafi kowa jin kai a cikinsu, saboda shine sak ya biyo mahaifinsu, yana daga cikin matasan da suka rungumi mining din Pi lokacin da yazo, dan gani kasheni ne akan Pi, dan zaku iya raba jaha dashi idan kayi kokarin rage masa burinshi akan Pi. Haka yayi sa'a yana cikin wanda aka budewa yin kyc da wuri, saboda haka lokacin da aka fara bumburutun Pi saiya zamana ya samu kudin da bai taba rike irinsu ba.

Khalifa ya bashi shawara ya samu sana'ar da zai dingayi, suka zauna sukayi magana sosai, kuma Anwar ya nuna masa ya dauki shawarar, yana komawa gida, suka zauna da Mummy ya fada mata kudurinshi na da yayi niyyar yayi musu gyara ne a gidan, sai ta rushe duk wani tsari da Khalifa ya dorashi akai, sai gani yayi an dauko gyaran gida, gini ne na zamanin da, na kasa, sai akayi masa shafen suminti, dan haka katanga akaja bayan an ware daki daya akayi masa gyara na gaske, sai katangar ta raba wannan dakin da sauran gidan ba'a gyara ba, ya siyo wannan katon gate din aka kakaba a gidan.

Sauran Pi din yace ba zai siyar ba zai jira a shiga kasuwa dashi ne, dan abinda yayi saura ya fara saro gilasai, hulunan hana sallah da zobunan azurfa, daman yana dan taba siyar da takalma, yana samun rufin asiri dai-dai gwargwado dan kuwa Anwar ya iya kasuwanci, karya ce kawai takeyi masa cikas, tunda kudin maimakon yayi abinda ya kamata dasu sai a siyi turaruka ko takalma designers. A wajen Anwar dama Jalila a yanzun, da aji kunya gara an kwana da yunwa. Kawai wani hali da suke dashi su dukansu, suna son farin cikin Mummy, duk wani fata nasu na yanda zasu gatanta ne, ko Jalila tayi niyyar yin auren kudi yanda Mummy take so, sai ga Balarabe da suka fara wata irin soyayya mai tsayawa a rai duk kuwa da tarin talaucin shi. Haka Mummy naji tana gani ta hakura akayi auren.

Shikuwa Auta Nur yanda duk akayi dashi haka yake binsu. Jalila a yanzun haka ta gama diploma dinta anan Kano Poly, amman ita data samu mijin daya kwanta mata sam ba zatayi wani karatu ba. Aure take so, tunda ta tasa tasan ma'anarshi, ko yaushe cike take da mafarkin auren nan. Balle data kara samun babbar waya, tana cikin group din matan sirri na Facebook, tana bibiyar manyan bloggers a manhajar Instagram, sai ta karajin tanason auren, babu kuma abinda yafi burgeta irin ace yau ta mallaki kitchen dinta na kanta, tana dafa ma mijinta abubuwan burgewa itama ta dauki hotonsu ta shiga wannan trend din da ake yayi na 'ga abinda nake ciyar da mijina'.

Shisa duk shiriritarta, tunda Mummy tayi musu tsaye a bangaren boko dama Islamiyya, itace dai sai taga dama take zuwa Islamiyar lokacin, bata wasa da addu'a akan aurenta. Dan bata dagowa daga sujjada bata roki Allaah daya bata miji nagari ba, kuma tana da yakinin rokonta Allaah Ya amsa ya jeho mata Baffa. Duk da karsashinta ya rage lokacin da taji yana da aure harda yara uku, amman shi da kanshi Baffan ne ya kara mata karfin gwiwa, a bakinshi takejin shi da Jamila aure ne akayi musu na hadi, yanzun a tare da son da takeyi masa, akwai tausayi mai yawan gaske da yake bata. Ace matashi dan kwalisa kamarshi, ga rufin asiri yana dashi dai-dai gwargwado amman baiyi sa'ar mata ba.

A goman karshen nan batayi wasa ba wajen addu'a, harda Mummy take hadawa idan Baffa shine mijin nata, to abin ya kwantawa Mummy a rai. Tasan duk yanda zasu so juna da Baffa, in dai Mummy bata karbe shi da budaddiyar zuciya ba, ba zataji dadin zaman yanda ya kamata ba. Ai tana gani akan Jalila, duk wani abu da Balarabe zaiyiwa Jalila sai ta kushe, ko ita kuwa ya bada aka kawowa haka zata karba tana kushe abin da Balaraben ma gabaki daya. Wani zubin ma da kuka Jalila take barin gidan saboda kwarzabar Mummy akan auren nata. Shisa ba zata taba wasa da addu'a ba ita kam, tunda tasan babu wanda zai tausaya mata sama da Ubangijinta, to kuwa gara ta gurfana a gabanShi ta kai kukanta.

Yanzun a cikin kawayenta su shida, Aisha da Hassana duk sunyi aure, saura su hudu, ita, Mimi, Nabila da kuma Maryam. Sunfi dasawa da Mimi saboda yanayin rayuwarsu yazo daya, suna da son asan dasu a waje, gayu, dama karya, duk da ita Mimi suna da kudi, amman kudin nasu bai kai yanda ita take zuzutawa ba. Maryam yanzun haka ansa ranarta, Nabila ma anyi gaisuwa, shiya karawa Aziza jin kamar ta janyo Baffa yazo ayi magana tasan cewa da gaske yakeyi, yau ma sunyi zasu hadu a gidan Hassana,ita, Mimi da kuma Nabila, tunda duk Hassana dince takeyi musu dinki. Ta kware sosai, haka kuwa akayi, suna cikin hira ne, Mimi take basu labarin saurayin da tayi Nawaf

"Nifa bawai baiyi mun bane ba, yanda yake isata da hirar matarshi da yaranshi shine abinda yasa duk ya fice a raina, to tunda yana son matar tashi uwarme ya kawo shi wajena?"

Hassana tayi dariya

"Ke dai Allaah Ya shiryeki, ai wannan alama ce mai kyau, ba wai hirar matar tashi ba da yakeyi miki, yanda yake nuna miki iyalanshi ma da muhimmanci a wajenshi, kema sai kiyi fatan idan abin ya tabbata Allaah Yasa kiyi muhimmancin nan"

Kai Nabila take girgizawa

"Koma menene, karka kawomun maganar matarka, babu ruwana da ita, kazo muyi hira kan abinda ya shafemu, nifa shisa sam bana son ma in kwasowa kaina mijin wata, duk yanda zakiyi dashi sai an samu damuwa, wannan makirar matar tashi saita kawowa soyayyar taku wani cikas din"

Aziza da take jinsu ce tace

"Bafa kowacce ba, wata ma bata da wannan muhimmancin a wajenshi, kinga kaman Habibi na, wallahi har tausayi yake bani, saboda dama can shi ba auren soyayya sukayi ba, wata dusa ce aka hadashi da ita, hakuri kawai yakeyi, shisa nake ta shiri, dan na tabbata kwace shi a hannunta ba wahala zaiyi mun ba"

Wannan karin Nabila ce tayi dariyar harda kyakyatawa

"Wallahi karya yakeyi miki..."

Take fadi har lokacin tana dariya

"Wato zama yayi yana shirya miki drama ke kuma kika hau? Auren hadin shekara mai zuwa ma kina iya ganinta da lodin shagamu, in babu kenan, ya mika mata ta karbe da hannu biyu, yazo yana shirgaki"

Wannan karin su duka sukayi dariya banda Aziza da maganar ta bata mata rai sosai

"Meye kuma shagamu? Kefa Nabila kina da matsala"

Mimi tace

"Ciki mana, ba haka suke zuwa suna samun su Aziza suna shirga musu karya ba, yanzun daya shiga gida zakiga ba zai sake waya dake ba sai gobe idan ya fito, makirin"

Fuska sosai Aziza ta sake daurewa

"To ni ba waya ba, wallahi har video call munyi dashi jiya da daddare, yana gidan nashi kuma balle wata waya"

Hassana tayi mata wani kallo

"Video call da daddare? Ita matar tashi tana ina?"

Dan murmushi tayi

"Nace miki fa wata dusa ce yake aure, tana can tana baccin asara mana"

Aziza ta bata amsa sunayin dariya tare da Nabila, amman banda Hassana da fuskarta ke kara hadewa waje daya

"Amman kinsan daga ke harshi baku kyauta mata ba, saboda abune da idan akayi miki shi ke ba zakiji dadi ba"

Mima ce ta karbe zancen

"Babu wani rashin jin dadi, aina dauka shirga mun kawa yakeyi, in har yana video call da ita a gida to da gaske waccen batama san ciwon kanta ba balle har tayi muhimmancin a wajen miji, idan irin wannan wawayen matan ne to fa kwace miji a hannunsu ba zaiyi wuya ba, ke dai kawai ki shiga da shirinki"

Ganin kome zata fada ba zasu taba fahimtarta ba,sai tayi shiru, amman ita tayi samari masu mata, bama guda daya ba. Ita asalima bataso ka kwaso mata maganar matarka, sannan in dai ka shiga gida, tasan lokacin komawarka gida yayi, koya zaka kirata ba zata amsa maka ba, da yake da anyi isha'i in ba wani abu zatayi ba, kwanciya takeyi tai bacci, ba'a wannan chatting din daren da ita sam. Tana kokarin kiyaye kin yin duk wani abu da ba zataso ayi mata ba a matsayinta na mace to kar tayiwa wata macen.

Sai ta cigaba da fere doyar da takeyi tunda daman suna tsakar gidane

"Duk dani dai in ba kaddara ba auren mijin watan nan bai kwanta mun ba"

Aziza ta kalli Mimi

"Nifa na kasa gane wannan maganar ta mijin wata, waishi namijin inace don mace hudu aka halicce shi? Sai wata ta kwakume tace ita kadai zata rayu dashi, ni wallahi babu wani mijin wata, mijinmu dai"

Nan fa musu ya kaure tsakanin Mima da Aziza da kowa yaki fahimtar dan uwanshi, ganin abin na neman zama rigima Nabila ta katse su da fadin

"Kuna da fadin, yanzun fa akayi azahar, kuna nema ku karar da dan energy din naku akan gardamar da banga amfaninta ba, kowa ba sai ya auri wanda yayi masa ba"

Kafin su amsa Hassana tace

"Ni iskancin kawo mun dinki a kurarren lokaci ma nake so ku duka ku bari, nayi muku magana kunqi jiko, to zaku sha mamaki wannan karin"

Su duka sai suka koma lallashinta, dan sun san Hassana, tsaf zata iya kin dinkawa ko da kuwa tana da lokaci, gashi sun kasa sake wani wajen dinkin, bayan kwarewar da tayi, suna samun rangwame saboda kawancen da yake tsakaninsu. Duk da haka Aziza da Nabila saida suka sake zantawa akan Baffa da suka tashi tafiya tunda hanyar su daya ce, acan ma suka bar Mima da yake ita bata da nisa da gidan Hassana din, unguwa dayace, layi biyu ne ya rabasu

A lokacin da Nabila take karawa Aziza kwarin gwiwar shiga gidan Baffa, da kuma karin dabarun da zatayi amfani dasu ta kamashi a hannu, wasu dabaru da take hadawa da fatan bawai ta kama Baffa kawai ba, a'a ta jijjige Jamila daga gidan gabaki daya ta rayu ita dashi su kadai. Shikuma yana can shago ulcer din da bashi da ita na neman duk wata hanya da zasu kulla zumunta...

********************** **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
************************* **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels

WhatsApp Number: 08138873799


Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** **************************


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels
End Ads