x

Login

Remember me
Forget password ?
x

sign up

Chapter 15 - KANA NAKA Book 1

  • 42001 words
  • 45000 words
  • Out of 97387 words

Category: Love Stories

Views 3094

01 Aug 2025
Start ads
After Image Ads
shigo suna ganinsu suka tashi suka nufesu gabadayan su suna musu oyoyo ita ta Daga Musty shi kuma ya Daga Anum sai ya Rungume Amir..
Daga inda nake ban tashi ba nayi musu barka da dawowa shi ya amsa ita kuma Hannu ta Dagamin saboda bazata iya Daga murya ba ammh Tana da Fara"a sosai nima sai na Daga mata Hannu.
Su da yaran shashen shi suka shiga sai na mike na Shiga kitchen na kwaso musu abincin su na bisu da shi sun baje afalo yaran suna ta wadaka da Ice_cream da su Sweet har da gashishiyar kaza,Zeey din tana zaune gefen Ya Ishaq har kafadunsu na dukan juna tana mgana a waya sai dai ba Hausa take yi ba,sannan ba Turanci ba kamar dai Fullanci.
Na sauke farantin Hannuna na mike kenan ya kirani na Dawo na durkusa a gabansu ya tambayeni abunda na Dafa na gayamai ya juya yana kallonta da ido suka ma juna mgana naga ta tashi tana wani Rangaji Har Lokacin tana mgana cikin Shagwaba ta shige ciki shi kuma kamar wani Sauna ya Bita da kallo ni kaina na kalleta ballatana shi.
Ahmad ya tambaya nace yana barci Sai cewa yayi"Meke damun yaron nan ne..?barcin sa ya fara yawa fa!
Ni dai ban ce komai ba na tashi na fice bayan nace ma Amir suzo su kwanta da Wuri Saboda makaranta gobe.
Falo na koma na Tattara musu littafan da jakunkunan su na kai musu Dakin su na gyara musu in da kowanne zai kwanta na fito musu da kayan barcin su,nayi ta jiran su har goma ta wuce suna tare da su sai kawai na wuce Dakina naje na Duba Ahmad sai sharan barcinsa yake haka kawai na kasa barci batare da ya'yana sun kwanta ba,Ban samu natsuwa ba sai da naji Hayaniyar su afalo na fito falon Amir nayi ma fad'an meyasa basu zo sun kwanta da Wuri ba su san gobe suna da makaranta"?
Anum ya kallah yana fadin"Umma Anum ce taki tasowa."
ina kai kallona wajenta ta wani kwabe Fuska tana Fadin"Umma ni wajen Anty da Daada zan kwana"
Sai yarinyar ta bani Dariya in ban yi wasa ba Anum ta Dauko iyayi wajen Ubanta to in ba Salo ba da shi ta Saba kwana ko yaushe ta san Anty ma..?
Dariya nayi, da yasa yaran suka Tsaya suna kallona hannunta na kama da na Musty Amir na bayan mu zuwa Dakinsu Lokaci daya ina Fadin"Baki san ba kyau yaro ya kwana inda Babba yake kwana ba. ?
Na fada ina zama gefen karamin gadon Anum cikin kallona tace"Umma to ba Ahmad na kwana a wajen ki ba..?
Kai na girgiza ina Dariya Anum akwai kalkalin baki cikin Mgana ta nace"Shi bai girma ba ai bai kai ku girma ba..Da shima ya kai kamar Mutsy ko Anum dina zan daina kwana da shi zai Dawo Cikin yan'uwansa"
Zata kara mgana na Dakatar da ita da Fadin"Shii..Sai gobe sai mu karisa Anum yanzu Dare yayi gobe akwai makaranta ku sauya kaya Mai jin Fitsari ya shiga yayi kafin ku kwanta"
Suka amsa min da Toh ni na saka ma Anum da Musty kayan barcin su araina ina Tunanin in na yaye Ahmad ya kara girma zai dawo kwana wajen su Amir ita kuma Anum Lokacin ta kara girma ita macece sai na cireta cikin yan Maza na koma muna kwana tare.
Sai da na tabbatar da sun kwanta Mun yi addu'an barci na taya muka Shafa jikinsu sannan na baro Dakin na koma nawa nima nayi shirin kwanciya yau da wuri barci ya kwasheni,Kila Saboda na gaji ne sosai sannan abun mamaki har barcin rana nayi ammh kuma na samu ishashen barci da Daddare.
Da Safe ma kamar jiya ne har su Amir suka tafi makaranta basu fito ba Haruna mai adaidaita sai da yayi min mganar kudinsa yace ayi ma megidan Tuni Tunda yaga yana gari nace zan gayamai in sha Allahu yayi hakuri.
Kamar jiya yau ma har kuryar Daki na kai musu abun karyawan su ita Zainab din tana Tiolet kamar yadda yace ban jira ta ba nayi fitowa ina gasgata mganarsa da yace bata aikin komai bata ma iya ba ganin yadda komai kuma ta kara Birkitasa kamar jiya ban gyara ba yau din basu fita da wuri ba sai yammah,Suna cikin Shashen sa sun kule,Ga shi nayi ta Dakon sa nayi masa mganar Haruna basu fito ba sanda kuma suka fito suna tare da ita Hannunuwan su sarke da juna shiyasa ban yi mai mganar ba yace min gobe zasu koma Saboda aikin su zai kaita gidan Anty Binta da gidan Anty Mahma sai kuma su zaga gari nayi musu adawo lafiya.
Yace kada nayi abinci da su zasu ci a waje na amsa mai da toh sannan ya kara Umartana da in shiga bangaransa na gyara musu kamar jiya nan ma na amsa mai da toh.
aiko basu dawo ba sai goma da Rabi na Dare ina Falo ina fama da guga Anum da Musty sun gaji da jiran Dada da Anty  sun yi barci Amir ne ke taimakamin in na goge daman kayan su ne, sai ya rika Dauka D'aya bayan d'aya yana kaima kowa cikin Dirowan kayansa.
Albarkacin Zainab har aka kawo ma su Amir Chips da su pizza,Sai kuma suka Tarar da su Anum din sun yi barci Ya Ishaq shi kadai ya shiga bangaransa ita ta tsaya tana waya naji dai Tana ta ambaton wani suna Daddy tana mgana cikin shagwaba irin na ya'yan gata..sai da ta gama sannan ta Dagamin Hannu sai nima na Daga mata Amir ta yafito da hannu yazo wajenta tana mai mgana ni ban ji me take fadamai ba.
Ta mike tana kallo na inaga abun gugan da taga ina yi ya bata mamaki kusa dani ta kariso da takalminta mai Tsini ta Duka a gabana tana fadin"Sannu fa"
Na amsa mata da mirmishi kallona tayi kafin tace"Hannun ki da bayan ki basa ciwo ne..?ba mai wanki da guga ne..?
Sai ta karkato kanta tana Fadin"Kina jina..?.
Sai ta ma bani Dariya cikin yanayina nace"Ina jin ki mana..ai ina jin mgana in kika yi a kusa dani"
Kai ta jinjina kafin ta kara kallona ta ce"Sannu fa"
Na kara amsa mata sai tace"kina kokari fa..na ji dadin girkin ki..In da a Abuja kike da kin samu kudi..Gidajen mu duk kukus suke d'auka sannan irin ku kuna samun aiki a manyan Restaurant wajen saida abinci kin gane..?
Tafad'a tana kallona Saboda Hausan nata sai a hankali bai zauna ba sai na daga mata kai alamun ina jinta sai kawai taci gaba da fadin"Meyasa baki yi karatu ba Fa'iza..?na tambayi Honey yace kece baki so why.?
Sai kawai na kalleta abunda na Lura da Zeey din macece faram faram bata da girman kai ko D'agawa sannan ita Kai Tsaye ce duk abunda ya shige mata Duhu sai ta yi mganarsa shiyasa ban damu da mganarta ba sai na yi mirmishi kafin nace mata"Ba ni ba ce ba na so..Karatun ne bai dace da Kaskantattun mata irina ba..Wad'anda basu da gata sannan masu nakasun ji irin ta Lalurata.."
Kallona ta tsaya tanayi ina ganin bakinta na motsi ta kasa mgana ita kuma tana so tayi mgana ammh hausan bata san yadda zata min na gane ba,Muna cikin hakane sai ga Ya Ishaq ya leko ya kirata sai ta tashi ta tafi ammh sai da ta waigo ta kalleni nima na kalleta ina tunanin mamakin mganata take yo menene ban sanin mata ba.
Daganan bamu kara haduwa ba sai da Safe da zasu tafi,misalin karfe goma na Safe yara tuni sun tsufa a makaranta,ganin har suna shirin tafiya yasa na yi mai mganar Haruna ina ga saboda a gabanta ne yasa bai yi Fada ba,ya cire dubu goma sha Hudun sa ya bani Saboda duk wata Dubu takwas ne,Sannan ni kuma ya bani Dubu uku na rike a hannuna wai bashi da kudi nidai na amsa ina godiya,Zainab ta bani Hannu mun yi musahaba tana ce min"Sai na ganki kun zo min hutu Abuja ke da yarana"
Mirmishi kawai nayi mata ta Dauki Ahmad har Haraban gidan na Rakasu ko Saboda ganinta ne yasa ya bude get din da kansa Dubu biyar ta bama Ahmad sabbi tace ya raba shi da su Anum,Har motar su ta bar Haraban gidan tana Dagamin hannu nima ina Daga mata bayan sun fice sai na maida get din na kulle na koma cikin Gida ina Sauke Numfashi.
Ban zata haka amaryan tasa zata karbeni ba sai ga shi na sameta a yanayin da ban zata ba.
Da yammah da Haruna ya Dauko su Amir daga makaranta na basa kudinsa yana ta godiya Anum har zata min kukan banza don nace Daada da Anty sun koma Abuja sai da nayi mata jan ido sannan ta shiga Taitayinta.
Tunda suka tafi bai kirani ba,nima ban kira ba nadai san shuru lafiya ne in da ba Lafiya da naji Labari sai nima na kama kaina na cigaba da kula da kaina da ya'yana tafiyar su da Sati Daya Sai ga Goggon karofi tazo min kamar Daga sama nayi murnan ganinta har bansan yadda zan kwatanta ba.
Tazo min da su kuka,Kubewa garin kunu garin Danwake,kayan miya da kuli kuli,Sai ta zo ma da su Amir gyada da mai gishiri da mai bawo,Sai alewan yara,Suna makaranta ko da ta iso da rana ne Lokacin nama zata ko Daga gidan Mama take sai tace min Daga Dutsemah take ta biya ta gaida ta Madina ta dade bataje ba naji Dadin jin Tamadina tana lafiya.
Bakina yaki Rufuwa da Goggo tace min kwana zatayi sai gobe zata koma ni kawai tazo dubawa.
Su Amir nata tsalle da suka Dawo suka ganta,suna son zuwa karofi ammh Ya Ishaq baya bari daga makaranta sai gida sai ko gidan Mama in ma sun je to yini ba kwana ba.
Bamu samu kebewa ba sai Dare bayan yaran sun kwanta Goggo ta na gayamin taji duk abubuwan da suka faru basu yi mata Dadi ba Sai dai tayi ma Yaya mariya fada meyasa ta biye ma Binta ai ko banza ni yar'uwanta ce bai kamata ta taho ta kyaleni ba,Goggo tace kinsan mariya da bakar Zuciya,Sannan ta riga ta rantse ne yasa bata ce ta Dawo ba,ni nake fadama Goggo zuwan ya Ishaq da amaryansa na gayamata mun zauna Lafiya da ita har suka koma Goggo ta cigaba da min nasiha duk akan nayi hakuri ne watarana sai Labari.
Sai Wajen d'aya saura na Dare muka kwanta da Safe kuma da Goggo Tayi shirin tafiya nace ta leka gidan Mama su gaisa tace min bazataje ba Dakyar na Lallasheta tace zata biya tayi mata Murna dagachan zata wuce a bakinta nake jin Hajiyar Dala ta kirata a waya tana mata fadan bata kyauta ba da bata zo ba Goggo tace nayi mata Tas daga Lokacin bata kara kiranta ba.
Sha d'aya na Safe na raka Goggo Har bakin Hanya mun rabu tana ta kara jadaddamin nayi hakuri da rayuwa watarana komai zai wuce sannan na Dage da gayama Allah shine Sarkin Duka Duniya gabadaya.
Mun rabu kamar na bita haka nakeji ammh ba Dama,har da kwallata sai da nayi,Bansan ya Goggo suka kare da Mama ba sai da washegari Badariya tazo take bani Labari Mama har da kuka ta kira Anty Binta da Ya Ishaq akan Goggo Tazo tayi mata cin mutumci Saboda ni..
Gabana ya fadi na zare ido ina kallon Badariya kafin nace"Sabo da ni kuma..?
Badariya tace"Tabbas..Kinsan Halin Mama har Hajiyar Dala sai da ta kira ta fada mata..Ni dai nasan kila Goggo Fada tayi mata shikenan sai cibi ya zama kari Anty Binta nata fada haka ma shi kan shi Ya Ishaq din a waya sai Fada yake barin ma jin Mama nata kuka"
Sai jikina ya fara rawa nasan komai kaina zai dawo aiko hakan ce ta faru Badariya ta tafi ba Dadewa daman Daga makaranta ta biyo sai ga Anty Binta da Mama har cikin gida wanda bazan iya tuna zuwan mama gidan nan na karshe ba.
Zagi da gori da cin mutumci ba wanda basu yin ba ina da goyon Ahmad a baya na Mama ta saka Hannu ta tsinkeni da mari,na Dafe kuncina Hawaye suka Gocemin,Ahmad na barci ne ammh sai da ya tashi Hayaniyar Mama yasa ya tsorata ya fashe da kuka shi yana na Sarari ni ina na zucci.
Mama ta kama kunnuwana ta murde tana fadin"Ni zaki hada ma gulma da munafunci har Goggon karofi ta taka har gidana taci min mutumci don Ubanki..?ai nayi miki komai Tunda na rike ki kuma sannan daga karshe Mijina ya aura miki D'ana kika shiga Cikin zuru'ata duk da bana so..Shegiya mai bakar aniya,Wlh fa'iza na tsaneki na tsani na bude ido na ganki a matsayin surukata"
Anty Binta ta karbe da Fadin"kuma ban da Ishaq din uban waye zai aureta ya zauna da ita ahaka..?
Mama tace'Ki barta zan yi mganinta Tunda bata san mutumci ba"
Haka suka gama zage zagen su,suna yi suna Dungurina suna murdemun kunni sannan suka saka kafa sukayi tafiyar su haka na zauna na Rumgume D'ana ina kuka shima yana kuka har sai yaushe ne zan daina Fuskartar wannan Tozarcin..?
Ba mai Lallashina na gama kukana na Share hawayena,Ashe ban tsira ba Sati biyu da Tafiyar su Ishaq,sai gashi ya Diro ranar asabar da yammah,Abunda yayi min yasa na Fahimci daman saboda yaci min Mutumci ya Dawo.
Har Bangaransa ya kirani na Duka gabansa shima ya ci min mutumci,har yana fadin ba Domin mugun kalaman bakin Baba akansa ba wlh da sai ya Sakeni sai naje Goggon ta auramin Isa ko Yusuf cikin manyan ya"yanta sannan ya kara jamin kunne akan yaya mariya da gaske yake yi kada ta kara zuwarmai gida in kuma wlh tallahi ya kara ganinta sai ya wulakantata.
Na Dago kaina cikin Hawaye muryata ta shake cikin wani yanayi nace"Kayi hakuri..Ba..zan iya fada mata ta daina zuwa ba ne"
Sai kawai na Fashe da kuka Tsawa ya Dakamin yana fadin"To ni zan gayamata in muka hadu Tunda gidan nan nawa ne ina da iko da shi kada na kara ganinta acikin su..In kina Tunanin yar'uwan ki ce in kun had'u wani waje sai ku gaisa ammh ba"a gidana ba kin ji maa na gayamiki"
Sai na kasa mgana kaina na kasa na Share majina kafin nace"Kayi hakuri don Allah.."
Mikewa yayi a fusace yana fadin"Ke dai kika sani kin dai ji abunda na gaya miki..daman abunda ya kawoni kenan Har ga Allah bana son zama agidan nan chan yafiye min kwanciyar Hankali ki kula Fa'iza kada a kara kirana afadamin an hada baki dake an tozarta uwata in hakan ta kara Faruwa zan manta kalaman Baba da komai kema na wulakanta Rayuwarki wlh"
Daman Tozarta ne yazo yi kuma yayi washegari tun Safe ya Dauki hanya,ko sallama bai min ba sai zuciyata ta kara Kek'ashewa na kara Fahimtar cewa ni din ba kowa bace a zuciya Ishaq da duka ahalinsa akwai yuyuwar na nemi abunda zan tsaya da kakafuna ko Saboda gaba da kuma ya'yana domin na Lura hankalinsa yayi gaba daidai da su Yaran ya daina Damuwa da su Sosai.
Tun tafiyar nan da yayi sai da yafi wata bai zo ya ganmu ba,Kudin Hannuna duka ya kare bamai lekomu dagamu sai Allah,kayan abincin mu sai ya kare mun fara shiga yanayi sannan ake aiko mana da Cefane wani Lokacin Direban gidan Anty Binta ko Badariya,a wannan gabar sai da yayi wata biyu da kwanaki sannan yazo ya ganmu shima din sallama suka zo yi Zasu tafi Umra shi da Zeey da iyayanta gabadaya har da ita Zeey din suka zo sallama kwana D'aya suka yi suka koma gidan Mama kuma suka Sauka sai da Safe suka zo min sallama,nayi masa korafin Haruna ya fara mganar rashin biyansa akan Lokaci sai ya fara masifan bazai iya ba gaskiya shi bashi da kudi kuma haka ya tafi bai bani ko sisi ba,Daganan na kuduri niyar bazan kara mai mganar ba Zan neman ma kaina mafita,Bani da wata mafita alokacin sai na maida lamurana wajen Ubangiji na rokensa yaga Halin da nike ciki da ni da ya'yana ya Gaggauta sama min mafitan da zan kula da kaina da ya'yana.



*Janafty*
*KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866

INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE

INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫

INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE

INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS

KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL

MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K

MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K

MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K

MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K

MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K

GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU

MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI

MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866

     *🅿️10*

*Wacece ZAINAB...?*

Cikakken sunanta shine Zainab Lawal bako asalin duka iyayanta uwa da uba Fulani ne gaba da baya,Mahaifiyarta Hajiya Halima bata yi karatun boko ba Saboda yar asalin rugar  Njob'oli ne fulani Jahar yola,Shi ma Dr.Lawal din, Mahaifinsa ya'yan maza suke da Mahaifiyar Hajiya Halima auran zumunci ne iyayansu suka kulla a tsskanin ya'yan nasu.
Shi Dr.Lawal a cikin garin Yola ya girma kuma nan aka haifesa saboda Mahaifinsa ya baro cikin Ruga saboda neman ilimi kuma ya samu Dalilin da yasa bai koma cikin ruga ba kenan sai dai Lokaci bayan Lokaci yana zuwa Dubasu,Sannan shima matarsa Daga Rugar aka aura masa shiyasa shima Alhaji Lawal aka ki bari ya bar gida.
Alhaji Lawal bako yayi karatun Boko
End Ads