zamanta Maman isuhu suke kiranta tayi danwake ta kawomin naci abuna muna ta Hira Da Tamadina duk da mganar nata sai a hankali ammh mu ya'yanta da ta zame mana Dole muna ganewa ni dai ban gayamata wani abu da zai tada mata Hankali ba ko mganar auran Ya ishaq ban mata karfe biyu nayi na tashi na fara shirin tafiya bayan nayi sallah na bata abunda nazo da shi ta Dafa kaina tana ta sakamin albarka.
Ta bani Ahmad na goya a baya na,na saka Hijabina nayi ma mutan gidan Sallama ta rakani har zaure tana D'ingisawa ina ta koma sai tace sai ta Rakani mun yi sallama kamar kar mu rabu har zan tafi ta riko Hannuna na Juyo ina kallonta ta kuramin ido sai naji jikina yayi sanyi cikin mamaki nace"Manene ke faruwa Tamadina..?
Kawai sai ta Dafa kaina ta jijjiga nata kafin tace"Kiii....yi....hakuri..Fa'iza..!
Sai naji raunina ya bayyana da Sauri na kauda kaina ina Boye hawaye na kafin na gyada kai ina fadin"In sha Allahu..Allah ya baki lafiya"
Daga haka muka yi sallama har na kule tana Dagamin Hannu.
Tunda bai amince na biya karofi ba Daganan ma hau motar katsina,na koma gida hud'u saura sallah kawai nayi na fara kokarin dora girki Saboda yan makaranta ammh gabadaya sai ina jin jikina duk yayi wani irin sanyi komai nawa yayi sanyi kamar an zare ma jikina lakka.
Ko su Amir da suka Dawo makaranta sai da suka ga yanayi na Amir mai wayon ciki ne ya dinga ce min"Baki da lafiya ne Umma..?
Sai nace mai a'a saboda kada na tayar musu da hankali sai na warware na shiga cikin su mukaci abinci bayan sun gama mukayi sallar isha'i tare bayan mun idar nayi musu karatun Qur'ani na kara ma kowannen su inda ya ke sannan nace su yi na makarantan bokon su da aka basu amatsayin aikin gida.
****
Tunda Ya ishaq ya tafi bai Dawo ba sai ana Saura kwana uku D'aurin auran sa,sannan ya Dawo shima din gidan Mama ya sauka sai Dare na gansa,gari kuma na wayewa ya kara fita Jamal ya Dawo tare naga suna ta zirga zirgan karbo dinkuna Gidan Mama kuma ya fara cika da baki Badariya ta fadamin Hajiyar Dala ta iso tun jiya sannan da yan'uwan Mama na yamai ni dai ta barayina bana wani shiri Saboda ban ga abunda zan shiryamawa ba.
Ana jibi Daurin aure da yammah sai ga Anty Mamah da Halisa sun zo gida na karb'e su hannun Biyu Saboda suna da kirki Har Halisa ba ta Dauko Halin Anty Binta ba.
Na kawo musu ruwa kenan na zauna muna gaisawa,ba islamiya Saboda alhamis ne Su Amir suna gidan Mama dazu da Jamal ya kawo wasu kayan Shahen Ya Ishaq ya tafi da su Ahmad ne kad'ai tare dani.
Bayan mun gaisa Anty Mamah ta kalleni sama da kasa har sai na Tsargu ina sanye da Riga da zani na atamfa da dankwali kaina na maida kasa ga Ahmad bayana na goya shi.
Anty mahma ta bude murya tana Fadin''Fa'iza ina kunshi ina gyaran kai..? Haka za'a dauko miki amaryan a ganki yarkace yarkace.?
Ban ce komai ba saboda basan me zan ce musu ba halisa tace"Ko Saboda ba anan Amaryan zata zauna ba ne shiyasa kika zauna ba wani gyara..?
Anty Mamah tace"Wannan ba Hujja ba ne..ya kamata ko kunshi tayi saboda gyaran kanta da kanta Halisa"
Ni dai kaina na kasa ban ce komai ba kamar daga sama sai da ya Ishaq ya shigo Gidan yana waya kamar Sauri ma yake yi Anty Mahma ta tsaida shi ya katse wayar yana Fadin"Mahma jira na fa ake yi a waje"
Da Sauri ta mike tana fadin"Ya ishaq me zan gani haka Uwargida ba kun shi ba gyaran kai anya zakayi adalci kuwa..?
Kallona yayi sama da kasa ina ganinsa ta kasan idona sannan ya kwashe da Dariya kafin yace"Tab a bakin Fatar Fa'iza daman in akayi mata kunshi zai fito?
Ba ni kad'ai ba hatta su sai da mganar ta musu wani yam!
Ina gani suna kallon juna ita da Halisa suka kuma kalleni sai na nuna kamar ban ji me yace ba,menene sabo acikin mganarsa a wajena a wajen su ne sabo.
Anty Halisa ne tace"Kai Uncle akwai ma wadanda suka fi Fa'iza bakin fata kuma suna kunshi ko ita da kake ganin bakinta ka saki kudi a sama mata mayuka masu kyau da Tsada kaga yadda Fatarta zata goge tayi Fresh kamar ba ita ba,ko Anty Mahma"?
Kai ta gyad'a kafin tace"Sosai ma yadda mayukan gyaran jiki da na fita suka cika Duniya ai da yawan mata ma ba Farin fatar su bane karawa suke da kwaskwarima"
Baki ya tabe kafin yace"Haka kurum na ba'ta kudina kan wannan abar."
Ya fada ya nuna ni da baki kafin yace"ko an yi mata ba kyau zai yi ba asaran kudi na kawai zan yi sannan ku daina cewa wai farin wasu har da kwaskwarima na Zeey din'a Inganttace ne babu algus,daga mahaifiyarta har mahaifinta Haifaffun Fulanin Adamawa ne"
Halisa tace"Uncle baka taba nuna mana Hoton ta ba"
Ina kallom su ya duba a waya ya nuna mata ta kallah ta kara kalla kafin tace"She is so Beautifull"
Baki ya washe yana jin Dadi Anty Mahma ya mikamawa ta karb'a tana Fadin"Hoto ba zahiri ba ne sai mun ganta ido da ido.."
Dariyan jin Dadi yayi kafin yace"Zaku ganta sati uku zamu yi zamu zo gaisheku in sha Allahu"
Sukace Allah yasa Daganan ya shiga Shashensa ya Dauko abu a leda ya Sake fita suma basu Dade ba sukamin Sallama suka tafi Anty mahma dai kallona kawai tayi tace min kiyi hakuri Fa'iza nayi mata mirmishi kawai ban ce komai ba.
Washegari sai ga Yaya Asiya ta Diro ita da Hafsah da Anty Nasara Goggo karofi ta rantse tace bazata zo ba Tunda dai Mama bata gayamata ba ayi sha'ani Lafiya.
Goggon karofi ta basu kayan miya da yawa sun zo min da shi,Sannan Yaya Asiya ta zo min da kayan kamshin girki da su kori saboda sana'ar da take yi a chan kano kenan Anty Nasara tazo min da less sabo dinkin Buba mai Tsada ta dinkamin kamar in yi kuka Allah Sarki dan'uwa mai rana.
Hafsah kuma ta tsifemin kai ina ta cewa bazan yi ba Anty Nasara tace"Zauna fa'iza ta tsefe miki ki wanke sai ayi miki kitso ki gyara jikin ki ba domin auran da mijinki zai yi ba Sai Domin kema kiji Dadin jikin ki"
Mganar ta yasa na zauna ta tsefemin kai Ahmad na Hannun Yaya Asiya su Amira kuma Daga makaranta basu Dawo gida ba da Jamal ya Dauko su da Motar Babansu gidan Mama ya sauke su tunda naji su shuru.
Ina ta tambayan su Ya mariya sukace zata taho dinki ne ba'a karisa ba ta tsaya karbowa
Da daddare kuma sai gata lokacin har Hafsah tamin kitso tana min yanka Salatif din da zata zana min dayake tana koya,Ko da Yaya mariya ta iso sun wanke kayan miya har sun bada nika sun tafasa sun tambayeni Cafanen girki nace bai bani komai ba kuma bai ce komai ba.
Yaya Asiya tace"Fa'iza kuma baki mai mgana ba..?
Anty Nasara tace"Ban da abun ki Asiya sai tayi mai mgana ai yasan ya kamata..?
Yaya mariya na gefe ta tabe baki bata dai yi mgana ba hira suka cigaba da yi bayan sun bar mganar acikin Hiran ne Yaya mariya tace ita ta fadama Tamadina Ya ishaq zai kara aure tace mata naje ammh ban fada mata ba Cikin Sanyina nace"Kawai sai na fada mata mijina zai kara aure..?
Duka sai suka kalleni Cikin Tausayawa ammh basu ce komai ba
Sai Dare Ya ishaq ya shigo gida Daman ina ta fargaba,ban san wani Rashin mutumci zai yi ba in yaga Yaya mariya agidan ba,Aiko da ita ya fara cin karo ta fito daga dakina,kallon kallon suka yi ma juna ni kuma ina falo zaune kafafuwana cikin leda Tunda an saka Lalllin,Hafsah ke gefena ta na sakamin na Hannu,jikina ya fara rawa bana so ya wulantamin yar'uwa,Hafsah ce ta gaishe shi ya amsa kamar bai santa ba Yaya mariya kuwa kamar bata gan shi ba haka tazo ta wucesa Ina ganinsa ya Dago yamin wani kallo ni kuma sai na sadda kaina kasa jikina na rawa fitowar su Yaya Asiya yasa bai yi mgana ba suka gaisa har zai shige shashen shi Anty Nasara tace"Ishaq wai me zamu dafa ne na taron Fa'iza gobe..??mun zo mun ga ba komai na cefane ko a wani waje za'a Dafa abincin namu ci ne kawai..?
Ta karishe fad'a cikin Zolaya kansa yasosa kafin yace"Na sha'afa ne ammh bari zan kira Mama ko Anty Binta"
Daga haka ya shige Ciki ya bar mu nan suka bisa da kallon mamaki,Ni dai gabana sai fad'i yake kada ya yi Tijaransa a gabansu,Kunshin da na saka ya Ceceni Domin sai chan Dare na cire sa kuma ya riga ya kwanta sai ban nemesa ba na yi sallar isha'i nayi shirin kwanciya ni da Yaya Asiya muka kwana Daki d'aya Yaya mariya da Anty Nasara da Hafsatu suka kwana Daki d'aya.
Kwana tayi bani baki da Shawarwari ina jinta kuma ina Dauka kalmar dai guda Dayace nayi hakuri to in ban yi hakuri ba ya zan yi..?
Da Safiyar ranar asabar karfe tara na Safe tawagan ango da waliyansa suka mika ko sallama Ya Ishaq bai min bai,bai kuma barmin komai ba,ina wanka naji su Anty Nasara na mganar sun fita shi da Jamal,a tunanin su zai dawo sai zuwan Badariya ta tabbatar da sun mika Hanya kuma ba dawowa zai yi ba Tunda chan amaryan zata zauna.
Ban yi amfani da kayan da Anty Binta ta bani ba Domin Yaya Asiya ma ta dinkama na atamfa mu hudu har da Hafsah dinkin ne Yaya mariya ta tsaya ta karbo mana.
Ganin har sha Daya tayi kawai sai nace su Dafa sauran shinkafar data ragemana Daman bata wuce tiya hudu ba Tunda Ya ishaq din bai ce komai ba kayan miya kuma sai suyi miya dashi Yaya mariya sai fada take tana fadin"Haba aiko Dai darajan kashin miya ma samu"
To kafin ma a tashi a d'aura sai ga Anty Binta tazo da mganar chan gidan Mama zamu koma ayi bikin gabadaya.
Yaya mariya ta Daka tsalle tace wlh ba wanda ya isa shikenan saboda sun maidani banza a banza taron ma ni da Dangina sai an yi min iko da shi.
Anty binta ko taki tafiya tace kafarta kafarmu ai nan din da gidan Maman duk D'aya ne
Su Yaya Asiya suka shiga tsakaninsu ammh sun fara cacan baki,nayi kuka kukan bakinciki da wannan tozarcin da aka shiryamin Yaya mariya tayi rantsuwan bazata je gidan Mama ba,ko sallama haka ta Dauki kayanta ta wuce karofi ni da Yaya Asiya sai Anty Nasara da Hafsatu dake goye da Ahmad muka tarkata zuwa gidan mama a ka kulle gidan key din ma na Hannun Anty Binta.
Dakin Badariya muka sauka Saboda nan muke da Daraja,kallon mutumci cikin Dangin Mama ko kawayenta ba wanda yayi mana gida cike da mutane sai harkan arziki akeyi su Amir sun shige cikin yara sa'o'in su suna ta wasa Anum ta saka anko Mutsy kuma kayan yan kanti Amir dai ban gansa ba Anum tace dashi Uncle Jamal suka tafi.
Abinci ma sai chan da Rana aka kawo mana shima sai da Anty Mahma ta shigo ne taganmu baki bude tace an kawo mana abinci mukace a'a ita ta fita ta samo mana waina da Jallop din shimkafa sai alala.
Duk yadda naso na Daure ma wannan wulakancin na kasa har ta su Yaya Asiya abun ya tabasu suna tare dani sun kasa fita Hafsatu ce Badariya ta jata.
Kawayen Mama sai dai su lekomu suna Dariya a wulakance,sanda yan Daurin aure suka kira sukace an Daura aure haka Anty Binta ta rika rangad'a gud'a ita da kawayenta itama Mama ance har da rawa sai da ta taka Anty Nasara ta kalleni ina ta sharan kwallah ta dafani kafin tace"Ki yi hakiru Fa'iza ki bar kuka..Watarana sai Labari"
Yaya Asiya abun ya ciwota sai ta kasa ma mgana har da kidan kwarya sai da yan yamai sukayi sannan da Daddare suka kure kid'a da wakar Bikin Ishaq da zainab suna rawa ni dai ina kan sallaya tun bayan da nayi sallar isha"i ban Daga ba ina kai ma Allah kukana.
Washegari ma Anty Mahma ne ta kawo mana kosai da koko muna gama karyawa su Yaya asiya suka yi Haraman Tafiya na kallesu a marairaice kafin nace"Tafiya kuma zaku yi..?
Yaya asiya tace"Kiyi hakuri Fa'iza ya zama Dole ga Hafsah nan ta zauna sai gobe sai ta dawo mukan yau zamu tafi in sha Allahu"
Ban hanasu ba domin suna da gaskiya gwara kayi nesa da in da ba'asan Darajan ka ba.
Da zasu tafi har Dakin Mama sukaje sukayi mata fatan alheri Hajiyar Dala bata ta nan da ita aka tafi Abuja ita zata tarbi Amarya ance suna hanya yau zasu dawo.
Mama sai mgana take har tana fadin"Nasara goggon taku dai taki zuwa to ku shaida mata an daura auran ba'a fasa ba"
Su dai basu mayar mata da mgana ba suka musu sallama suka kama Hanya ransu ba Dadi.
Naso aranar na koma gida Anty Binta tace ban isa ba,Sai an watse taro Sai Yammah mutanen abuja suka Dawo Hajiyar Dala murya har waje ta na bada Labarin gidan arzikin da Ya Ishaq ya nemi aure tazo da Turamen tamfa na iyaye guda goma da kayan gara mota guda har da shaddodi da kuloli kayan uwar miji da Uban miji Robobi cike da kayan fulawa har da nakiya da alkaki.
Nima Anty Binta ta kawomin alkaki da Cin cin,Sai kula mai biyu guda daya na karb'a na saka albarka a bakin Badariya nake jin har da Turmin Atamfa akace abani Mama ta Dauke tace ba za'a abani ba araina nace ko an bani bazan Daura ba ai ban dace da kayan alfarma irin shi ba da su yafi Dacewa.
Agidan muka kara kwanaa sai Ranar Lahadi da yammah muka koma gida bayan ni da Hafsah mun zage mun gyara gidan Mama tas sannan Anty Binta ta bani key din gidan na Tattara duka ya'yana muka koma gidana Hafsha kuma nace ta bari sai washegari sai ta tafi."
*Littafin KANA NAKA book 2,3 paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*
*Nagode sosai da addu'o'in ku ga kawu Madalla da ku naji dad'i Allah ya amsa, shi kuma kawu Allah ya jaddada rahma a kabarinsa Ameen summa Ameen.*
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866
INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE
INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫
INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE
INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS
KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL
MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K
MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K
MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K
MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K
MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K
GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU
MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI
MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866
*🅿️08*
Da muka koma gida na zame jikina na shige daki nayi kuka na rarrashi kaina daga baya ranar ban yi moruwa ba ina kwance acikin d'aki ina Tunanin makomar rayuwata,Yaran suna tare da Hafsatu har ta ko da Ahmad Amir ne ya dame ta da Ina Umma sai tace na kwanta bana jin dad'i ne tunda taga yanayi na.
Ita ta yi musu girki cikin sauran k'wayanim taliyan da suka rage mana ta dafa sai ta dib'i Tumatir din nan Tafashasshe tayi miya da shi suka ci ta zubomin nace ta dauke sa bazan iya saka wani abu aciki na ba.
Tare da yaran suka yi ta burumtun su afalo ina jin su kafin ta yi musu shirin barci ta rakasu d'aki suka kwanta Ahmad kuma tayi mai wanka sannan ta kawo min shi ya fara rigima na bashi Nono sai yayi barci ni kuma na Rarrafa na tashi na yi alwala nayi Sallar mangariba da isha'in da kasalan Rayuwa ya danne ni na kasa tashi.
Washegari tun safe Hafsah ta shirya bayan su Amir sun tafi makaranta Haruna mai adaidaita na roka ya kaita inda ta hau motar Karofi,ta barni Dagani sai halina acikin gidan da bansan makomata ba.
Tun kuma bayan tafiyarta ban karaji Daga kowa ba hatta Yaya Asiya bata kirani ba Daman goggo nasam tayi Fushi ga abunda kuma daman ya sake Faruwa nasan tun kafin su Anty Nasara su koma Yaya mariya taje mata da Labarin komai.
Harta bangaran su Maman ba wanda ya kara nema na ballatana ace bari a kaga Halin da nake ciki ni da ya'ya to wanda ma Hakkinsa ke kan mu ai bai Damu damu ba ballatana wani ya nuna Damuwarsa a kanmu.
Tunda bayan auran Ya ishaq da Abar kaunarsa ban kara jinsa ba bai kirani ba kuma bai min sakon kudi ba an wayi gari bani da ko sisi a hannuna.
Na shiga damuwa ga shi kayan abinci duk sun kare daga shinkafa sai sauran Taliya ta ragemin Indomie ta kare saboda ina dafa musu sau biyu a sati suna tafiya da shi